Best / Popular Hausa Novels

Furar Danko Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: FURAR DANKO 1.txt

Chapter 82 of 94

         

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣9️⃣

.......Alhamdullah yau Lulu zata ce kasancewar abubuwa sun tafi mata yanda take so. Dan duk da zaman shari'ar yau aka fara Alhmdllh tana hango nasara a cikinta. Bayan barin kotu da Hassan yazo ya kaita da kansa office ya sake maidata, ta ɗan taɓa aiki bayan sallar azhar ta fito. Tana jan mota ta fita Security ɗin nan ya dannama Smart waya ya sanar masa. Godiya yay masa sannan shima yay kiran wanda ya saka ya dinga bibiyar masa ita akan yabi bayanta da napep ɗin. Kai tsaye anguwar da mijin Hawwah yake ta nufa, da tambaya ta isa gidansu Sa'id. Mai Napep da ke binta ya kirasa ya sanar masa. Sosai Smart yay mamakin abinda ya kaita, har ya dinga jin son yazo amma dai ya dake da ƙyar dan son ganin iya gudun ruwanta. Sama-sama ta gaishe da maigadin tare da tambayarsa ko hajiyar gidan na nan? Amsa mata yay da eh cikin washe haƙora. Fuska ta yamutse cike da izzarta ta ce, “Sanar mata tana da baƙuwa”. Babu musu ya amsa mata da to yana nufar cikin gidan. Mintinan baifi uku ba sai gashi ya dawo ya ce ance ta shiga.
          Kallon gidan ta dingayi side by side tana taɓe baki, a irin dukiya ta gidansu gidan su Sa'id ɗin ba komai bane ba, sai dai ba laifi suma dai da gani akwai kuɗin sai dai ko kama ƙafarsu basu isa yi ba. Ƙofar da take ƙyautata zaton falon gidan kenan ta nufa, cikin sa'a ma sai ta hango wata yarinya tsaye kamar tana kuka da alama mai aiki ce, isowarta kusa da ita ya sata daina kukan ta risina ta gaisheta. Sau ɗaya ta amsa mata ta ɗauke kanta. Yarinyar ce ta mata iso cikin falon, babbane sosai ya kumaji ɗirka-ɗirkan kujeru kamar bana dattijuwa ba. Kallo ɗaya taima matar dake zaune a falon ta fahimci itace mamar mijin Hawwah ɗin, dan ko'a ido ka kalleta kasan za'a zuba da ita kam. Zama tai kanta tsaye tun kan ma ace ta zauna, maman Sa'id dai kallonta take alamar rashin sani, duk da Lulu ta fahimci hakan sai ta basar, cikin ɗaukar kan nan nata na isa da ƙasaita ta ce, “Hajiya barka da rana. Sunana Barrister Mawaddat Isma'il Jiƙamshi.”
      Sai da zuciyar maman Sa'id ta motsa jin ƴar waye, sannan sunan kansa na Mawaddat ɗin duk mai bibiyar harkokin mata a fanin fyaɗe dole zai santa, ita kanta dama tunanin ina tasan wannan fuskar takeyi. Lulu data lura da hakan ta cigaba da faɗin, “A yanzu haka matar Aliyu M. Idris Mawashi yayan matar ɗanki dan bana tunanin kin halarci bikin sati ɗaya daya shige”.
      Gaba ɗaya Mama duk sai ma taji ta daburce, dan tabbas Sa'id yata roƙarta zuwa bikin amma tace bazataje ba dan ba'a gayyaceta ba, koma an gayyacetan bazataje bikin matsiyata ba dan tasan dai bai wuce tuwo da waina da zoɓo ba. Harga ALLAH bata san ɗiyar wa Aliyun ya aura ba. Da ɗan jimami ta ce, “Da gaske kece matar Aliyun?”.
           Lulu dake mata wani kallo a yamutse ta amsa da, “Oh baki yarda bane? Zaki iya tambayar ɗanki ni yanzu ba wannan ne ya kawoni ba. Nazo nan ne game da case ɗinki da Hawwah, kinyi ƙoƙarin zuba mata mai dake saman wuta da nufin ƙonata, ba kuma wannan ne karo na farko ba da hakan ta faru. Kinci arziƙin ɗanki shiyyasa banzo da police ba a yanzu haka domin kamaki. Amma nazo da kalaman gargaɗi a gareki a karo na farko. Su iyayenta sun barki saboda jin nauyin karamcin ɗanki. To ni kuma a matsayina na mai kare hakkin mata kuma matar Yayanta bazan iya barinki ba. Kin haifi Sa'id ba kin haliccesa bane, yana kuma da damar yin aure tunda bake zaki auresa bane, matsayinki daban matsayin uwa matsayin matarsa daban matsayin mata. Nan gidan aurenki ne, shi kuma nan gidan da aka haifesa ne, kina zaune da mijinki lafiya dan haka itama ki barta ta zauna da nata mijin lafiya. Wannan takardar da kike gani na tattara dukan abubuwan da kikai mata ne, tare da bincike mai yawa akanki a wajen ƴan anguwa da ƴan uwanki dana mijinki, kuma sun bani duk wani information a kanki har ma wanda bakiyi zato ba. Haka ma mijinki nayi waya da shi yanzu haka, dan haka kina da zaɓi biyu zaki saka hannu zan saka hannu Sa'id zai saka hannu hakama Hawwah da sharaɗin zaki fita rayuwar aurensu ki zauna a matsayinki na mahaifiyarsa, zakuma subar wannan gidan su koma nasu, sannan kije da kanki gidansu ki bata haƙuri ki bama iyayenta haƙuri. Zaɓi na biyu ƙin amincewa da shawarar farko na shigar da wannan case ɗin kotu mu zuba shari'a wlhy har sai na kaiki jail dan har video ke gareni na randa kika kusa kasheta a dalilin hankaɗota daga saman upstairs gashi”. Ta ɗaga mata wayar tana mai playing video ɗin, jikin maman Sa'id ya fara rawa, Lulu ta sake shiga wani ta ce, “Ga kuma na randa kika watsa mata ruwan shayi harta ƙone a wuya shima”. Sosai Lulu taga ruɗewa a idanun Mama. Tai murmushi da kaɗa kanta cike da isa. “Ba waɗannan kawai ne ba, akwai wasu tari-tari kuma duk Hawwahn ke ajiyesu, bata nuna bane saboda mutuncin ɗanki. Amma ni yanzu na shirya fiddosu a gaban alƙali. Kin san dai mijinki siyasa yake yi har yana shirin fitowa takara a shekara mai zuwa ko, sannan yayanki a yanzu haka ɗan majalissa ne, to a dalilinki duk zan iya tarwatsa wannan damammakin, dan bayan kasancewa jinin Jiƙamshi jinin Alhaji Sufi Ado Garko nake kuma. Sai ki zaɓa na baki nan da kwanaki uku kacal. Na barki lafiya”. Ta faɗa tana miƙewa murmushi ɗauke da fuskarta ta ɗaga mata yatsu biyu tai ficewarta. Sosai jikin maman Sa'id ke rawa da kakkarwa. Dan kuwa Lulu ta daketa ne a inda taji zafi sosai. Videos ɗin nan sun matuƙar tayar mata da hankali, har tana mamakin yaushe Hawwah duk ta ɗaukesu batare da ita ta sani ba. Na biyu matsayin Lulu da hatsabibancinta akan shari'ar duk da ta saka a gaba. Na uku zancen siyasar mijinta da tai matuƙar ƙwallafama rai da buri a yanzu tare da matsayin ɗan uwanta da shima take taƙama da tinƙaho da shi a duk inda ta shiga. Idan wannan damar duk ta kufce musu ai ta shiga uku wlhy, dan za'a mata dariya matuƙa. Itafa dama kishiyar uwar yarinyar nan ce ke sake tunzurata akan tsanarta (Umma), duk da dai dama bata sonta kasancewarta ƴar talakawa, dan taso ace Sa'id yay auren kece raini ne na ƙwarya tabi ƙwarya. Amma ya ƙare da auren ƴar malam shehu......

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.