Best / Popular Hausa Novels

Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

Reading file: TMW BOOK 3.txt

Chapter 62 of 86

Sultana kuma ba Halin tace zata ga Laulayi ga makaranta dole ta na ji ta na gani muka tafi muka barta.
Shinkafi muka fara zuwa can naji abun mamaki,ana ta cewa Sultana tace ita yan biyu zata Haifa.
Umma tace bata sani ba, Cikin da bai yi kwari ba ne har ta san yan Biyu zata haifa?
Ni kuma har a raina sai na yi mata Fatan Allah ya bata, ni bata san na gada ba ne, iyayen su Amma kakkaninsu tagwaye ne kuma asalin Zuru'rsu suna haihuwan Tagwaye
Ita kuma Sultana saboda ni ne ta ke son ta haifi Tagwaye ita a dole sai ta yi kwacen son da ake yi ma ya'yana ya dawo a kanta.
Tab ni ko a raina nace iska na wahalar da mai kayan kara.!

*Janafty*
*TMWB3K016*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65

Kwana Biyar muka yi a shinkafi Daganan muka wuce Gummi ni da Umma, naji dadin garin Shinkafi sosai ba in da Umma ba ta kaini ba. Sai dai kiji ana nuna ni ana fad'in nice matar da Abubakar ya aura a Boye kafin ya auri Sultana.
Kuma ba tsamgwama ba Wulakanci gidan baba Sammani muka sauka nan muka yi kwanakin mu har muka tafi, Su Asim sun sha jagwalgwala kamar me, ba su wannan gidan ba su wannan gidan.
Da zamu taho kuma suka had'o min da kayan arziki, ni Alkalama suka bani da shinkafar Tuwo sai gyad'a aya da sauran tarkace sukace na had'a ma su Asim kunu ne, daga ganin yadda jikinsu ya yi fresh da kiba kunin alkalama na ke ba su.
A gummi ma mun samu kyakyawan Tarba Mallam zakari daman tun zuwan mu na Farko nasan halin kirkinsa.
Ya yi ta kara ce ma Umma ko ita fa? Ganin mu tare kad'ai ya kara sanyaya masa rai ya yi ta fara'a da murna ni kaina ya yi ta sakamin albarka tare da Nasihun zaman duniya.
Matansa ma alhamdulillah sun karramamu, Barin ma Inna mero ita Umma mahaifiyata ta Dade da rasuwa sai sauran matan mallam da yan'uwanta masu aure a garin duka mun ziyarcesu sun gani sun kuma ga su Asim sun saka albarka.
Anan dai kwana hud'u muka yi muka Dawo gida, Daura ne bamu samu zuwa ba, Assadiq yace na bari in Bikin Tahir ya tashi sai mu tafi gabadaya Umma na jin haka tace itama da Farko da taji zamu je sai ta ce mu bari mana Tunda ga Bikin Atrahiru na matsowa.

Wasa wasa fa na share watanni biyu da wani abu a garin Gusau kuma a dakin Umma Tunda har Lokacin Assadiq bai ce min na koma ba, ni kuma ban gayamssa na gaji da zama zan koma ba.
Daman kuma ya fad'amin na dauki kaya masu yawa tunda zan jima acan, sai dai jimawar ne ban dauka zata kai wattanin haka ba.
Sai da na zauna da Umma na kara ganin Tabbacin Abunda Anty Surayya da Assadiq ke fad'amin a baya a kanta.
Hakuri, sanin ya kamata da kyakyawan zuciya Umma ta na da kirki sosai da ba ta da bakinciki ko kyashi na yi mata Uzuri ya fi sau Saba'in Tunda na Fahimeta.
Na kuma san a irin  Labarina da yanayin auren mu ya kasance da Assadiq a matsayinta na uwa na Tsammaci abunda yafi haka Daga bangarenta.
Duk da ba zama muke yi mu yi Hira sosai ba daga gaisuwa sai abunda ba'a rasa ba. Mganar su Asim ma tafi had'amu Tunda ni dai tun zuwana ban san wahalarsu ba Umma ce da Mama sai Farida ke ta wahala da su ni kam sai in suna kuka a kawomin su na basu Nono, sai kuma in zamu kwanta da Daddare.
Ni iyakata in na tashi da Safe, mai Musu aikace aikace sai da rana take zuwa kafin tazo na gama gyara bangaren Umma tas tun Tana cewa na bari har tagaji ta kyaleni.
Ni na riga na saba da aiki Shiyasa ban iya zama, hatta Abun karyawa da Safe ni na kan yi, Har Abba ya sha cin girki na Wani lokacin da rana ne mai aikin kan Dafa ammh har na Dare in ya kare da naga Umma zata Daura sai na karb'a na Dafa.
Sultana kafin ta koma sai dai taci ta kwanta ita a dole mai laulayin ciki Alhalin in hira ne da yini ta na rike da waya ta iya shi.
Tayi wani abu da ya bani mamaki bayan Bikin Siyama.
Tunda taga Assadiq ya dawo bayan Bikin ta mike ta nuna taji sauki ta warke, Umma tace ya dauketa su koma Gidansu.
A lokacim ban Fahimci abunda ta ke nufi ba sai da ya gama kwanakinsa ya tafi tsakanina da shi sai gaisuwa ko tambaya game da abunda yara ke Bukata.

Ranar da ya koma Abuja ta kwaso kayanta ta dawo ma Umma wai bata son kamshin gidan sannan komai taci sai tayi amai ta barta ta zauna a wajenta kafin Assadiq ya dawo.
Mamaki ya kamani hatta Umma sai da ta Fahimceta kuma daga haka ta Samu sara da ya dawo zata koma gidanta yana barin garin zata Dawo wajen Umma har sai da Umma ta mata Fata fata tace ta zauna gidan mijinta bata son iskanci in abinci ne za'a rika aika mata da shi.
Tunda tana gani ta ji sauki har makaranta ta na zuwa ta kuma yini waya da charting sai taga mijinta ya Dawo ta narke masa su koma gidansu.
Kuma duk Saboda kada ya samu Sararin kebewa dani ne tunda ina Gaban Umma.
Ni bata ma sani ba, ko yana gari ban cika nuna kwad'ayina a kansa ba.
Wani lokacin ma nafi zama a bangaren innani da Rana tunda yanzu jikin Innani ya fara saki tafiya ma dakyar ta ke yi ko da Sandar bata cika ma yawan fitowa ba. Jikin tsufa sannan ga Shekaru shiyasa yau lafiya gobe Ciwo ga shi bata san asibiti sai dai Likita Abba ya Dauka ya na zuwa gida ya na Dubata.
Yanzu duk hiran Innani ba shi, sai dai ranar da taji jikinta da karfi zata saka akawo mata su Asim ta Biye musu su yi ta wassani, nima muna zence da ita Sosai yanayinta kad'ai in ka kallah zaka san Innani shekaru sun yi nisa duk da bata cikin wahala ammh jikinta ya fara saki na alamun shekaru ya fara tafiya.

Kuma ni in dai yana gari iyakata da shi mu gaisa shine ma ya yi ta kirana a waya yana son ganina kuma nasan Dalili saboda kada ma ya Rutsani a daki yasa ban cika zama a daki ba, in ba Falon Umma ba ina bangaren Innani Tare da Farida ina tayata kula da Innani da ta zama sai dai a lallab'a yanzu.
Sau d'aya ya tab'a min Magiya na bishi muka je Hotel muka kad'aice da sunan mun je gidan matar abokinsa kuma Tunda muka dawo naga kamar Umma ta Fahimci abunda ya Faru ban kara yarda na bisa ba.
Tunda dai ni kaina ban taba jin Labarin a garin gusau yana da wani aboki ba, d'aya na sani shine Tahir kowama shi ya sani.
Ko ya yi min magiya ba na Biye masa zuwansa na karshe har cewa ya yi na koma gidansa na zauna tare da Sultana kafin na koma zariya.
Ba halina ba ne yi masa gaddama ammh na tuna yadda na wulakanta ne a baya da ya kai ni Shiyasa da Sauri nace masa bazani ba, ya bar mata gidanta nima ina jin dad'in zama tare da Umma.
Kuma nace masa Anty Surayya ta na zuwa Lokaci bayan Lokaci ita da su Anty Sakeena.
Tunda bayan bikin Siyama duk naje gidajensu mun kara gaisawa, gidan su Sajida ne ban kara marmarin komawa ba.
Hatta gidansu mama naje, ni fa yanzu a gusau in da ban je ba kad'an ne sosai nasan gari.
A lokacin kallo na ya yi kafin yace"Siya yanzu ke sanin gari yafi miki Bukatun  mijin ki? Ni ne fa Assadiq din ki?
Ina marairaicewa nace"Ka yi hakuri To, ba haka ba ne kaga ina tare da Umma kuma naga kana da wata matar ba gauro ka ke ba."
Kallona ya yi na wani Lokaci kafin yace"Shikenan, tunda an hanani Babba, to ko sumbata ne a rika bari ina Rage zafi da shi."
Ban hanashi ba nima na taimaka masa muka samu natsuwa da gangar jikin juna.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.