Complete Hausa Novels

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 67 of 125

"Abbu..."

Ya kira sunan na fitowa da gunjin kuka, ta ina zai fara yiwa Abbu bayani, me zaice mishi, me zai cewa Abbu, ya dade yana jin bai cika mishi alkawarin daya rike ba, ya dade nauyin amana na bibiyar shi, amman yau yake jin duniyar shi ta tsaya cak, kuka yake na yanda lokaci daya kaddara ta bude mishi shafin da baisan ya zai karanta shi ba balle yayi tunanin wucewa, saboda an kashe fitilar da take haske da rayuwar shi, duhu ya baibaye ko ina. Yau kuka yake da dukkan zuciyar shi, kukan maraicin da bai taba shi ba shekarun da suka wuce sai yanzun.

Ji yake kamar wani abu na ruri banda zuciyar shi, kafin kwakwalwar shi ta sanar da shi wayace, wayar shi ce take ihu, dakyar ya iya daga jikin shi ya rarrafa inda wayar take kan tebir ya mika hannu ya dauka, zuciyar shi nayo tsalle zuwa cikin makoshin shi ganin

"Hamma"

Rubuce a jikin screen din wayar da ta subuce daga hannun shi tana faduwa kasa, baiko matsawa yayi kamar wayar na dauke da wani abu da zai iya cutar da shi, sam a lissafin da yakeyi na mutanen da zasu tuhume shi Rayyan ya bace mishi, komai ya bace mishi banda Abbu har wayar ta yanke bai iya motsawa ba, tana sake daukar ruri wasu hawayen na kara zubo mishi

"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"

Yake fadi yana maimaitawa, yanzun kam ya tabbatar da wannan shafin da kaddara ta bude mishi shine shafin karshe, babu yanda zai ayi yai tsahon ran ganin wucewar shi, zuciyar shi bata da karfin daukar wannan tashin hankalin

"Ka kula da Layla, ka kula mun da Layla kaji Bilal, zuciyata na mun wani iri"

Maganganun Rayyan suka dawo mishi, sake durkushewa yayi, da yawan mutane in suka shigo su kaga Bilal din zasuyi mamakin ganin namiji kamar shi yana kuka haka, abin zai zame musu baqo, saboda an san namiji da juriya, shi da kan shi in da wani yace zai kuka kamar dan shekara biyu zai karyata, saboda bai taba hango rayuwa zata bashi wannan dalilin ba, amman yau kuka yake

"Me zan ce musu?"

Ya furta a zuciyar shi, ashe akwai wani abu da ba zai fassaru ba, ashe akwai kalar kaddarar da babu kalaman da zasu misaltata, ya akayi Layla ta zo dakin su? Yaushe Layla ta shigo dakin su?

"Sai kayita bacci kamar ba namiji ba, ka dinga rufe daki idan ba kowa a gida..."

Rayyan kan ce mishi, saboda kar a shigo a illata shi yana bacci, amman bai taba bacci irin wannan ba, bai taba baccin da za'ace Layla ta shigo har tahau kan gadon shi bai sani ba, har wani abu ya shiga tsakanin su haka

"Ko mafarki nake? Ko da gaske mafarki ne?"

Ya furta yana tashi zaune, fuskar shi harta kumbura saboda kukan da yakeyi, wayar shi ce take ci gaba da ruri, dakyar ya iya mika hannu ya dauka

"Layla"

Ya gani, cikin sauri ya daga yana karawa a kunnen shi, watakila da gaske mafarki yake, muryar shi a dakushe yace

"Layla..."

Sai dai yanayin tata muryar ya tarwatsa wani abu a cikin tashi zuciyar da ba yajin zai taba komawa dai-dai

"Hamma ba mafarki bane ba, ba mafarki bane Hamma..."

Wayar ce ta sake subucewa daga hannun shi a karo na biyu, sosai yake kokawa da numfashin shi, sai dai wannan karin a juye ta fadi, yana ganin screen din, baisan iya mintinan da ya dauka ba kafin ya ga kiran Aisha ya shigo, dariya yayi wannan karin, saboda abin ya fara fin karfin shi, nata kiran na yankewa na Ayya ya shigo

"Ayya..."

Ya kira wata dariya da ta fito da sautin kuka na kwace mishi, da gaske karshen duniyar shine yazo, sosai yake tabbatar da hakan lokacin da idanuwan shi da suke wani irin radadi suke kafe akan screen din wayar da kararta ta daina zuwa kunnen shi, yana kallonta in wani kiran ya yanke sai wani ya sake shigowa, kiran mutanen da kamar sun san abinda ya faru, kamar suna jira ya daga ne su fara jeho mishi tambayoyin da yasan bashi da amsar su...!

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 12, 2020

19

Har ta sauka daga cikin napep din jinta take kamar a wata duniya ta daban. Tayi gaba yayi mata magana

"Hajiya kudin"

Jakarta ta bude, bata san nawa bace ta dauko ta miqa mishi, tayi juya ya sake cewa

"Ga canjin, ko kin barmun?"

Hannu tasa ta karba tana zuba su cikin jakar da ko zageta batayi ba. Ta sha jin kalmar tsiraici, ta dauka tasan ma'anar kalmar, a da ta dauka tsiraici shine ka rabu da tufafin jikin ka, sai yau ta fahimci akwai tsiraicin daya girmi rabuwa da tufafi. Akwai suttura da ba kaya bane kawai yake saka jinta a ranka, haduwa take da mutane a hanyar hostel din, musamman da ta shiga, sai ta tsinci kanta da jan mayafinta tana kara gyara shi, babu inda yake bude a jikinta, amman jinta take kamar bata saka komai ba, kamar kowa na ganin duk wani tsiraici da yake tare da ita.

A daddafe ta karasa dakin su, babu kowa sai Anisa da take zaune akan gadon Layla din, da yake nata saman na Layla ne, in ba lokacin baccinta yayi ba anan suke zaman su, wasu ranakun ma in tayi bacci Layla bata tashin ta. Yau ita batayi lakca ba sai karfe sha biyu na rana. Tana dawowa ruwa ta kara watsawa ta samu waje ta kame ta dauki waya tana dannawa, da yake taci abinci a restaurant, yayarta ta turo mata banner din Zahra Tabiu. Su kan siyi Donut dinta sosai, matar karshe ce, taje gidan Yayar tata ne ta samu Donut, duk a tunaninta na Zahra Tabiu ne, ko da ta fada mata ita tayi sam bata yarda ba, sai da ta kwana taga tayi a gabanta

"Inalillahi... Anty yaushe kika koya? Ina kika koya?"

Murmushi Antyn tayi

"Zahra Tabiu dince fa ta koya kwanaki, kin san nayi saving lambarta saboda siyen Donut, to shine naga tana talla zata koya yanda akeyi online, dubu biyar"

Ware idanuwa Anisa tayi, zatayi abubuwa da yawa da dubu biyar

"Kuma har kika iya haka?"

Tayi maganar cikin rashin yarda, dariya Antyn tayi mata

"Akwai videos haka, sosai ake ganewa, dan su Ammar sun fasa mun screen din waccen wayar dana nuna miki, kiyi joining in zata sakeyi"

Batayin ba ko da Anty ta turo mata, amman duk wani Donut da zata siya sai taji kamar bai kai na Zahra Tabiu ba, shine da safe da ta tashi taga Anty ta turo mata banner din, ta zabtare rabin kudin koyarwar daga dubu biyar zuwa dubu biyu da dari biyar. Gara dai ta koya ta huta, in ta koma gida ta dinga cin kudin Yayyenta, tana da kwalayen Donut Fairy data siya, in sun ce tayi musu order sai ta karbe kudin tayi a gida ta saka a kwalin, in sun cinye tabi ta kwashe. Lambar wayar take dubawa ko iri daya ce da wadda take da ita +234 806 515 6303. Ta gama dubawa kenan ta ga ita din dai ce, sai ga Layla ta shigo dakin kamar an korota. Kallo daya Anisa tayi mata tace

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.