Tmw Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: TMW BOOK 3.txt
Chapter 66 of 86
*Janafty*
*TMWB3K017*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk
Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haÉ—in mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan.
Sultana dai ta gama makircinta da kokenta kokenta na kada Assadiq ya tafi dani Abuja hak'anta bai cin ma Ruwa ba.
Na dauka daga wannan Lokacin ta Saduda ashe ba haka ba ne, ta fito da wani Sabon Tsirfa ko nace tsohon ya yi da ba wanda bai san irin wannan abun na masu kishi ba.
Addabarmu ta fara yi sai muna cikin barci ance dare mahutane ga bawa ammh ita a wajenta bamu isa mu huta ba.
Karfe biyu na dare uku haka zata rika Kiran Assadiq kullum kuma mganarta daya ne, abunda ke cikinta sun hanata sukuni sun hanata barci.
Ko tace ta kasa tafiya maranta na Ciwo, karya dai da makirci iri iri sai kuma ta kira ta na kuka.
Kuma abunda ya bani mamaki tana wajen Umma ne ammh ba ta rabo da korafin wani abu na Damunta.
In yace aje asibiti sai tace ba na asibiti ba ne, da farko ya fara Biye mata sai da ya kira Umma ya gayamata ita ta yi masa fad'a tace ya fita Batun Sultana sakarci ne ita bata taba sanin wani abu na Damunta ba, balle kuma har tace Cikin jikinta ya hanata barci sai kace ya yi watanin haihuwarsa.
Ashe bayan Umma tayi mgana da Assadiq sai da ta sameta har daki ta yi mata fad'a akan abunda take yi.
Shikenan Sultana ta saka kuka tana fadin ita ba'a son abunda ke damunta ba kuma anzo ana cewa karya ta ke yi.
Nima ranar ina zaune kusa da Assadiq Umma ta kirasa na so na tashi ya hanani, anan naji yadda Umman suka yi da sultanan a raina sai da na yi Dariya ita abun nata harda yarinyata ko rashin Hankali ne bansani ba ta na wani abu kamar wata yar fari.
Duk karshen wata ya ke zuwa Gusau in ya tashi dawowa Umma ta bashi abubuwa na amfanin girki tace a kawomin wanda dai tasan zai zama wahala in aka tashi nemansa anan.
Kuma ko da ya ke kokarin zuwa Duk karshen wata ya yi mata kwana uku bata gani, ita tunaninta na ba ta na fita Samun jin dadin Rayuwa.
Sannan Assadiq ya fi sona a kanta kuma ta na Tutuyar Ita a Budurwa ya aureta ni kuma ina bazawara ban Canchanci samun wannan soyayyar Daga wajensa ba.
Ko da yaushe ya tafi ya dawo cikin Damuwa ya ke da bacin rai duk da bashi ya ke fad'amin ba ni nake Fahimtar sanin ba wanda zai bat'a masa rai bayan ita.
Ya aureta domin Cika Umarnin da Biyayyan iyayensa ammh daidai da Rana d'aya bata bari ya Huta ba.
Muna da wata uku a Abuja ta samu Hutun makaranta Lokacin cikinta ya girma watansa na bakwai.
Karshen watan da yazo tace sai ta Biyosa tazo taga waje, Alhalin ko cikin yan'uwansa Anty Surayya ce kawai da Anty Sa'ima suka zo suma wani Biki ya kawosu a kuma ranar suka koma.
Sai Anty Subai ita kuma bikin Dangin mijinta suka zo, itama waje kawai tazo ta gani sai su Asim bata kwana ba.
Ai ko sun sha Rigima domin kai Tsaye yace mata bazata bishi ba, da ta kara sakaa masa kuka ya kira Umma ya gayamata yana ikirarin gaskiya ya gaji da Halin sultana.
Umma kuma ta zo har gidan taci Mutumcinta ta kuma ce ba inda zataje ita bata duba yadda cikinta ya yi nauyi ba, sai Zalama da kishi ne a gabanta ba Fatan Allah ya Sauketa lafiya ba.
Umma ta Rusa mata Tunaninta na zuwa Abuja taga a inda na ke zaune, ammh taji alwalashin in ta haihu sai taje sai dai ayi wacce za'a yi.
Ni bansan cewa ma ta kusa haihuwa ba sai watan gaba da zai je na biyosa saboda Umma su ga yara, ni kuma na Duba Innani da jiki ya kara rikicewa ga ido ya tashi yanzu ko gani ma batayi ga gilashin ammh ya daina mata amfani.
Assadiq da Abba sun yi sun yi ta bari a koma Asibiti Innani tace ba inda zataje a jagwalgwalata gwara su kyaleta har ta Allah ta zo ta Dauketa.
Yanzu Innani tafi karfin Farida ta kula da ita Umma da Mama ke kokari suma kowacce Lokaci bayan Lokaci ta kan leka taga abunda zata taimakama Innanin da shi Tunda ko da Sandar tafiyar ma sai an kamata.
Ga kuma laluran ido mai sa mai rai ya Mutu yana Tsaye.
Ni na matsama Assadiq ya Taho damu tunda kadaici duk ya isheni in ya tafi aiki dagani sai su Asim,su kuma tunda suka fara tafiya suka zama mab'arnata nata, yini na ke yi fama da su.
Ko Umma bata san tare zamu zo ba sai dai suka ganmu kwatsam aiko gida ya Dau murna ga su Asim ga su Asim.
Shashen Umma na sauka kamar yadda na Saba, ammh sai ta saka Farida ta kwashi kayanmu ta maida bangaren Assadiq.
Umma tace Abba ya ba da Umarnin indai nazo nayi masauki a bangaren mijina.
Sultana na gidan sanda muka Iso Tunda ta ganni shikenan Annurinta ya Dauke kallo nan dagani har ya'yana da kowa ke santin su ganin sun Fara tafiya bamu isheta ba.
Nima ko wannan karon naji mganar Assadiq da yace in bata girmamani ta gaisheni ba nima bai kamata na zubar da nawa girman na bita ina gaisheta tana min wulakanci ba.
Na ganta ta kara ramewa ko ni da Cikina na fita kyen gani ta yi baki sai kuraje sai dai haka ta rika Turamin ciki gaba tana wani tale kafa ko an gayamata ban ga cikin ba ne Oho?
Siyama na gidan muka iso ita naji tana yi mata kirari da Maman Biyu.
Sai bayan mangariba Assadiq ya kwasheta zuwa gidansu.
Shashen Innani naje gaisheta na iske ta sha magani har ta kwanta daganan sai na koma Shashen Mama itama na iske bata nan suna bangaren Abba ita da Umma tare da Asim.
Sai Siyama kad'ai na gani da tace min itama yanzu megidanta zai zo ya Dauketa.
To da yake ta na kirana a waya kuma sannan mu kan yi yar Hira a chart,sai na zauna muna hiran inda muka koma ina gayamata zaman bariki ba dad'i yanzu haka wajen mu Biyar ne a Estate din mu, mu biyu ne musulmai Kafayat bayarbiya ce itama.
Saurn duk ba addinimmu d'aya ba, ni da ya ke ba na fita ba ganinsu na ke yi ba kafayat ne ta shigo waje na sau daya muka gaisa nima na shiga wajenta sau daya.
Ita tana sona saboda su Asim sauran kuma sai dai daga nesa a daga ma juna Hannu ina gayamata na zama kamar mayya ni kadai a gida sai yara in Assadiq ya fita Office.
A bakinta nake jin Diraman Sultana kwanaki na sai ta bi Assadiq a Abuja sannan take gayamin ta gama yad'a cewa itama yan Biyu zata haifa.
Ina dariya nace"Allah ya ba ta."
Siyama tace"Tab Anty Siya wannan cikin na sultana bani da sanin gaibu ammh ina da tabbacin Daya ne aciki."
Ni dai ban ce komai ba sai dai na yi mirmishi.
Ban tambayeta ba ta fara fad'amin daman su Anty Sajida ke zugata kuma shiganta makaranta ta yi Sabbin kawaye suna Hore mata kunni.
Ni dai bakina kanin kafatana Allah ya kyauta kawai nace sai dai abun da ya bani mamaki da tace min har ita Sultana ta janye mata tunda ta samu masu bata Shawaran da ta ke so.
Ko kuma tana ganin tunda ita bata shiga jami'a ba yanzu ta wuce da saninta ni kuma sai na tambayeta me yasa bata Cigaba da karatu ba?.
Kai Tsaye tace mijinta yace ba yanzu ba.
Ni fa duk wani abunda Sultana ke yi ba na sani sai na had'u da yan'uwan Assadiq, tunda shi dai baya gayamin aiko zuwana naji mganganu kala kala na mganar kayan haihuwa tace ma Anty Surayya wanda zata siya mata yafi nawa Tsada sannan kuma ita yan Biyu zata haifa duka maza Saboda haka kayan jarirai na Guda biyu za'a siya.
Da Surayya tace mata a takardan Scan ance yan Biyu ne? Shikenan tace wai ta karyata ta, tunda Sultana ta fara zuwa awo kuma ba wanda ya taba ma ganin Takardan Scan din nata waya sani ko Assadiq din ya gani.
Karshe dai Anty Surayya ta tattara kudin siyayya ta mikama Sultana tace ta siya da kanta shine Ta kira Sajida suka shiga kasuwa tare suka siyo abunda suke so.
Da Assadiq yaji yace a kyaleta tayi duk abunda taga yafi yi mata daidai.
Anty Surayya ta ke gayamin da ta zo gidan muka shige shashen Assadiq in da na sauka muna mgana.
Da yake akwai shakuwa sosai Tsakanina da Surayya muna hiran da ya shafe su sosai tace ai yanzu na Riga na zama SS Shinkafi.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.