Complete Hausa Novels

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 19 of 125

"Ni daban, kai daban, bana so kana cin abincin ta, amman ba zaka jini ba"

Shiru yayi ya kyale Rayyan din, idan wannan maganar ce sun saba, Ayya tagaji, shi dinne ya kasa hakura har yanzun. Duk cikin karatun duniya da ake mishi babu wanda ya rike da kyau irin cewa Mami zata barbada mishi abu yaci. Abincin shi yaci gaba daci kan shi a tsaye, yana ganin Rayyan din ya mike ya dauko uniform din shi da safa

"Wanki zakayi?"

Kai Rayyan ya girgiza

"Me yasa zan wanke, Layla zata wanke mun"

Yanda yayi maganar zaka rantse da Allah Layla din yar aiki ce a gidan ba 'ya ba.

"Layla baiwar kace? Me yasa kaci ka takurama yarinyar nan ne wai?"

Kallon shi Rayyan yayi

"Me yasa ita bata damu ba sai kai?"

Kai kawai Bilal ya jinjina, yana kallon Rayyan din ya fita. Ba shiga bangaren Mami yakeyi ba, idan ba wani yaron zai daka ya ruga ya shiga bangaren nata ba, itama sam bata shiga harkar shi tunda rashin kunya yake mata kamar zai daketa.

"Layla!"

Ya kira, itama sai lokacin da ta zubama Bilal abinci ta samu ta zuba nata, tana zaune da remote a hannunta da ta kasa tsayawa waje daya taji ya kwala mata kira

"Rayyan ne ko?"

Mami ta tambaya, duk da muryar su shida Bilal din ba ko yaushe ake banbance taba, amman tasan idan Bilal ne zai shiga har ciki, ba zai tsaya daga bakin kofa yana kwala ma Layla kira haka ba. Cokalinta ta mayar cikin abincin tana mikewa, marin da yayi mata yau da safe ta fadama kanta tana zaune zai zo nemanta, zatayi banza da shi, haka ma tacewa Mami data shiga tana kuka

"Ina zaune zai kirani, kinsan Allah Mami ba zanje ba nima, kowa yayi harkar shi"

Murmushi kawai Mami tayi, ita yanzun ta daina tsoma bakinta a tsakanin su. Tun tasowar Layla idan Rayyan din yai mata wani duka har ranta Mami take ji, tayi fada da Ayya yafi a kirga kan cin zalin Layla da Rayyan yakeyi. Sau biyu ta taba kaiwa Abbu kara, duka lokutta biyun kuma tana shan kunya, dan ko muryar Rayyan din Layla taji da gudu take fita, sai ta dauki ido kawai ta saka musu. Yanzun zata shigo tana kuka shabe-shabe, tana fadar yanda ita da Rayyan sun raba hanya, sai ya aiko kiranta ta ajiye koma meye takeyi ta tafi.

Kamar yanzun da ta ajiye abinci, jikinta har kyarma yakeyi ta fita

"Ki wanke mun"

Ya fadi yana ajiye uniform din a kasa

"Yanzun idan na gama cin abinci"

Kallonta yayi

"Idan ba zaki wanke mun ba ki fadamun, tun dazun bakici abincin ba sai yanzun?"

Kayan ta tattara tana turo labbanta gaba, ta wuce ta koma ciki, tana jin tsakin da Rayyan din yayi. Sai da ya dafe kirjin shi duk da yayi kokarin ganin bai hada idanuwan da ita ba, amman sai da taja zuciyar shi ta doka. Ita kuwa cikin daki ta shiga

"Ni fa zan taimaka in wanke mishi Mami, amman shine wai ba zan gama cin abincina ba, zaiyi fushi ya dauka"

Murmushi kawai Mami tayi tana kallon Layla harta wuce da wankin tana kuma cigaba da mita.

"Allah ya kyautata kaddarar da take tsakanin ku Layla. Allah ya kare maraicin ki"

Shine addu'ar da Mami take bin ta da ita a lokutta irin haka. Har tsoro takeji idan taga sunyi wani abin ita da Rayyan. Ko yara batajin suna cewa Hamma Rayyan ya basu abu, amman wani lokacin zakaga Layla da abu kuma tace shi ya bata. Har kudi a cikin aljihun makarantar shi duk idan ya bata wanki

"Ki mayar mishi da kudin shi"

Mami kance idan ta nuna mata ta tsinta, amman sau biyu ta gwada tana shan maruka, yana fada mata yanda bayaso tana zuwa kusa da shi

"Hamma zai sauke Jujun shi a kaina Mami"

Ta bawa Bilal kuma sau biyu shima ya mayar mishi, saiya Bilal din ya dawo mata dasu yace mata ca yayi ta rike, yana sane yake bari, ba zai bata da hannun shi bane ba. Ba kuma zai bude baki yace ta dauka ba. Shisa har a ranta Mami tana tsoron kaddarar da take tsakanin Layla da Rayyan din. Bata da wanda zata furtawa ne kawai, tunda ita ba wasu kawaye gareta ba, sirrinta yana cikinta, gara ta zanta damuwarta da Haris da ta fadawa wani can. Shikuma yanzun ya sami gurbin karatu a Zaria, duk da yakan yi kokarin zuwa wani lokacin duk karshen wata, idan karatu yayi tsanani kuma sai yakai wata uku ma bata saka shi a idanuwanta ba.

Tana nan zaune, sai da Layla ta gama wankin tukunna ta dawo ta zauna tana daukar abincin

"Har abincina yayi sanyi"

Ta furta cikin yanayin mitarta

"Ki dumama"

Cewar Mami, kai kawai ta girgiza

"Nifa bama na son wanki, Mami kinsan bana son wanki, shine Hamma yake sakani"

Murmushi kawai Mami tayi, indan Layla ce ba gajiya takeyi da mita ba musamman akan Rayyan. Haka ta gama cin abincin tana mitar ta tashi ta wuce kitchen, kwanonin ba yawa garesu ba, ta daifi so ta wanke, sam batason aiki a kanta. Duk da akwai miya da yawa, Mami tace ko taliya sai a kara dafawa, gara tayi wanke-wanken saita fi jin dadin zama tayi kallonta a nutse. 

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 11, 2020

06

"Abbu...Sannu da zuwa"

Huda da take zaune a cikin falon ta fadi cike da farin cikin ganin shi, idan kaga yanayin autar ta Ayya zaka rantse tayi satika bata ga Abbun ba, a maimakon kwanaki hudu

"Huda"

Cewar Ahmadi yana dorawa da

"Ke kadai? Duk ina kowa? Ina Ayyar ku?"

Da murmushi a fuskar Huda har lokacin tace

"Kowa yana daki, Ayya tana sallar isha'i"

Numfashi Ahmadi ya sauke, a gajiye yake jin shi, ko dan tun da suka isa Abuja bawai sun zauna waje daya bane ba, hidimar da ta kaisu kawai sukeyi

"Ma shaa Allah, Ke kinyi sallar dai ko?"

Kai ta jinjina mishi

"Tun dazun ma... Hamma Bilal ne daya shigo sai yace inje inyi"

Wannan karin Ahmadi ne yayi murmushi

"Madallah da Hamma Bilal...bari inzo kafin ta idar"

Ya karasa maganar yana ficewa daga dakin. Kan shi tsaye bangaren Maryama ya nufa, ita da Jabir ya samu zaune a falon suna cin abinci. Jabir suna gaisawa ya dauki filet din shi yana ficewa

"Sannu da dawowa...kayi zuru-zuru"

Maryama tai maganar cike da kulawa, yar dariya Ahmadi yayi

"Yanzun nan? Ko dan ba zama mukayi waje daya ba, kinsan ni da nayi zirga-zirga sai fuskata ta nuna"

Murmushi tayi

"Hutu ne yai maka yawa"

Ta karasa maganar da sigar tsokana tana mikewa, tana jin dariyar da yakeyi. Ruwa taje ta kawo mishi, bata ma gwada mishi tayin abinci ba tunda girkin Maimuna ne, tasan ko yana so ba zai taba ci ba. Wani lokacin ita kadai takan yi tunanin ko duka maza haka suke da adalci irin Ahmadi, sosai yake duk wani kokarin shi na ganin yayi adalci a tsakanin ta da Maimunar

"Ya kuke? Fatan dai kowa lafiyar shi kalau... Na shiga in duba yaran a daku nan su dana shigo, ina jin basu dawo daga sallar isha'i ba"

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.