Furar Danko Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: FURAR DANKO 1.txt
Chapter 50 of 94
    A motar tuƙinsa yake tayi, yayinda ita da Deen suketa surutunsu da dariya. Dan indai Lulu da Deen ne kam babu mai shiga tsakani. Sai ya ƙulleta da haushi ta mammakesa da kiransa mai shegen surutu kamar akku. Sun tsaya a wani ƙaramin super market Uncle Yousuf ɗin ya fita shi ɗaya. Bai jima ba ya dawo, sai kuma a wajen masu fruits, nan kam da ga motar ma yay bayanin abinda yake so aka kawo masa ya bada kuɗin suka cigaba da tafiya. Lulu dai bata tambayi ina zasuje ba. Hasalima hankalinta gaba ɗaya naga Deen ne. Sai da motar ta tsaya ne sannan hankalinta ya dawo ga inda suken. Kallon anguwar take a ɗan yamutse, duk da ba wani datti bane ko makamancin hakan, hasalima titi ne shimfiɗe da ya miƙe samɓal kasancewar gidan su Smart na a farkon shiga layinne. Sai dai yanayin gine-ginen da kai kawon mutane dana ababen hawa riiiii yasa zaka tabbatar dai irin tamu ce dangin malam Shehu....
    “Papa nan fa?â€Â
  Cewar Lulu a gatsine.
Maimakon bata amsa wayar da yake dannawa ya kai kan kunne. Ta daiji yana amsa gaisuwa, sai dai bata fahimci mi ake cewa da ga can ba. Sai kuma taji Uncle Yousuf É—in na cewa, “Kai dai kaÉ—ai ne a É—akin ko? Okay gani nan shigowaâ€Â. Daga haka ya yanke wayar tare da buÉ—e murfin yace, “Oya ku mujeâ€Â.
    “Uncle.....â€Â
  “Shiiiii...†yay saurin katseta tare da mata alamar zip a baki. Dole ta haɗiye abinda take son fadar dan babu alamar wasa akan fuskarsa. Shi da kansa ya kwashi ledojin, ita kuma ta fito riƙe da hannun Deen tana ta faman yamutse fuska. Sauƙin ma babu kowa a ƙofar gidan. Wanda ke iya hango su kuma ba sosai suke iya ganinsu ba duk da harda masu leƙe saboda son gulma irin ta mutane. Soron ta dinga bi da kallo duk da shima dai fes yake gashi kuma lailaye da sumintinsa. Hakama koda suka shigo gidan ko'ina fes babu wani datti, ga gidan shiru babu yawan hayaniya sosai dan yaran sun wuce ismaliyya, sai ma matan anguwa da wasu a dangi dake ta faman shigowa yin ALLAH ya sanya alkairi da auren Smart ɗin da ba'a san da shi ba. Sai kuma wanda suka san baida lafiya na ɗorawa da jajanta yaya jiki musamman maƙwafta. Anan dai ta inda suke basu haɗu da kowa ba har suka shige sashen ɗakunan samarin gidan da ke a farkon shiga. Anan sun ɗan haɗu da wasu. Bakowa bane kuma sai Mubarak da kema Smart wankin kayansa na ciki, sai Abdull a gefensa yana kallon film a waya da eirpiese a kunnensa. Mubarak ya shiga musu sannu da zuwa cikin girmamawa dan ya gane Uncle Yousuf, itako Lulu dama kallo guda tai musu ta ɗauke kai gefe a ranta tana ƙunƙunin ina ne nan Uncle You ya kawosu. Duk da dai gidan babu wani makusa tare da shi a ɓangaren tsafta a ginensa dai na masu ƙaramin ƙarfi ne. Ita ba hakanne ya dameta ba, kawai bata cika son zuwa irin wajejen nan bane, shiyyasa ko aikinta ya ratsa da hakan zaka ganta cikin rashin sakewa da son a gaggauta abar wajen. Abdull da Mubarak ya zungura shima ya shiga gaishesun. Duka dai Uncle Yousuf ne ya amsa da tambayarsu ko Aliyu na nan? Duk da yasan yana nan tunda dai yayi waya da shi. Sun amsa masa da girmamawa Abdull ya tashi yay musu iso.
    Tunda Uncle Yousuf ya ambaci Aliyu ta kafesa da idanun son jin Æ™arin bayani, sai dai bai kulata ba yay gaba dole suka bisa a baya. Yana zaune a saman katifarsa da Æ™arin ruwan da doctor ya Æ™ara saka masa babu jimawa saboda rashin Æ™arfin jiki da ya tashi da shi. Wando ne 3 quarter a jikinsa da Æ™aramar t-shirt data kama masa jiki sosai. Ainahinsa na tsayayyen mutum ya fito sosai. Fes É—akin yake ga Æ™amshin turaren wuta mai daÉ—i da Maryam ta saka masa bayan ta share. Gefensa kaÉ—an flaks É—in shayinsa ne da cup da ya sha sai kayan tea a wani basket mai Æ™yau harda bread alamar dai nan É—in ne wajen ajiyarsu. Sai kuloli biyu da jug mai riÆ™e zafi da aka dama masa kunun gyaÉ—a. Sallamar Abdull da ta Uncle Yousuf ta sashi É—ago idanunsa da ke kallon tv ya zubama Æ™ofar tare da amsawa. Abdull ya fara shigowa da faÉ—in, “Yaya Smart baÆ™i neâ€Â. Kalmar baÆ™in ta bashi É—an mamaki, dan shi a tunaninsa Uncle Yousuf É—in ne kaÉ—ai kasancewar su Daddy basu jima da tafiya ba su. Kafin ya kai Æ™arshen tunaninsa Abdull ya gama ajiye ledojin da ya amsa a hannun Uncle Yousuf Deen ya shigo, Uncle Yousuf biye da bayansa Lulu a Æ™arshe. Harga ALLAH sai da gabansa ya faÉ—i, bawai na tsoro ko makamancin hakan ba, shi dai kawai ya samu kansa da jin bugawar Æ™irji. Sai dai kuma abinda bai sani ba bashi kaÉ—ai ba. Ita kanta Lulun sai da nata Æ™irjin ya harba. Hannu ya miÆ™ama Deen yana faÉ—in, “Welcome my little handsomeâ€Â. Cike da farin ciki Deen ya nufesa shima yana murnar ganinsa. Zama Uncle Yousuf yay a sofa É—in É—akin Æ™wara É—aya yana murmushi, yayinda Lulu ta wani cakuÉ—e fuska da yamutse ta duk da taji shock É—in ganin inda Uncle You É—in ya kawo ta ta danne, dan tunda tai masa kallo É—aya a yayin shigowarsu bata sake ba.
     Smart da ke sauraren surutun Deen da ya karaÉ—e É—akin ya dubi Uncle Yousuf cike da girmamawa ya ce, “Uncle Barka da safiyaâ€Â.
   Shima cike da kulawa yake kallonsa da tausayawa. Amsawa yay da “Barka dai Aliyu yaya jikin naka?â€Â.
    “Alhmdullah ai na miÆ™eâ€Â.
  “Kana dai dauriya Aliyu ga shi harda su Æ™arin ruwa. ALLAH ya baka lafiya yasa kaffara neâ€Â.
  “Amin ngdâ€Â.
Ya faÉ—a can Æ™asan maÆ™oshi yana bin Lulu da ta dogare tsaye da kallo Æ™asa-Æ™asa. A take wani abu ya tokare masa maÆ™oshi akan shigar jikinta. Lallai yasan akwai babban yaÆ™i a tsakaninsu. Dan shifa bazai yarda da wannan shigar shegantarkar ba gaskiya. Uncle Yousuf da shima ya juya yana kallon Lulun ya nuna mata gefen katifar yana faÉ—in, “Zauna mana kikai mana tsaye a kai Mawaddat. Ba kuma kiga Aliyu babu lafiya ba?â€Â.
    Kamar zata fasa ihu taji, ta sake yamutse fuska da É—aureta a taÆ™aice ta ce, “Uncle nan ma it's okâ€Â. Sai kuma ta dubi Smart fisha cike da gatsali ta ce, “Sannu faâ€Â.......âœÂï¸Â
*_Kuma sannu fa🙋 dangin Smart 😂🤣🤩. Dangin mu Lulu's team Barka da rana😚😘😉._*
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIPðŸâ€Â¥Ã°Å¸â€™Â¯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶ðŸâ€Â¥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmuðŸ˜ÂðŸ™Â_*
ð“ð²ð©ð¢ð§ð 📲
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.