Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 45 of 125
"Hamma..."
Cikin ido ya kalleta
"Kina gwada hakurina Layla, kin sani ko? Wallahi ba zan sake magana dake ba"
Dogayen takalman kafarta ta cire, ta saka nashin, da kanshi ya kwashe nata ya saka a ledar daya zaro silipas din yana bata, karba tayi ta rike baqar ledar. Hannunta ya sake kamawa suna tafiya. A hankali har suka fara hango makaranta, ba hira sukeyi ba sam balle tace tafiyar tana mata dadi, amman yanayin Rayyan din ya nuna yana cikin nishadi. Musamman yanda ya kalleta yaga tana ta turo baki
"Ki maida hankali, kilan bakin ki ya rigaki zuwa hostel"
Ya furta yana kara sauri, yana kallon yanda take kokarin kamo shi tana kara turo baki, sai da tasa murmushi ya kusan kwace mishi, tunda dai babu yanda zatayi da shi. Har kusan kofar hostel din ya karasa da ita, inda sukaci karo da su Bilal su kuma, Aysha zata rako shi, sunyi tsaye suna hira
"Hamma!"
Ta kwala mishi kira tana murmushi, kallon su Bilal yakeyi da mamaki suna karasowa inda suke, hannun Layla da yake cikin na Rayyan ya kalla, bai amsa Layla ba saboda wani sanannen abu da yaji ya mishi tsaye a makoshi. Kirjin shi harya fara zafin da yakan mishi duk idan ya gansu tare haka
"Ayshan Hamma"
Layla ta fadi tana mata murmushi
"Layla..."
Aisha tace cikin gaisuwa, tana kallon Rayyan
"Ina wuni"
So yakeyi yayi mata murmushi koya ne, amman sam bayajin yi
"Lafiya kalau. Sannu da kokari, mungode"
Ya fadi, yana saka Bilal kallon shi cike da mamaki, Layla ma mamakin takeyi, shi kuma tun rannan yake so yayi mata godiya saboda tana ma Bilal kirki. Tun satin daya wuce yake hada kalaman da zai fada mata in sun hadu, sai yaune ya samu ya fada, baisan me yasa su Bilal suke kallon shi kamar sunga wani abu a fuskar shi
"Bakomai"
Aisha ta furta a kunyace, Layla zatayi magana Rayyan yaja hannunta sunayin gaba, ta cika surutu, baiga abinda zata fada ba kuma, bayan an gaisa. Tsayawa yayi yana sakinta hadi da fadin
"Tam sai da safe"
Kafin ta amsa ya juya, inda su Bilal suke tsaye ya karasa yana dan matsawa gefe hadi da jiran Bilal din, shima hakan yagani yayi sallama da Aisha din yana samun Rayyan. A hanya suka tsaya sunayin sallar isha'i sannan suka nufi gida. Sai da Rayyan ya tsaya wani shago ya siyi sigari.
"Ba zaka daina sha ba ko Hamma?"
Bilal yai tambayar da wani yanayi a muryar shi, sai da Rayyan ya zari kara daya ya kunna yana zuqa ya fitar da hayakin tukunna yace
"Me yasa kake magana a kai?"
Tunda yasan ba dainawa zaiyi ba, shima ya kamata yabar asarar bakin shi. Ba so ya daina bane bayayi, ko yanzun kamar dole ake mishi haka yake zuqar sigarin, kafin su karasa gida yasha kara hudu, yana shirin daukar ta biyar ne Bilal ya fisge kwalin daga hannun shi yana sakawa a aljihu, Rayyan baice mishi komai ba, haka da suka shiga daki ma baice mishi komai ba. Asalima kan tebir ya zauna ya fara rage tarin assignment din da yake gaban shi, yana kallon Bilal ma yayi nashi kafin ya fara danne-dannen waya da bazai wuce hira yake da Aisha ba.
Nan Bilal yayi bacci yabar shi, kwayoyin shi ya sha ganin Bilal din yayi bacci, amman har karfe uku da rabi ko gyangyadi, sai wajen hudu yadan kwanta, yasan ko da babu sallar asuba, da wahala baccin ya wuce awa daya. Rufe idanuwan shi yayi, baya ganin komai sai hotunan Layla kala-kala a cikin kan shi.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 28, 2020
13
Kwance Bilal yake yana nazarin wani lissafi, saboda har an fara test tun satin daya gabata, jarabawa nata karatowa. Amman Rayyan zaune yake yana zane, wani lokacin zaka rantse da Allah hutu Rayyan yake zuwa yi Zaria ba karatu ba, saima lokacin jarabawa, idan baka gan shi yana zane ba, to zaka iya ganin shi yana kwance shiru, tunda shi dai baya hada hanya da wata kafar sada zumunta, har dan whatsapp din da akeyi ma bayayi. Asalima wayar shi da screen din ya fashe yar karamar Nokia ya siya ya saka sim din shi a ciki.
Idan wani abu na makaranta ne daya kama sai an duba yanar gizo, da kwamfuta din shi kirar laptop yakanyi amfani. Kuma yana daya daga cikin mutane hudun da suke jagorantar ajin su ta fannin karatu, inda Rayyan dinne na biyu, idan da zai maida hankali ma tsaf zai zama gwarzo a ajin.
"Wai ba test kace kuna da shi ba?"
Bilal ya bukata, kai Rayyan ya jinjina mishi
"Ba zakayi karatu ba?"
Raba idanuwan shi da takarda Rayyan yayi ya kalli Bilal din, kallon da yake fassara "Da ni kake?". Kafin ya mayar da hankalin shi kan zanen da yakeyi
"Lokutta irin haka kana sakani inajin kamar bani da kokari"
Dan numfashi Rayyan ya fitar
"Kana da kokarin ne? Tun dazun kake kallon takarda daya"
Bude baki Bilal yayi, kafin ya mike zaune
"Kasan wanne lissafine? Kake kira takarda daya kamar wani abu marar wahala"
Fensirin hannun shi Rayyan ya ajiye, ya dan juya zaman shi yana mika hannu ya fisge takardar da take hannun Bilal, duba tambayar yayi, batare daya dago ba yace
"Ina misalin? Wanda akayi?"
Tashi Bilal yayi ya dauko jakar shi yana fito da littafi ya dubo wani misalin yana mikawa Rayyan daya karba, sosai ya nutsar da hankalin shi yana ganin yanda aka fitar da abin. Kafin ya fara duba wanda Bilal yake nazari, a idanuwan shi yaga yanda komai zai kasance, juyawa yayi ya ajiye akan tebir, cikin mintina kasa da sha biyar ya gama fitar da shi yana jefawa Bilal din
"Ba zaka maida hankali sanda ake maka abu a aji ba, kana can kana wasu tunane-tunane..."
Rayyan din ya fadi a fadace, dauka Bilal yayi yana duddubawa, murmushi yayi
"Bayani zakayi mun dalla-dalla..."
Hararar shi Rayyan yayi yana sake hade fuska, dariya Bilal yayi mai sauti wannan karin yana tashi ya janyo kujera ya zauna gefen Rayyan din daya ke watsa mishi wani kallo
"Ni kyaleni"
Ya fadi saboda surutu Bilal zai sa shi yayi, watakila sai yayi mishi bayani sau biyu ko fiye da haka, amman sai ya zaqulo wata tambayar yayi mishi. Haka kuwa akayi, har saida ya kule daya fahimci Bilal din ya gane, surutun kawai yake so ya saka shi. Ganin yayi Rayyan din yayi banza ya kyale shi yasa Bilal komawa kan gado abin shi, so yake ya sake fitar da lissafin a wata takarda daban dan yaga koya fahimta, shekarar shi ta farko ya fadi jarabawa guda daya. Rayyan yaita mishi fada kamar zai mare shi, wani lokacin ko bai niyyar karatu ba yakan dauko yayi saboda masifar Rayyan da ba karewa takeyi ba.
Ranar ne karo na farko da yaji kamar yayi dissapointing din Rayyan din, yanayine da baya so ya kara faruwa. Duk da kwakwalwar su ta bambanta, yana iya kokarin shi. Rayyan zanen shi yaci gaba dayi, amman baya tafiya yanda yake so, saboda yau ya kasa rufe gabaki daya tunanin shi kamar yanda yakanyi a lokutta irin haka. Layla ce manne a ran shi, tun jiya bai ganta ba, har wayarta ya kira amman a kashe. Yanzun ma wayar da take ajiye kan tebir ya dauka ya duba ko ta turo mishi sako, amman shiru, sake gwada kiranta yayi yana jin bata shiga ba, kamar matsalar network tunda ba'a ce mishi a kashe take ba
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.