Tmw Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: TMW BOOK 3.txt
Chapter 64 of 86
Sadiq kuma Tuni ya bi umarnin Umma ya fice abunsa bayan ya gama Hararata kamar Idanuwansa za su fad'o, ni kuma na kauda kai ni na yi hakane Saboda a samu masalaha ni bani da damuwa su je can ni sai na zauna anan tare da su Umma.
Allah na Tuba wani Dare ne jemage bai gani ba? Ai sai dai daran mutuwarsa.
Abba kuma ya Cigaba da fad'a akan su Sajida Mama ce ta kara da cewa"ai ni ko su Salima nace su fita sha'anin shiga abunda ba ruwansu, kada su je su ja da ikon Ubangiji."
Umma tace"Suma ki kyalesu lokaci suke jira, duniya zata koya musu hankali, ko ni da na haifi Sadiq din na saki nace Allah yasa albarka to su kuma Munafunci me suke ta kai kawo a kansa?
Ni dai duk ina zaune ina jinsu, Sultana kuma na ta jan majina ta na Shesshekan kuka, Umma ta kalleni tace na tashi naje na shirya tunda zamu kama hanya ne.
Abba ma yace haka ya kamata Kada magajin gida yazo yana jirana.
Nima Umarninsu na bi na koma Bangaren Umma na cigaba da shiryawa.
Can sai ga Sultanan ta Shigo bangaren Umma, ta kuma bi ni har cikin Dakin da na sauka ta iskeni na gama had'a kaya na da na su Asim gabadaya.
Assadiq kawai na ke jira ko sallama bata yi ba haka ta shigo kanta Tsaye.
Na dago ina kallonta cikin mamaki ammh dai ban yi mgana ba.
Sai na maida kaina kan wayata na Bude data muna Chart da Safiya rokonta na ke yi, ta taimaka in na dawo ta rakani cikin makaranta na yi Screening.
Ganin haka yasa ta tsaya a gaba na rike da kugu tana fad'in"Dole ki kalleni ki watsar mana, kinsan dai nafi karfin ki nesa ba kusa ba ni a Budurwa Yaya Sadiq ya aure ni ke fa? Bazawara sauran wani, kuma ma kin ji kunya mai kwacen mijin wasu kawai."
Ta karishe fad'a cikin Rashin kunya, ina jinta sai dai ban tanka mata ba.
Mirmishi kawai na yi na dago ina kallonta kafin nace"To nagode sosai."
Na maida kaina kan wayata a karo na Biyu.
Sai ta ji haushin ban Biye mata ba, cikin kara Tusamin haushi tace"Uhm ki kara ma Bokan ki kud'i, tunda aikinsa ya yi kyau ga shi Yaya Sadiq zai tafi dake Abuja, sai dai ina so ki sani wlh Tallahi yana can ne ammh zuciyarsa na tare dani, in a baya kina Fariyan saboda ya'yan da kika haifa ne nima cikin gareni kuma nima in sha Allahu yan Biyu zan haifa sai naga karyan Tsiya, har Umma da ke sonki yanzu sai ta daina da ke da ya'yanki dama a rashin uwar daki ta yi na kishiya."
Saboda na kara Tusa mata haushi sai na kara Dagowa ina fad'in"Allah ya baki yan uku ma in dai Alheri ne ina miki Fatan haka."
Ta murgud'amin baki lokaci daya ta na shafa cikin jikinta tace"Ohon miki dai, kyaji da munafunciki."
"SULTANA..!"
Mukaji muryan Assadiq daga sama a tare muka juya muna kallonsa yana Tsaye a kofar dakin sanye da Shadda Tazarce har da hulansa na bakar Dara.
Bamu da masaniyar ya dad'e a wajen, kuma yaji duka maganganun Sultana ko daga yadda ya ke bin Sultana da wani kallo na zaki gane kuran ki.
Shigowa dakin ya yi a Fusace lokaci d'aya yana fad'in"Sannu rasa kunye beran tanka, nace sannu da aiki."
Kanta na kasa ta fara fiki fiki da ido na alamun bata da gaskiya.
Ni kuma muryata a kasa nace"Sannu da zuwa.'
Kallo daya ya yi min ya kauda kai cikin kaushin murya ya kalli Sultana Lokaci d'aya yana fadin"Kada ki manta ba ke na fara Aura ba, ita na fara aura kuma a bisa al'ada itace Uwargida tana gaba da ke a wajena sannan a shekaru ma tana gaba da ke, ban ce ki sota ba, saboda daman ba ke ce daman ya dace ki sota ba. Ni ne ya dace da na sonta Tunda ni na ijiyeta. Ammh ki sani ya zame miki Dole ki koyi girmamata matukar kina son zama lafiya tare dani, in kuma baki so ki Cigaba da tozarta ta, ni kuma na yi alkwarin kare darajarku gabadayan ku, bazan kuma lamunci d'aya na cin mutumci d'aya ba."
Ya karishe fad'a yana nuna Sultana da yatsa.
Cikin gwaron Numfashi ta kwaso magana ya dakatar da ita da cewa" Bana son jin komai, na riga naji komai malama, ki fita ki bama mutane waje kawai."
Ya fad'a ya na nuna mata Hanyar Fita, ai sai gata sumu sumu ta fice ta na wani sunne kai kamar mutuniyar kwarai.
Ganin yadda ya Harzuka yasa na kallesa ina fad"in"Ka yi hakuri Assadiq"
Cikin kuramin ido yace"Ba hakuri zaki bani, ke ce zan gayama gaskiya ni ban ce ki zauna tana miki tozarcin da taga dama ba, ki rike girman ki yadda zata gane kina gaba da ita."
Kai na gyad'a kafin nace"In sha Allahu, ni ban ma Biyre mata ba."
Kai Tsaye yace"Kin yi kyan kai, kayan kin gama had'awa?
Ya fad'a yana kallon akwatuna da ke tsakar dakin, sai na gyada masa kai sannan nace masa Eh.
Bai ce komai ba ya kwashi akwatunan zuwa Haraban gidan Lokaci d'aya yana cemin na shirya yanzu zamu tafi.
Ganin tafiyar da gaske gaske tafiyar ne sai duk jikina ya yi sanyi, Na je bangaren Innani na yi mata sallama ta rike hannuna ta na fadin"Yar nan ina jin dadin zama da ke kuma zaki tafi?
Farida na gefe tace"Innani kuma Abuja fa Anty Hasiya zata koma inda Yaya Sadiq ya ke aiki."
Innani tace"Shi magajin gida can Habujan zai tafi da ke?
Sai na gyada mata kai kafin nace"Eh Innani haka yace"
Innani ta ja numfashi zata yi mgana sai ga Assadiq ya shigo tare da su Asim dama nace ya karbo su su yi sallama da Innani.
Hannuna ta saki ta rike nasu tunda Assadiq ya zauna a gabanta ya rike mata su.
Sai ga Innani na hawaye ta na shafa kansu, suma kamar sun sani suna ta jan hannunta.
Innani ta kalli Assadiq kafin tace"Tare zaku tafi da su can Habujan ne magajin gida?.
Cikin Sauri yace"In sha Allahu, ,Ammh yanzu Zariya zan kaita akwai abunda zata karisa sai zuwa nan da Sati biyu zan koma na Dauketa mu koma can gabadaya."
Innani tayi shuru kafin tace"ita sulsana nan zaka barta kenan?
Yace"Eh innani zata zauna tare da ku, zan rika zuwa ina ganin ku in sha Allahu."
Cikin gamsuwa Innani ta jijjiga kai kafin tace"Shikenan, da dai zaka yi hakuri ka bar min yan yara nan suna Debemin kewa magajin gida."
Assadiq ya yi mirmishi kafin yace"Innani ai suna shan Nono, ammh ki yi hakuri na yi miki alkwarin in aka yayesu nan gidan za su dawo hannun Umma."
Sai Innani taji dadi ta rika shafa kansu tana saka musu albarka.
Harda 500 ta kwance a hannun zaninta ta ba su, nima ta na ta sakamin albarka.
Har sai da Assadiq yace"Innani kwata kwata yanzu kin daina sakamin albarki d'in nan."
Innani na gyara gilashinta tace"Ai yarinyar nan sai dai Allah ya saka mata, nan ta ke zama tare dani duk abunda na ke bukata shi ta ke yi min dole kaji ina saka mata albarka matar taka yar kirki ce, ka riketa Amana da gaskiya Allah ya yi muku albarka gabadaya ya baku zaman lafiya da Zuru'a dayyiba, ya kuma raya muku ya'yanku cikin Addinin musulunci ya Had'a maka kan matanka gabadaya."
Ni da shi muke ta amsawa da Ameen Ameen.
Sai da na yi hawaye da Innani ke ta fad'in"Allah yasa mu gana.".
Ni kuma sai nace"In sha Allahu akwai rabon gwanawa a gaba Innani."
Ba ni kad'ai na yi kuka ba har Umma da Mama sai da suka yi hawaye Anty Surayya ma sai ta zo muka yi sallama
Umma ta had'amin sha tara na arziki kaya sabbi ta dinkamin su Asim kuma kaya sai dai su ba ma wasu, ga kayan wasa sannan Umma ta ce min duk abunda nake Bukata na yi mata mgana.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.