Tmw Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: TMW BOOK 3.txt
Chapter 20 of 86
*Janafty*
*TMWBK3006*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65
Daren ya kasance mai tsawo a gareni, na kasa barci sai faman juye juye na ke yi, ga ciwon kai sannan ga cikina ya karamin nauyi.
Domin na sha wahala a motar da na shigo zuwa gusau.
Duk yadda Surayya ta rika lallashina da nacin na huta kada na damu babu abunda zai faru, sai naji na kasa jikina ya yi sanyi gabadaya gabbaina sun saki, in na kalli cikin jikina sai naji Rauni ya Rufeni, ba na so abunda muka aikata ya shafi d'an da ke Cikin mu, sannan gefe d'aya ina jin Matukar Tausayin Assadiq duk abunda ya faru ko zai faru saboda ni ce.
Da naga na kasa barci sai na rarrafa na tashi ina jan kafa na fad'a Tiolet din dake cikin dakin na Dauro alwala nazo na daidaici in da Anty Surayya tace min gabas ne na tada salla.
Dakyar na iya yin raka'a hud'u ina tsaye, da naji nagaji sai na koma na zauna saboda girman cikina kamar ana hurashi sai kuma ya koma kasan marata ya yi tulu kamar wacce ta shiga watan haihuwarta, alhalin kuma wattanin cikin wata bakwai ne.
Na yi addu'a sosai acikin daran nan da Fatan duk abunda zai Faru gobe kada ya zama mai Tsauri ga Rayuwata sannan kada ya zama mai kuntata ga Assadiq.
Sai wajen uku na dare na yi barci, kuma kiran sallar asuba a kunnina Tunda daren ne gabadaya ya yi min Tsawon da na kasa samun natsuwa ballatana na iya yin cikakken barci.
Ko da Surayya ta shigo ta tasheni sai ta iskeni ina salla a zaune, tunda da asuba da jan kafa na iya shiga bayi, kafafuna daman tun jiya suka kara Kumbura saboda zaman mota, sannan ga sallar da na yi a zaune da safen sai suka kara hayewa dakyar na ke tafiya.
Sai bayan na idar da sallah ta dawo mu ka gaisa cikin sakewa da Fara'arta kamar yadda na Fahimceta macece mai girmama Dan adam kamar irin Assadiq dina.
Ganin yadda na mike kafafun ne yasa ta kalli kafafun sannan ta koma ta na kallon Farar Fuskata lokaci d'aya ta na fadin"Sannu naga kafar ta tasa ne"
Mirmishi nayi ban yi mgana ba saboda jin nauyi sai itace ta cigaba da fadan"Allah yasa kada wannan yar mganan da za'ayi yau ya taso da naguda fa"
Ta karishe fad'a cikin sigar Zolaya, sai na kalleta kafin nace"Ban kai ga watan haihuwata ba, cikina wata bakwai ne fa."
Sai ta zaro ido ta na kara kallona kafin tace"Wata bakwai fa kikace Asiya.?
Sai na gyad'a mata kai alamun hakane cikin mamaki tace"Ikon Allah gaskiya kina da girman ciki ni da Randami, ni wlh na dauka cikin ya shiga wata na Tara ne"
Sai kawai na sunkuyar da kaina cikin Sanyin murya nace"Haka kowa ke tunani, ana ta mamakin girman cikina shiyasa nake jin nauyinsa a jikina da kafafuna."
Cikin Tausayawa Surayya tace"Sannu dole zaki ji kam, bari na samo miki man zafi ki shafa. Ya samu su sauka kafin mu tafi chan gidan."
Da Toh na amsa mata sai ta tashi ta fita ba jimawa sai gashi ta dawo ita da yaranta ta saka su, suka gaisheni na amsa ina tambayan sunayensu.
Namijine ke ma uwar rad'a sai tayi dariya kafin ta kalleni ta na fad'in"Matar Uncle din ku ce Sadiq, sunanta Asiya."
Sai ya waro ido kafin yace"Mommy ita Anty Sultanan fa?
Batare da wata Damuwa ba tace"Dukkansu matansa ne Khalil"
Zai kara mgana ta dakatar dashi da cewa su je su yi shirin makaranta.
Sai da suka fice ne sannan ta duka ta na fadin"Bari na taimaka miki."
Ita ta shafemin kafafuna da man zafin nan, tace zuwa anjuma zai saki yadda bazai takurani ba.
Ina tayi mata godiya kamar na yi kwallah ganin yadda ta karbeni batare da ta kyamaceni ba.
Kafad'ata ta dafa cikin sigar lallashi ta na fad'in"Kada ki damu Asiya, ni a wajena da ke da Sultana duk d'aya ne Sadiq dai shine kanina duk da itama Sultanan kanwata ce, ammh a Ture wannan bangaran kuna da tudun matsayin matan kannena ne, kuma nice Babba a gidanmu in ban zama mai gyara ba, bazan so na zama mai barna ba kuma Dan adam ai ya na da Daraja bai kamata wani mutum ya kasance mai dariya ko wulakanta kaddaran wani wanda ba shi ya yi kansa ba."
Har ta fice ina jin kalamanta a raina sannan a gefe d'aya ina kara jin na samu natsuwa a cikin raina.
Kuma man zafin da ta shafamin naji dadinsa sosai, Assadiq ke raina shi na kira ammh sai wayarsa bata shiga ina da kyakyawan zato kila ya taso ya na kan hanya ne.
Adda Fati na kira, a raina nace gwara na fara fad'a mata kada Lamarin ya Rikice na koma da wani Labari wanda su ba su san dashi ba.
Da ta dauki wayata sai da tace min"Lafiya Hasiya?
Saboda taga kiran wayata da Sassafe, cikin Boye yanayina nace"Lafiya lau Adda Fati ya yara?
Ta amsa min Lokaci d'aya ta na tambayata ya nauyin jiki nace mata da Sauki sai tabini da addu'an Allah yasa na sauke lafiya acikin raina na amsa mata da Ameen.
Shuru muka yi na wani Lokaci ita kuma sai ta Fahimci akwai mgana a bakina cikin Wani yanayi tace"Hasiya..! Menene ke faruwa ne?
Cikin karfin hali nace"Adda ina gusau fa Tun jiya."
Cikin mamaki Adda Fati Dagachan bangaren tace"Gusai kuma?
Ta fad'a cikin Sigar Tambaya.
Cikin gyad'a mata kai kamar ta na ganina nace"Eh Adda, ina Gusai yanzu haka ina gidan yayar Assadiq a nan na kwama ma"
Cikin wani karin mamakin Adda Fati tace"Yayarsa kuma? Ke Hasiya yi min gwari gwari ni bangane ba."
Sai na gyara zama na muskuta saboda na gaji da yadda na zauna.
Cikin ajiyar zuciya nace"Labarin mai Tsawo ne Adda, ammh mafi muhimmanci ne shine Assadiq ba maraya ba ne, ya na da uwa da uba a raye sannan shi din d'an Dangi ne. A takaice dai iyayensa ba su san ya aureni ba sai yanzu da yayyensa mata suka gano hakan."
Adda Fati baki ta Bud'e cikin mamaki da Al'ajabi kafin ta samu zarafin magana na katseta da fad'in"Na kiraki ne na fad'a miki Saboda ki sani, ba lalle na dawo da aurena a kaina ba, in komai ya rikice ba su aminta dani ba zan sake dawowa a sakakkiyar bazawara a karo na uku."
Ban jira cewarta ba na kashe wayar Saboda kukan da ke neman kwacemim.
Ina jinta ta na ta sake kira ban bi ta kanta ba, sai ma kaina da na kwantar saman gadon dakin na fashe da kuka, sai da na yi ma ishi sannan na share hawayena, na koma gefe ina sauke ajiyar zuciya.
Acikin cikina nake jin motsin da yasa na Dafe cikin ina yar dariya, sai dai wani abu na bani mamaki ni fa ba Motsin abu daya na ke ji acikina ba, sanda naje awo na karshe na yi musu Complain suka kara yi min scanning suka kuma kara samun Tabbacin Rai d'aya ne aciki sai dai likitan yace ya Danganta da koshin lafiyan jaririn Cikina shiyasa na ke jin motsin kamar yafi rai d'aya.
Ni dai na yi shuru ne, ammh har acikin raina nasan abunda ke cikina yafi guda d'aya saboda nauyin da na ke ji, sannan a tare zan ji suna Taushin Cikina ta bangarori da Dama, na yi dai shuru tunda wannan ne na Farko sannan kuma ban isa na san abunda Allah ya Boye a cikina ba, ko su likitocin ai sai abunda Allah ya ba su ikon sani suke iya sanin.
Ina nan zaune sai ga Anty Surayya da Farantin kayan karyawa ta kawomin.
Tace naci na koshi sai na yi wanka na Shirya in mijinta ya fita aiki zamu tafi chan gidan
Cikin Sanyin jiki na amsa mata, alokacin bata ga idanuwana ba sai da ta dawo bayan na gama karyawa sannan ta lura da fuskata, cikin wani yanayi tace"Asiya ba nace ban da koken koken nan ba?
Sai na dukar da kaina kafin nace"Ban yi kuka ba Anty surayya."
Mirmishi ta yi kafin tace"Kin yi min karya , Saboda ai kinsan Fuskarki bata isa ta Boye kukan ki ba."
Nan ta ke na gane kuskurena da sauri na bata hakuri sai ta kalleni kafin tace"Ni baki yi min laifi ba, saboda kinga halin da kike ciki, matsalane wani abu ya sameki a cikin wannan yanayin naki shiyasa kikaji ina ta miki mganar ki saka natsuwa a ranki in sha Allahu alheri ne zai Faru."
Sai na jinjina mata kai, Tiolet ta shiga tace bari ta dauko Botiki Tankinsu ya lalace baya ba da ruwa sai an kira mai gyara.
Da kanta taje ta juyomin ruwan da ta sanya a gas ya tafasa ta kawomin tace na gasa jikina da kyau, ban mata musu ba na tashi na cire kayana na Shiga wanka kuma kamar yadda tace na gasa jikina sosai kuma naji dadi.
Da na fito man zafin nan da ta barmun na kara mulkema jikina Sai naji duk inda jikina ya Rike daga jiya zuwa yau ya sakeni.
Doguwar rigar Abaya na saka mai Ruwan kasa, tunda kayan Atamfofi sun daina shigata saboda kiban da na kara da kuma cikin jikina.
Nagama saka Rigar kenan ina Dauran gyalen kayan a kaina sai ga Anty Surayya ta shigo itama ta yi wankanta tas ta sha kwalliya sai tashin kamshi ta ke yi.
Kafin ma nayi magana ita tafara washe min baki,ta na fadin"Kin gama Shiryawan Asiya?
Da sauri na gyad'a mata kai alamun Eh, sai ta juya ta na fad'in"To dauko Hijabinki ki biyoni falo zaku gaisa da Dr ne."
Ba musu na dauki hijabina dogo wanda ya kaimin har gwiwa fari na saka nabi bayanta zuwa falo, na iske ta zaune ita da Mijinta da alamu ma yana Shirin fita ne.
Kaina na kasa na kariso tunda naji sanda tace"ka ganta dai Dr."
Nayi kokarin na Durkusa sai na kasa na rike baya ina Cije baki da Sauri yace"Ke zauna kan kujera a bunki, ina ke ina Durkushe a wannan Halin da kike ciki."
Jin haka yasa na zauna saman kujera kaina a kasa ina gaisheshi ya amsa Lokaci d'aya ya na kallona sannan ya na Bina da Sannu sannu.
Surayya ya kallah kafin yace"Allah Sarki itama ai yarinyace kamar Sultanan nan."
Surayya tace"Eh ko zata girmeta da kad'an ne, kila ta yi sa'ar salima."
Sai ya jinjina kai kafin kuma ya murmusa yace"Abubakar Sulaiman Shinkafi i like u Staryle, ina son kanin nan naki Surry, Yana da wani irin Confident da Natsuwa tare da Hankali."
Ta na kallonsa tace"Sadiq ne, Abba kan ce karamin su babbansu."
Ya na yar dariya yace"Gaskiya ya fad'a ko ni da na ninka shekarunsa bazan iya yin abunda ya yi ba, in kika Lura ko magana ki ke da shi farat daya zaki Fahimci ya na Tauhidi da kiyayewa Sabon Allah, ga shi he is so kind Mutum ne Simple Straighth Forward. Kai Tsaye zaka ga ya na yin abu ba shayi bakomai ga Tausayi da zuciyar Taimako."
Surayya na jin dadin kyakyawan Hallayar Sadiq da mijinta ke zayyanowa game da kaninta tace"Duk gidanmu ba kamarsa Sadiq na da kyakyawan zuciya."
Dr yace"Sosai fa, kema wani Lokacin kuna kamanceceniyar Hali shiyasa taku tazo daya sannan Namiji ne fa tsayayye, zai iya rike mata Hud'u kuma su zauna lafiya."
Ya dago ya na kallona kafin yace"Ya sunan ki ne?
Kaina na kasa nace"Hasiya!"
Cikin mamaki ya kalli matarsa kafin ya yi mgana ta Rigasa da cewa"Asiya sunanta."
Ina jinsu kamar zan ce ni ba Asiya sunana ba, sai kuma na fasa kada kuma na fara wuce iyakata.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.