Complete Hausa Novels

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 87 of 125

"Nawa ne zamu dinga biya?"

Yayi tambayar saboda har ran shi bayason takurawa Bappa din, bashi kadai ba har sauran mutane.

"Zan iya kiran Uncle dina in tambaye shi, amman ba ma shiri"

Numfashi Rayyan ya sauke, ya kula Bappa na da son maida magana da yawa wasa, kamar Bilal haka yake wani lokacin

"Da gaske bana son imposing..."

Kai Bappa ya girgiza mishi

"Karka damu, babu wata matsala, ka yarda dani shine saukin mu, idan ina da wani wajen ba zan zauna a gidan mutimin nan ba"

Cewar Bappa, kallon da Rayyan yake mishi yana saka shi karawa da

"Karka ce mun a cikin Uncles dinka babu wanda baka so"

Kai Rayyan ya girgiza mishi, bawai yasan sauran bane ba, zai iya kirga lokuttan da ya taba ganin su har suka gaisa. Cikin su Yaya Ayuba ne kawai ya sani sosai sosai. Kuma karyane kace akwai wani abu da zaka ki so a halayen shi. Mutum ne mai saukin kai, kusan zai iya cewa duka yan gidan su Abbu ne da sanyin hali, har matan daya gani kuwa.

"No way"

Bappa yai maganar cikin rashin yarda yana saka murmushi kusan kwacewa Rayyan din, bayason mutane, amman Bappa na da wani abu a tattare da shi da yaja shi hira haka har maganar ta tsawaita

"Ba kamar kai ba, ni ina son kowa"

Yayi maganar cikin sigar wasa, sosai Rayyan yayi dariya

"Karka manta karantar mutane ne fanni na"

Murmushi Rayyan yayi yana fadin

"Bana son mutane, ko kadan"

Kusan zaice ranar ne ya san menene aboki, menene magana da wani da bai hada jini da shi ba. Duk da cikin satin farko na zama da Bappa ya saka shi jin kamar zai dinga tsigar gashin kan shi saboda yanda Bappa yake tura shi bango, kuma dariya yakan yi

"Bafa zan zauna bana magana bakina yayi tsami ba"

Tunda sassafe zai fara bashi labari, wani lokaci saiya nemi wani abu ya jefa mishi, saboda sai da safen yake samu yadan runtsa bayan ya gama shiryawa, wajen karfe tara suke fita, amman surutun Bappa ba zai barshi ba

"Bacci kakeyi?"

Zai tambaya, ko yayi shiru ya kyale shi zai fara mishi surutu yana bashi labarai

"Wai akan me zaka dinga bani labarin da ban tambayeka bane ba Bappa?"

Ya tambaye shi wani lokaci, sai yaci gaba da kurbar shayin shi yana bashi labarin kamar ma baiyi magana ba, juyawa Rayyan yayi yana daukar dayan Pillow din ya rufo daga kunnen shi zuwa fuskar shi, kafin yayi amfani da shi yana jifan Bappa daya addabe shi, ko Layla bata takura mishi yanda Bappa yakeyi a yan kwanakin daya san shi. Sosai yake shigar mishi hanci, musamman ma akan magungunan da baisan me yasa yake sha a gaban shi ba, tunda ko Bilal baisan yana shan su ba.

Ranar da ya saka shi a gaba yana fada mishi illar kwayoyin da bukatar sake ganin likita tunda ba damar ya ga kan shi yana abusing magunguna haka kamar bai sani ba ya tura Rayyan din bango, sosai yake jin ya gaji da yanke mishi hukunci da Bappa yake dan yana shan kalar magungunan da yake sha, duk da ba kullum ba, kuma guda daya yakan sha.

"Me yasa kake tunanin ka sanni ne Bappa? Dan kana shan Anti-depressant baya nufin ka fahimci matsalata"

Cikin ido Bappa yake kallon shi

"Ka fahimtar da ni"

Numfashi Rayyan ya sauke, watakila idan ya fito da abin a fili yayi mishi saukin dauka, watakila idan ya fadama Bappa ya daina damun shi, ba zaice ga dalili daya da ya saka shi bude bakin shi da yake rufe da matsalolin shi duk shekarun nan ba, dan ko likitocin da ya dinga gani bai fada musu ba, har wanda sukayi tunanin bayan depression yana tare da post traumatic disorder wato PTSD, da sauran tarkacen ciwuka da suka shafi mental health.

"Bana son ganin Babana, ko kadan bana son ganin shi, bana son magana da shi, bana son duk wani abu da shi yake so. Koma menene idan ya nuna yana so zuciyata kamar wani na turata ta nisanta da abin... Idan ya matso kusa dani kamar zan mutu nake ji. Bappa babana fa, Abbu, bana son komai yana hadamu kamar ba daga jikin shi na fito ba..."

Rayyan ya karasa yana numfasawa da nauyin da abin yake mishi a zuciya

"Kowa na dariya da shi, suna magana, suna hira. Kowa nayi da baban shi, ni ban samu wannan ba. Ban kuma san dalilin da yasa na kasa samu ba, karka tambayeni. Ina tuna lokuttan da nake zama tare da shi, amman lokuttane masu nisa, bansan me ya faru ba lokaci daya..."

Ganin Bappa yayi shiru yana sauraren shi da dukkan hankalin shi yasa Rayyan cigaba da magana, a wannan bigiren baima jin zai iya yin shiru ko da yaso, duk da abu da yawa da yake damun shi din baisan yanda zai misalta ba. Kirjin shi ya dafa

"Kaman akwai duhu a zuciyata da kaina haka nake ji, duniyar duka bata mun dadin zama, ko karatun Qur'ani da nake samun sauki bana iyayi wata rana, jikina namun nauyi in tashi, ban san ya zan fada ka gane ba, amman bana jin dadi, na zabi Psychology dan in fahimci matsalata, amman babu abinda nagane, nawa ba depression bane ba, ya wuce haka"

Ya karasa da wata irin karamar murya, kafin shiru ya ziyarci dakin, siririn numfashi Rayyan ya sauke, akwai tarin maganganu da yake sonyi amman ya gaji, ba da surutun ba, da yanda zai hada abinda yake cikin kan shi ya zama kalamai. Gyara zama yayi da nufin ya koma ya kwanta, muryar Bappa ta daki kunnuwan shi

"Mu biyar mukai accident, Mamana, Yayyena guda biyu sai Kanwata, ni ka dai na fita..."

Kallon shi Rayyan yayi

"Ban san me yake damun ka ba, ba kuma ina kokarin nuna maka matsalata tafi taka bane ba, ina so ka fahimci komai zaiyi dai-dai, kowacce matsala tana da lokaci... Bana jin taka na da alaka da asibiti. Baba zai zo Kaduna nan da kwana biyu, sai muje mu fada mishi, kila zai iya taimaka maka"

Kai Rayyan yake girgiza mishi tunda ya fara maganar, shima baisan ya akayi ya fada mishi ba, bayajin bakin shi zai sake budewa a karo na biyu ya fadama Baba kamar yanda Bappa ya kira shi. Kallon Bappa din yake da wani yanayi na daban

"Allah ya jikan su"

Ya furta a hankali, kan da Bappa ya jinjina yana amsawa da

"Amin Ya Rabbi"

Shi yasa Rayyan sanin yaji me yace, saboda a hankali yaji muryar shi ta fito. Hidimar su sukaci gaba dayi bayan nan kamar kowa baisan ciwon kowa ba. Har kwanaki biyu suka cika, Bappa baice mishi komai ba, bai sake daga mishi maganar zuwa ganin Baba ba, duk da yaji sunyi waya sun gaisa. Jikin shi na mishi wani iri, musamman da ranar tazo asabar, su kadaine a gidan, sauran yaran da suke nan sai da ya gansu duk basu shige sa'annin Layla ba. Gashi suna da hankali, basa wani hayaniya suna damun su, ko falo suka zauna suna kallo da wahala kaji hayaniyar su, kuma zasuyi kasa da maganar tv din.

Har yamma suna gida a zaune, Bappa ya dafa musu taliya, kamar Haris, ya iya dafa abubuwa da yawa. Kuma mai dadi yakeyi musu ba irin girkin Bilal ba. Dan haka babu inda suka fita, yanzun ma yana zaune yana kallon wani film a laptop din Bappa, Chinese ne ma, amman yana mishi dadi, yaga Bappa ya mike, gyara zama yayi yana cigaba da kallon shi, har saida ya dawo yana fadin

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.