Best / Popular Hausa Novels

Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

Reading file: TMW BOOK 3.txt

Chapter 46 of 86

Sun tafi da cewar sai ranar taron suna za su dawo in sha Allahu.
Sun tafi kenan ba jimawa sai ga Salima ta zo ita da Zahra'u da Fathihatu sai ya'yan gidan Baba Tanko su suka rakaso gidan Adda Fatin tunda ba su san gidan ba..ni na ke gayama salima zuwan su Anty Surayya nace mata yanzu suka tafi sai ta kirasu a waya sukace ai sun kama hanya sai ranar suna za su dawo.
Salima sai ta koma gefe da Zahra'u ne da Fathihatu muka yi ta hira suna ta santin yara sai dai abunda na Lura itama Salimar kamar cikin gareta.
Kuma da alamu tana son yara domin haka ta Daukesu ta na ta kallonsu ta na mirmishi.
Kuma ta yi ta daukansu Hoto, Da ta tambaayi sunayensu Habiba ta gayamata, sai tace ga sunan da Anty Surayya tace a rika kiransu ta yi mirmishi tace sunan ya yi.
Sun jima tunda Sai bayan la'asar suka tafi sukace mim sai ranar suna bayan sun gayamin sakon Hajiya Murjanatu tace tana yi min barka kafin tazo.
Zuwa Lokacin nasan haihuwata ta zaga gabadaya dangi, kuma da karin yan Biyun da na haifa yasa gidan Adda Baya Rabo da Jama'a.
Maman suhailat ma bata sani ba bata nan ashe tun washegarin Ranar da su Assadiq suka je ta yi tafiya, sai da ta dawo sannan tazo Dubani ni da twins ta na bani Labarin zuwan su Assadiq.
Ni kuma nace mata ai a ranar aka yi min aiki tunda a asibiti ma suka same mu ka yi ta yi jimami.
Mutanen gidanmu na samaru su mamanboy, sun ta zuwa asibiti Dubani kuma da muka dawo gida ma sun zo sau Biyu, Ramatu kuwa kusan nan ta ke yini sai da yamma ta ke komawa gida Nura baya nan na Haihu ammh ya yi min barka ta waya.

*******
Ana gobe sunan Twins  muka yi waya da Assadiq yace yaso ya shigo ammh bazai samu zuwa ba sai bayan suna.
Muna cikin magana sai yace zai kirani in ya gama mgana da Abba.
Ni kuma daman yace kada mu yi shirin komai kudi zai Turomin na shagalin suna da komai da komai.
Abunda ban sani ba Surayya ta same shi sun yi mgana da tagaji da sha mata kamshin da ya ke yi.
Ammh sai da ya nuna mata bacin ran meyasa bata gayamai ga abunda ke Faruwa tun farko ba?
Anty Suraya ta bada uzurin Saboda Halin da ya ke ciki yasa ta boye mganar ammh ba da wata manufa ba ne.
Da haka ya sauko suka yi mgana ya ce ta kara siyamin wasu kayan fitar suna ni da Twins a dinka sannan mganar abunda za'a yi na shagalin suna ita ta bada shawaran a tura mana kudi sai mu yi komai da kanmu Tunda Hakkin mu ne, raguna ne tace ba laifin in ya siya sai su tafi dashi a ranar suna da Safe in kuma yana ganin akwai walaha ko mijin Adda Fati zai iya wakiltawa ya Tura masa kudin a siya Ragunan ya yanka da Safiyar ranar suna.
Sadiq yace zai yi mgana da Abba, Har mganar Umma sai da suka yi yace Umma ko barka bata yi masa ba, shi kuma bai yi mata mgana ko a fuska bai nuna mata wani abu ba ya samu dai ta sauko ta na amsa gaisuwarsa.
Har mallam zakari sai da ya kirasa ya yi masa barka.
Surayya tace ya kyale Umma zata sauko a hankali ammh mganar su Sadiya fa? Ya kamata ya karbo wayar Hasiya da key din dakinta dake wajensu."
Shuru ya yi kafin yace"Kyale su dani, so na ke yi naga iya gudun ruwan su."
Da haka suka rabu a ranar kuma da ya yi mganar da Abba shima ya Goyi bayan haka Shiyasa da rana ya kirani yace na Tura masa lambar mijin Adda Fati da shi suka yi mgana.
Raguna uku yace a siya sannan ya Turo mana isheshen kudin Hidiman suna yace muyi amfani da shi.
Adda Fati da ta gayamin uban kudin da ya Turo sai da na yi hawaye na kirashi ina yi masa godiya.
Sai kawai yace komai zai yi min bai biyamin kwatakwancin karamcin da na yi masa a rayuwa ba.
A ranar da yammah sai ga Goggo Husai tare da babbar yar Goggo Hassu ita baza ta samu zuwa ba sai Matar Baba Sammani uwargida sun taho daga Shinkafi Domin hallatar taron suna.
Assadiq yaji dad'i sosai shi daman bai ce kowa yaje suna ba wanda yaga dama ne yaje, Innani daman tace in taje suna ba mai kara yi mata wayau ya dawo da ita magajin gida shi da kanshi yace a barta acan sannan itama Siyan zai gayamata Innani zata Tsaya ta kwana Biyu in ba haka ba sai ta kara tada wani Fitinan kuma.

Bayan bayan sun dawo daga sallar Mangariba Shi da Abba, sai Abba ya wuce bangarensa shi kuma sai ya Shiga bangaren Innani ya kara gaisawa da baki suka taba Hira sama sama daganan ya baro su zuwa Shashen Abba ya ci karo da Sultana Tunda aka yi haihuwar wannan ne gani na Biyu da ya yi mata.
Ganin Farko zasu tafi makaramta ta gaisheshi ya amsa fuskarsa a had'e.
Sai kuma yau abunda ya bashi mamaki bata yi masa barka ba daman kuma baya Tsammanin haka Daga gareta Shifa tunda ta nuna masa bata da kunya ya fita sha'aninta..bazai zauna yarinya karama na wasa da Tunaninsa ba.
Kallo daya ya yi mata ya dauke kansa ya so ya wuceta ne sai yaji ta na gaishe shi sai ya Tsaya kad'an yana amsawa.
Kuma ya tsaya ne yaga ko zatayi mgana yaga kuma ta wuce bangaren Umma ya bita da kallo.
shifa yanzu an gama kuresa bazai kara matsa mata ta koma ba, ta yi ta zama tana Biye ma Umma har sai Lokacin da tagaji da ganinta a gabanta tace ta koma shidai kam ya Riga ya gama Tsara matakin da zai Dauka.
Bangaren Abba ya shiga cikin sa'a kuma sai ga Umma da Abba sai Sadiya da Sajida daman dazu yaji muryoyinsu a shashen Umma da Rana shiyasa yaki shiga.
Shifa Tun da yaji Labarin abunda suka aikatama Siya yaji baya son ko ganinsu bai kara yarda sun had'u ba kuma ya gama sanin duk masu kaunarsa acikin yan'uwansa da wad'anda suka kirasa suka yi masa barka da wad'anda suka ja da Hukuncin Ubangiji duk ya san su, kuma ya yi ma kowaccen su wajen zama.
Umma ce kadai bai riketa a rai ba Tunda ita c din sha Kudun ce uwa ce bashi da yadda zai yi da ita ammh su yana da yadda zai yi da su, tunda ba wacce ta haifesa acikin su. Sannan ba wacce ta taba daukan Laluransa ballatana iyalansa.
Ko a hidimar suna nan da kudinsa ne na banki tunda duk wattanin da ya yi yana jinya ma'aikatarsu duk wata suna saka masa albashinsa.
Sannan Abba shi ya ba shi kudin Raguna duk da yace ya barshi ammh yace kada ma yace komai.
Da su ya samu ya yi hidimarsa sannan ya Tura ma Tahir kudinsa da ya ara lokacin haihuwar siya.
Sanda ya shigo ba su san da shigowarsa falon ba tunda yanzu in dai acikin gida ne baya tafiya da sanda ya fara lallaba tafiya hakanan.
Sai in har zai yi tafiya mai nisa ne ya ke dogara sanda.
Ba su san ya shigo ba ya yi tsaye a kofar bangaren Abba da farko ma kamar ya koma sai dai mganar da yaji Sajida na gayama Abba ne yasa ya Dakata.
Karan Surayya suka kawo domin ba su da kunya.
Domin sunga Abba ya yi musu Shuru haka ma shi ma, da ita kanta Surayya shiyasa suke Tunanin ba wanda yasan abunda suka aikata.
Mgana suke akan taki saka su cikin Lissafin wad'anda za su tafi suna Zariya gobe Sajida ta kirata a waya taki Dauka kuma taje gidanta ta yi mata wulakanci shine suka zo suna gayamai ta ya ya zata ware su, ai suma yan'uwan Sadiq ne.
Tsabar yadda mamakinsu ya kamashi sai da ya murmusa yana tsaye.
Abba ne ya hangosa sai ya kira sunansa.
Dalilin da yasa suka san yana falon kenan duka suka waiga suna kallonsa.
Umma kuma na gefen Abba,  ita su Sadiya suka fara samu da mganar tace su gayama Abbansu itama Surayya ta rainata yanzu sai tazo gidan nan bata nemeta ba.
Itama tana so Abban ya tambayeta hala ita ce uwar sadiq din? Domin taga ta zake da yawa akan Lamarin shi da bakar Annobar yarinyar nan. ita fa ba yan Biyu ba ko yan goma ta haifa ma Sadiq bazata kaunaci bala'i da Annoba a kusa da magajin gida ba.
Kuma ganin daga Sadiq din har Abba sun yi banza da ita basa ma mata maganar sai ta fara rena kanta itama ta kwaso kananun maganganunta bata ta san zata bare da su ba.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.