Furar Danko Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: FURAR DANKO 1.txt
Chapter 71 of 94
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmuðŸ˜ðŸ™_*
ð“ð²ð©ð¢ð§ð 📲
 🫗 ð™ð™ð™ð˜¼ð™ ð˜¿ð˜¼ð™‰ð™†'ð™Š.....!!🫗
      ð‘©ð’Šð’ð’šð’ ð‘¨ð’ƒð’…ð’–ð’ð’ ð’„ð’†ðŸ¤™ðŸ»
ð‘ªð’‰ð’‚ð’‘ð’•ð’†ð’“ 6ï¸âƒ£8ï¸âƒ£
......Ba ita kaɗai ba, hatta shi ma kallon da sukema junan na ƙarshen ƙwal uwar daka na matuƙar zafafa masa garkuwar jiki, amma ya zaɓi nuna jarumtar nan da duk aka san Aliyu Zakin fama da ita ta taurin zuciya da tsaurin shanyewa ya ƙi janyewa. “Gamawata na nufin karɓar umarni na, saɓanin hakan kuma.. hummmm!†yaƙi ƙarasawa sai danne lips ɗinsa da yay da haƙori cikin tabbatar da gargaɗi. Itama saita danne natan da salon muzuba mu gani tana mai ɗaura ɗayan hanunta saman nasa da ke akan natan ta turesa masa. Komai baice mata ba, sai lumshe idanun nasa yay kawai. Saman gadon ta koma ta zauna tare da ɗaukar laptop ɗinta ta cigaba da abinda take yi batare data sake ko satar kallon inda yake ba. Sai dai zuciyarta taƙi samun nutsuwa dan kalamansa ne ke faman mata kai da kawo. Ba wannan ne karo na farko daya mata irin waɗan nan kalaman a cirkuɗe ba, na baya ma kuma sun cimata rai da zafafa ta harta ƙagautu da son jin fasararsu, amma na yau sai batajin suna mata raɗaɗi ƙagautuwar ce kawai ke zaburar da zuciyarta akan hasashen mai iya fassara mata su. Karan farko da taji tana ɗan kewar Nadiya, amma kuma hakan bazai sa tai kiranta ba. Duk da kuwa ta turo mata tarin sakwanni na ban haƙuri amma tai biris, hatta taron bikin nan Nadiya tata roƙon son zuwa, anan ne ta mata reply da cewar (ba'a buƙatar ki) da ga haka kuma bata sake bi takanta ba. Su Afrah kam bata ganin sunada hankalin da zata iya sakasu a sabgarta. (Mubeen ko su Hussain) zuciyarta ta ayyana mata. Mubeen ai ƙaninta ne, ita kuma bata son raini gara ma su twins ɗin, gamsuwa da hakan ya sata ɗaukar wayarta ta shiga WhatsApp, abinda bai dameta ba sai abu mai muhimmanci ya taso mata. Dubawa tai dan ganin wanene online, sai taci sa'ar ganin Hassan dan haka tai masa sallama sannan ta rubuta masa kalaman da Smart ya faɗa mata, (dan Lulu fa irin mutanen nan ne masu ƙwanya matuƙa, tanada saurin ɗaukar abu da haddacesa, ko'a makaranta ƙuruwace ta gaske da kaifin brain yasa zama popular ga malamai da ɗalibai, dan ma abubuwa da yawa sun faru da suka so taɓa mata karatun musamman ma harkar shaye-shaye ALLAH dai ne ya ƙaddara da rabon zata haye da amsa suna lawyer a yanzun). Sai dai anyi rashin sa'a tana turawa Hassan na komawa upline, sai kawai ta ajiye wayar da tunanin bari ta bashi mintuna tasan zai dawo, idan ma bai dawo ba zatai kiransa. Ta cigaba da aikinta sama-sama har akai kiran isha'i, har lokacin kuma Smart na'a ɗakin yana karatu ne shiyyasa shima hankalinsa ba'a kanta yake ba har sai da akai kiran sallar sannan. Yanzu ma koda yace tazo suyi jam'i bata musa masa ba, bayan sun idar ne ya dakatar da ita daga yunƙurin tashi ta hanyar tura mata littatafan da malam Nasirudden ya bashi. Littatafan ta zubama idanu, kafin ta ɗago ta kallesa fuska a tsuke.
    Kafin ma tace komai ya bata amsa da “Naki ne, zamu fara karatu sai ki shirya. Dan ya kamata kisan addininki. Hakan ne zai sake tabbatar miki da ke wacece, ki kuma san yanda zaki bautaba UBANGIJI, ki yima mahaifiyarki da Æ™asa ta rufema idanu addu'a, ta haka ne kawai zatai alfahari da ke dajin farin cikin barin baya da tayi, zaki san yanda zaki roÆ™a UBANGIJI da miÆ™a masa kukanki akan bukatunki ya amsa mikiâ€.
   Yana gama faɗa ya miƙe batare da jiran cewarta ba. Tayi niyyar maida raddi akan maganar farko, sai dai ta ƙarshe tai mata takunkumi da hakan, tana son mahaifiyarta matuƙa, tana tsananin begenta kuma. Duk abinda zaka jingina mata da ita yana saurin sanyayata koda batai niyya ba tayi, balle ma ita in dai akan neman abinda duk za'ace ilimi ne da zai amfaneta bataga dalilin dazai hanata amsa ba, a ganinta hakan ribarta ce, ta ƙara koyon abinda bata sani ba....
*_WASHE GARI_* kamar jiya kowa a ɗakinsa ya kwana, garama shi yaɗan leƙata kusan ƙarfe uku na dare daya idar da sallar daya tashi yayi. Samun ɗakin a buɗe ya bashi damar shiga, sai ya sameta tana barcinta a cikin lallausan duvet ɗin gadon, ta rage hasken tabar mai pink. Wayoyinta ya ɗiba duka biyu ya fita da su, kusan akansu ya ƙarasa daren sai gabannin asuba ya kwanta, ana kiran salla kuma ya tashi. Yau ma ya tadata yin sallar, sai dai yana fita ta koma tai kwanciyarta har sai da ya dawo yay mata jan ido sannan ta tashi. A lokacinne ya ajiye mata wayoyinta ya koma can ɗakin ya kwanta sai barci.....
     Kusan takwas da wasu mintuna ta kammala shirinta tsaf, tayi matuÆ™ar Æ™yau cikin skert da riga na atamfa da suka fiddata tsaf, kamar kullum babu kwalliya, É—an kwali ma bata É—aura ba dan bata iya zaman wahalar É—aure-É—auren nan dama a gida Afrah ke mata. Sosai ta baza Æ™amshi aka toshe ido da glass bayan ta yana Æ™aramin veil a kanta ta naÉ—esa a kafaÉ—unta. Dan Æ™yau kam tayi Æ™yau kamar ka saceta ka gudu. Cikin takun nan nata na yanga da gayu ta fito É—auke da tarkacenta, sai key É—in motarta da aka kawota da ita kaÉ—aice a nan É—in sauran ba'a kawo mata ba. Kanta tsaye ta doshi hanyar fita, sai dai me tana taÉ“a Æ™ofar ta jita a rufe. Ƙaramin tsaki taja da duban agogon dake a tsintsiyar hanunta. Sam bata son makara, dan haka ta nufi kitchen da nufi fita ta Æ™ofar baya, sai dai nan É—in ma É“am. Cikin É—an jin takaici ta rumtse idonta da komawa falon, kayan hanunta ta zube a saman kujera ta nufi É—akin Smart. Yana tsaka da barcinsa ya ji ana bubbuga masa gefen filon daya tada kai, da Æ™yar ya buÉ—e idanunsa da ke jingim da nauyin barci ya sauke a kanta. Kauda natan tayi da ga kansa a gadarance ta ce, “Malam bani key zan wuce. Ka wani bi ka rurrufe Æ™ofofi kamar a prisonâ€.
     Kallonta yake shi dai da ga sama har Æ™asa har takai Æ™arshen maganarta. ƘoÆ™arin tashi yay zaune ya jingina da gadon ya harÉ—e hannayensa a Æ™irji rabin Æ™afafunsa zuwa Æ™ugu lulluÉ“e cikin bargo.â€
    “Malam ka tsaya kana kallona kamar wata hoto, bayan kuma kaji na faÉ—a maka bana son na makara ko? Inada important abubuwa a officeâ€.
    Wani É—an jan idanunsa yay kamar zai lumshe sai dai kafin ya rufe É—in ya sake buÉ—esu a kanta. Cikin yanayin muryar wanda barci bai isa ba da É—an taÉ“e fuska ya ce, “Ban fahimceki ba, sake maimaitawaâ€.
   Kallon takaici ta watsa masa. Dan ta fara hasala. Amma sai ta danne da Æ™yar a É—an zafafen dai ta ce, “Wai kai miyasa komai a wajenka abin wasa ne. Kasan ko mi kake yi? Ka bani key ni ba neman jidali nake baâ€.
      “Humm ke idan ance miki ki fita a yau a kuma haka yanda kiken nan sai ki fitan?â€.
Harara ta watsa masa cikin gatsali da faÉ—in, “Sai ka hanani fitar idan na tashiâ€.
“Okay haka kika ce? To ko zan tabbatar miki ko Æ™ofar gate bazaki fita ba, idan kema kin shiga duniyar mafarkinne sai ki farka, dan idan har kinga kin fita a gidan nan da sunan aiki sai next week ma. Sannan bada wannan shigar ba idan har kina son aikin naki kenan. Dan bazan hanaki yi ba saboda wasu dalilai na, amma ba'a yanda ranki ya raya miki ba. Yanzu a Æ™arÆ™ashin ikon Aliyu Mika'il Idris Mawashi kike ba su Daddy ba. Abinda ya tsara a gidansa dole shi za'ayi ko ana so ko ba'a so. Garama ki nufi kitchen haÉ—a mana break fastâ€. Da ga haka ya juya yay kwanciyarsa. Wani irin Æ™arajin kiran sunansa ta Æ™wala a matuÆ™ar zafafe. Sai kawai yaja filo ya É—aurama kansa ya toshe kunnuwansa ma ya maida idanunsa ya lumshe. Masifa ta fara zazzaga masa zuciyarta na raÉ—aÉ—i kamar zata fito ta baki, amma bawan ALLAHn nan yay biris da ita, da ya ga ma filon bazai masa ba sai ya É—auki bluetooth É—in sa da ke a bed side drawer ya manna a kunne ya saka Æ™ira'a abinsa. Fita tayi a É—akin dan ta fahimci sai ta haÉ—ashi da Daddy. Wayarta ta cira a handbag ta shiga dannama Daddy kira. Bugu biyu kuwa ya É—aga dan fitowarsa a wanka kenan shima zai yi shirin office. Kafin ma yace wani abu ta sakar masa kuka da faÉ—in, “Daddy kaga mutumin nan ko? ALLAH ina raga masa ne saboda abinda Baba da Uncle You suka cemin, amma idan ya ce muyi ta inda ya É“ullo zan hargitsa masa rayuwa, nifa babu lallai babu dole zan dawo gida Daddy, garama komi Baban zaiyi yayi....â€
    Duk da abinda Daddy keji na yunÆ™uro masa shima sai ya danne da Æ™yar, cikin tausasa harshe ya ce, “Baby kinga relax mi yake faruwa? Mi yay miki?â€.
   “Daddy Office fa zanje yabi ya kulle Æ™ofofin, naje ya bani key amma yay min banza yama saka bluetooth a kunne wai babu inda zanje sai next week, irin like kamar wata baiwarsa da ya saya a kasuwar bayiâ€.
  Ƙololuwar É“aci ran Daddy ya kai, a taÆ™aice ya ce “Ina zuwaâ€. Ya yanke kiran, number Smart ya lalubo a karo na farko ya danna masa kira. Kasancewar bluetooth a kunnensa ya sashi jin shigowar kiran a bazata, hannu ya kai ya zare guda É—aya yana kai hannu kan wayar tasa ya É—auka dan ganin wanene mai kiransa haka. Bai san number É—in ba, dan baida Number Daddy, kamar zai share sai kuma dai ya É—aga gudun kar yay mistake.
    “To sannu isashsheâ€.
Kalmar data fara dukan kunnensa kenan a maimakon sallama.........âœï¸
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.