Tmw Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: TMW BOOK 3.txt
Chapter 12 of 86
Sajida sai ta kara zooming din Hoton ta na gani kafin tace"Tabbas ba musu itace, kinsan ai fara ce sosai shiyasa na ga neta. Big sis sadiq me zai ja mana? Ba dai ya koma Bin matan aure ba ne?
Ta fad'a cikin tashin Hankali, Surayya ta Girgiza mata kai kafin tace"Ba na wannan Tunanin Sajida, a sanin da na yi ma Sadiq mutum ne mai ilimi da sanin ya kamata, ba zai aikata haka ba."
Sajida ta koma ta zauna da yarta a hannu lokaci d'aya ta na fad'in"Big sis kaina ya Daure? Ko da bikin ne suka had'u da juna?
Surayya na kallon wani gefe tace"Ba'a lokacin ba ne, sun jima da sanin juna Sajida."
Sajida ta yi shuru kafin tace"Big sis wlh na shiga Rud'u, me ke shirin Faruwa ne?
Surayya ta koma ta zauna gefen Sajida Ta na fadin"Koma wacece to alaqar da ke tsakaninsu ba ta haramci ba ne."
Sajida tace"To alaqar uwar menene tunda ba aure suka yi ba?
Surayya ta kalleta kafin tace"In kuma ace sun yi auren fa? In kuma ace ita din MATARSA CE.!"
SAi Sajida ta zabura kafin tace"Matarsa?
Cikin Dimuwa, surayya ba ta sami zarafin magana ba, kiran Saddiqa ya shigo wayarta da Sauri ta Daga.
Mirmishi kawai ta ke yi na dacin zuciya da takaici, Saddiqa na gayamata ta tura mata adireshin inda Hasiya ke zaune, kuma har da karin Shedar mijinta ma'aikaci ne a garin Abuja.
Surayya ta yi ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa mu bar mganar nan a tsakanin mu uku, bayan mu kada najita a waje, ni da Sajida gobe in sha Allahu zamu tafi zariya domin mu kara Tabbatar da zargin mu."
Saddiqa tace"Gaskiya ya kamata, ni wlh duk na Rude, Umma kawai na ke tunawa, fata na Allah yasa ba Sadiq din mu ba ne"
Surayya bata ce komai ba ta katse wayar, a ranta ta na tunanin suna ma yaudaran kansu ne in suka ce wai ba Sadiq din su ba ne.
Sadiq ne shine ajikin wannan Hoton ba wani ba.
Sajida ta katse mata Tunani da fadin"Me zamu je yi a zariya?
Surayya ta mike ta na fadin"Sanin gaskiya, da kuma sanin abunda ke Boye game da Rayuwar kanin mu da bamu sani ba Sajida."
Sajida sai ta kasa mgana itama har taji idanuwanta ya kawo kwallah.
Me sadiq ya ke aikatawa ne a wannan garin? Daman shiyasa ya nace ma garin, har Sa'insa ya fara yi da su saboda haka ashe ashe.
Allah yasa ba abunda suke zargi ba ne Allah ma yasa kama ce ba shi ba ne.
Surraya tace bayan su uku kada wani yaji wannan mganar sai ta gama Bincikan gaskiyan Lamarin
Sannan tace ko Sadiq kada su bari ya Fahimci wani abu.
Za su je zariya kuma zasu tono abunda Sadiq ya dad'e ya na Boye musu.
Daman kuma ta Fahimci hakan Tuntuni, rashin Hujja ce yasa ba ta taba Furtama kowa ba.
Sun Rabu da Sajida akan sai goben, Direban mijin Surayya zai tukasu zuwa zariya, ita kuma Saddiqa daga bangaranta surayya tace ta jira su Dawo daga zariyan
Saddiq ita kanta hankalinta a tashe ya ke, Wayau ta yi ma Khairiya tace ashe Hasiya kawar wata kanwarta ce, sai daga baya ta ganeta, daman kuma ta rasa lambarta ta na son adireshin Hasiya saboda kanwar nata na son in ta shiga zariya taje wajen Hasiya.
Shine khairiyan tace bari ta yi ma kanwar nata mgana, sai gashi har da lambar Hasiyan aka Turo mata.
Daga khairiya har Safiya ba su san abunda hakan zai haifar ba.
Ballatana Hasiya da ke chan bata san abunda ke faruwa ba.
Uwa uba Uban gayya Sadiq da ke chan Abuja kan aikinsa bai taba kawo ma kansa abubuwa zasu lalace masa batare da ya sani ba.
*Janafty*
*TMWBK3004*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65
*LAME NIG!*
*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*
Washegari.
Zariya.
Yau Alhamis muna da karatu a makaranta, ammh saboda yadda na tashi cikin nauyin jiki yasa na yanke shawaran bazan fita ko'ina ba.
Kafafuna ne na lura yau sun kara tasawa, sannan kamar cikin jikina ya sauka a saman kafafuna haka na rika ji, Dakyar na iya tashi na yi shara da goge goge saboda wajen kwana hud'u ban iya taba komai acikin dakin ba.
Assadiq ya kirani Tun asuba shi ya ma tasheni sallar asuba, kuma bayan na idar ya sake kirana mun yi mgana, sai da ya tabbatar da lafiyata kalau sannan yace na koma na kwanta na Huta.
Ban yarda na fad'a masa yanayin da na ke ji ba, yanzu sai ya d'aga Hankalinsa ya kasa natsuwa, kuma naga lalurorin ma su cikine, shiyasa ban gaya masa ba dama ya tambayeni zan shiga makaranta ne sai na amsa masa da Eh! Har kuma yace zai Turomin kud'i ya na tunani na hannuna sun yi kasa.
Ko da na gama gyaran dakin nan, sai da koma na zauna ina ta faman Numfarfashi na tsawon wani Lokaci sannan na tashi na shiga kitchen na Dumama ragowan Tuwon da Maman Suhailat ta zubomin jiya.
Tuwon masara miyer karkashi, rabi na ci jiya na rage na safe, ga uban wanke wanke jibge na fara tunanin ko na kira Adda Fati ne Habiba tazo? Domin har ga Allah zan sha wahala in nace zan tsaya na yi wannan wanke wanke.
Sai da na gama cin Tuwon sannan na fara Tunanin wanke kwanukan, abun dai sai a hankali ina yi ina faman Hutawa, kafin na gama baya na ya kage, kafafuwa sun kara nauyi, ko gyara kitchen din ban yi ba, na koma cikin Daki na kwanta da na huta sosai har sai da naji ina jin barci barci.
Sai dai ban kwanta ba, ta shi na yi na sake ruwan zafin da na saka a kittle, na shiga wanka na gasa jikina, da na Fito sai na Shafa mai, saboda kaya na duk sun matseni na dai na saka su, iyakata Dogayen Riguna da T.Shirt da riga da zani.
Kuma duka sun yi datti, na had'a zan kira Habiba ta zo ta je gidan Adda Fati da shi ta wankemin, Tunda ni dai yanzu ina gabda daina Daukan Laluran kaina.
Sai na Bude bangaren da Kayan Assadiq suke cikin Wadrope d'ina na Dauko wata farar T.Shirt dinsa na saka na dauka ma zata yi min yawa Tunda ta na da fad'i ammh sai naga ta shigeni gabadaya, sai na had'a ta da wani zanin Atamfata na saka Hula.
Wayata na dauka na yi masa Hoton kaina da Rigar ina Dariya a raina nace in yazo zan nuna masa rigarsa har ta faramin kad'an.
Game na fara yi a waya ta, daganan bansan Lokacin da barci ya kwasheni ba, sai da naji kamar daga sama ana ta Bugamin kofa, na mike da sauri wajen saukowa daga kan gado har sai da naji kafafuwana sun sage, kuguna ya amsa sai da na tsaya na yi salati na d'an sarara sannan na fita zuwa falo ina kokarin gyara hulan kaina.
Har na isa kofar dakin knooking a ke yi cikin Sanyin murya nace"A na zuwa."
In da ace nasan abunda zan gani in na Bude kofar nan, na tabbata ko da kud'i aka had'ani bazan taba Budewa ba.
Gwara rashin Budewan akan Bud'ewan, ina jin d'an cikina na Motsi lokaci bayan Lokaci ammh yau da na ga Yan'uwan Assadiq Tsaye a gaban kofar dakina sai da naji kamar abunda ke cikina yafi d'aya, Saboda yadda cikina ya murd'a naji ta ko'ina ana juyi tare da irin naushi kamar dai akwai abunda yafi d'aya acikin cikina.
Tsabar kad'uwa yasa sai naji kamar an kafeni a wajen, bakina na rawa tare da kiftawam idanuwana, zuciyata kuma ta na barazanan fitowa waje saboda Tsabar tsoro da Firgici.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.