Furar Danko Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: FURAR DANKO 1.txt
Chapter 86 of 94
____________
.......Dada tayi tunanin Lulu zata sake dawowa gidan, amma bayan duk Æ´an rakkiyar Baba sun dawo sai gashi babu ita, sai ma sanar mata da akai ta wuce gidan ta. Hakan ya sake girgiza Dada ta kuma tabbatar da eh lallai da alamar Æ™amshin gaskiya a zancen mutanen nan asiri yaron nan yay ma jikarta. A take ta dannama Fulera mai Æ™unshi kira, batare dako amsa gaisuwar ta ba tace ta sameta yanzun. Fulera ido a kuÉ—i tuni tai tsalle tayo waje da ga gidan su, dan dama dai zawarci take kusan shekara tara kenan. Cikin Æ™anÆ™anin lokaci sai gata a Garko house. Ta sami Hajiya Dada tare da mai aikinta dake mata irin waÉ—an nan ayyukan na sirri, dan Dada tunda jajayen sawu Æ´an hannun bin malamai ne kam. Cikin gurfana Fulera ta miÆ™a gaisuwa, Dada ta amsa cike da isa. Babu wani jan lokaci ta sanar musu abinda take son a mata. Zasuje wajen mutumin da tace mata a Zuru ita da mai aikinta. Ba haka Fulera taso ba, amma dai babu damar musu dan haka ta amsa da to. Mota Dada ta bada akaisu tare da kuÉ—in amma sai ta damÆ™awa mai aikin nata. Nan ma Fulera taji zafi, ta dai danne, damar fara fita data samu kafin mai aikin Dada ta kimtso ta samu ta dannama Hajiya Naqiba kira ta sanar mata komai. Dariya Hajiya Naqiba tai da faÉ—in, “Kai tsohuwar nan mayyace akwai shegen wayo. Barta ai inta san wata bata san wata ba. Kwantar da hankalinki bari na kirashi kafin ku isa.â€
   Haka kuwa akai hajiya Naqiba tai kiran malam na-zuru, duk yanda suke so haka ta tsara masa, shima da yake shegen kansa ne yace karta damu. Abinka da lafiyayyar mota basu sha wahala ba, dan bayan azhar kaɗan suka isa zuru saboda gudu na masifa da drivern yayi. Malam na-zuru da yake yasan da zuwansu kafin ma su faɗi abinda ya kawosu ya shiga zayyane musu wai ai ya gani ne a cikin aikinsa. Tuni mai aikin Dada ta ruɗe ta danna mata kira, nan ma fa sukai magana da malam Na-zuru ya sake fanfa Dada da kalolin sharri wa Smart dangane da auren Lulu, harda cewa ai asiri Smart ɗin yay musu dan yaga kuɗi. A yanzu haka ma yana Niger yaje anyo masa wani babban ƙulli, zaita kwantar musu da kai ya nuna shi na ALLAH ne sai anan gaba kaɗan zai bayyana halayyarsa da mugun nufinsa. Tsaf Dada tahau ta zauna saboda tayi imani da malaman tsubbu matuƙa gaya. Malam na-zuru ya haɗa musu kayayyaki suka sake ɗakko hanya....
   WASHE GARIN Lahadi Lulu da Æ´an kwananta ta zubasu a mota ta kaisu sabon Saloon da ta fara zuwa yanzu ana mata gyaran jiki. Tsaf aka gyara Æ´ammatan nan suka fito tas da su kamar basu ba. Daga Saloon sun shiga wani joint suka É—an sha ice-cream da abinda baza'a rasa ba. Daga nan suka koma gida. Kasancewar duk sun gaji kuma basa tare da yunwa suka shige É—akin dake matsayin masaukinsu masu kwanciya nayi masu fira nayi. Itama anan falo ta É—an kwanta dan ta haÉ—iyi kayan nata duk da kaÉ—an take sha dan kar yaran su fahimta. Wayarta ce ta shiga ruri, takai hannu ta É—auka tana jan Æ™aramin tsaki. Ganin Dada ya sata waro idanu waje, sai kuma ta É—aga da sauri. Kafin tace komai Dada ta ce, “Ina mai gadin naku anata horn kamar ya mutuâ€. Da mamaki Lulu tace, “Mai gadi kuma Dada? A ina wai?â€.
    “Gidan da aka kawoki mai kama da bukkar fulaniâ€.
  Dariya Lulu tai tana miÆ™ewa. Ta ce, “Uhm Dada baÆ™ya gajiya dama mutane sharri idan baki son su. Wannan gidan ko makaho ya shafa ai yasan badaga nan ba. Ina zuwaâ€. Ta yanke wayar tare da zura slippers ta fita. Da kanta ta buÉ—e musu gate É—in. Dada na hakimce a bayan danÆ™arereiyar motar da sukazo baÆ™a wulik, sai drivern ta. Koda ya samu waje yay parking sai da ya buÉ—e mata ta fito tana wani yamutse fuskartar ta tsufa da bin gidan da kallon banza. Yi Lulu tai kamar bata fahimceta ba ta rungumeta tana murnar ganinta. Dada ta tureta da faÉ—in, “Ni karki kadani fitinanniyaâ€.
   “Ni na isa kadaki Hajiyar Baba Garko. Yanzu yana asibiti yana fama da kansa ke kina nan kina yawoâ€.
   “Oh kijimin yarinya da Æ™ulli, yanzu zuwa na dubakin kuma bammayi miki gwaninta ba kenanâ€.
      “A'a kimun yi haÆ™uri muje cikiâ€.
   A falon ma dai Dada sai yamutse-yamutse take duk da ya mata Æ™yau matuÆ™a. Nan ma Lulu tai kamar bata lura ba taje ta kawo mata ruwa da lemo. Tana zama ta jeho mata tambayar “Ina yaran dana ganki da su É—azun?â€. Cikin rashin damuwa Lulu ta nuna É—akin da su Maryam suke. ÆŠan jimm Dadan tai sai kuma ta miÆ™e, “Kinga muje É—akin ki magana nazo muyiâ€. Babu musu Lulu ta miÆ™e suka nufi bedroom É—inta da Asma'u ta gyara Æ™al sai tashin uban Æ™amshi yake yi. Nan ma dai sai da Dada ta gama Æ™are masa kallo sannan ta ja numfashi. “Kaya har kaya anzo an zubesu a wannan takurarren gidan.†ƙin cewa komai Lulu tayi, dan haka Dadan ta cigaba da faÉ—in, “Game da zuwa duba Alhaji ne. Shin zakije ne?â€. ÆŠan jimm Lulu tayi, sai kuma ta nisa da faÉ—in, “Ina son naje kam Dada, sai dai yanzu Aliyu yayi tafiya maybe ya dawo gobe. Idan ya dawo mukai magana sai kijiâ€. Sosai zantukan lulun ke sukar Dada da sake gaskata fa amma jikarta asiri, yo Mawaddat É—in ta data sani mai zafin nan da Æ™yamar abu ga murÉ—aÉ—É—en hali wai namiji ke juyawa haka. Namijin ma talaka É—an talakawa fitik mai amsa sunan drivern ta. Kai wannan al'amari akwai ayar tambaya. A zahiri kam murmushi tai da cewa, “To ba laifi hakan ma yayi. Af kinga zan manta ga wannan kisha maganin ciwon maran nan ne dake damunki dama nace zan amso miki, inata shiririta sai kwanaki aka amso kinata zuwa gidan kuma ina mantawa. Shiru Lulu tayi tana kallon goran ruwan kamar tace a'a sai kuma dai ta amsa, dan ranta bazai taÉ“a bata Dada acikin jerin wanda zasu iya mata wani abu daban ba, sannan tana saran ganin period É—inta nan da kwana uku, tasan kuma azabar da take sha na ciwon maran. Amsa tai ta ajiye gefe, amma sai Dadan tace tasha mana. Ai ba'a wasa da magani. Badan Lulu taso ba ta buÉ—e tasha kusan rabi ta ajiye. Daga haka suka cigaba da hirarsu da Dada wadda duk bugun cikine akan auren nan da son sanin wanene Smart. Ita dai Lulu tana bata amsar abinda ta sani ne kawai, har cikin ranta kuma bata kawo komai ba. Sai da Dada take cemata tafa kula, karta yarda yaron nan ya mata wayo ya kwanta da ita, dan yanda kwanakin nan suka kusa cika zai iya shirya mata muguntar maza. Lulu tai murmushi da faÉ—in, “Dada kenan nace miki ki kwantar da hankalinki, Shifa Aliyu ba irin waÉ—an nan da kike tunani bane. Na tabbata tunda har ya amince da auren nan na wata É—aya ne kuma zai sake ni bazai taÉ“a saÉ“awa ba zai sake nin, yanzu haka ma jiran dawowarsa nake mu fara maganar dan shiyyasa nace ki dakata da batun tafiyar nan, cases É—in dake gabana zanyi Æ™oÆ™arin kammalasu na É—an É—auki hutu daga duba Grandpa zan É—an huta kafin na dawo Nigeria gaskiyaâ€.
   Sosai Dada taji daÉ—i dan haka ta shiga sanya mata albarka. Daga haka ma sai ta miÆ™e tana faÉ—in, “To bara na wuce tunda na kammala abinda ya kawo ni. Sai na jiki É—inâ€.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.