Complete Hausa Novels

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 26 of 125

Tana can tana tsoron Layla karta lashe kurwar Bilal, ashe lallabowa tayi wajen Rayyan, shiru yayi yana kallonta

"Tambayar ka nake kana jina"

Yanda yakan yi duk idan bayason yin magana an saka shi yayi dole shi yayi da fuskar shi yanzun ma

"Ina magana da ita ne Ayya..."

Ya amsa, yana saka kirjinta wani irin lugude, ko ita Rayyan baya tsayawa yayi wata magana da ita. Bilal ma ta kanga yana bin Rayyan din idan yana son magana da shi. Asali yaune rana ta farko tun tasowar shi da taji yace yana magana da wani har ya tsayar dashi dan basu gama ba

"Rayyan..."

Ayya ta kira wannan karin da bayanannen tsoro a muryarta

"Idan nagama zan shigo"

Ya fadi yana dauke idanuwan shi daga kan Ayya. Hannun Layla ya kama yana fisgarta cikin yanayin da yasata binshi dole, suna barin Ayya tsaye ta saki baki cike da mamakin abinda ya faru a gaban idanuwanta. Cike da ta'ajjabin da gaske a gabanta Rayyan ya damki hannun Layla batare da tunanin abinda yayi ba dai-dai bane a tafarkin addini idan bai guji bacin ranta ba, idan ma ji yake dan in aka bibiya ta wani bangaren ya hada jini da Layla, kuma sun taso gida, ai hakan baya nufin ita din muharramar shi ce.

Bayan wannan ma, yaushe Rayyan ya fara magana da Layla, yaushe ya sakata cikin jerin mutanen da yake kulawa, harma kusancin su ya kai na ya damqi hannunta ya jata subar waje kamar akwai zancen sirrin da sukeyi da bayaso ita taji. Rayyan fa, Rayyan dinta da take daukar kafafuwanta, ta karya matsayinta na mahaifiyar shi mai cikakke iko da hakki a kan shi ya taso yazo har inda take ya gaisheta, taje dakin su dan kawai ta saka shi a idanuwanta. Shine yau take ganin kusancin da tayi shekaru tana neman ta samu a tare dashi yana nunawa akan Layla, akan mayyar yarinyar da taki jinin ta wayi gari ko a tunaninta tajita, balle kuma ta saka ta a cikin idanuwan ta

"Bayana kike son gani Maryama... Sakani raba Ahmadi dake bai isa ba? Kassarani kike neman yi shisa kika kawo wannan mayyar..."

Ayya take fadi muryata na rawa, cikin tashin hankali kamar wadda ta samu tabin kwakwalwa. Gabaki daya hankalinta idan yayi dubu kowanne a tashe yake

"Tafdin... Na rantse da Allah ba'a isa ba...ina tunanin wuta a makera ba zanji tashin ta a bayan gari ba"

Duk tsoronta akan Rayyan, duk tunaninta akan halayen shi ta alakantasu ne da abinda tayi kuskure ya sha, sanadin da kawancen su da Khadi bai koma kamar da ba, saboda tayi da ita su koma wajen Malam taqi, sai tama dinke mata, sam ta daina labarta matsalolinta da ita. Gwaggo ce a lokacin kafin rasuwarta, idan ta matsa sai tace mata tana karbo taimako a wajen Malamin Khadi. To dan Rayyan ne ta dinga amso karya tambaya, da yana yaro in ta danne shi tana samu ta dura mishi, daga baya ba zai sha ba, banda abinci sai ruwan leda, ko ya tarya a fanfo, ko zobo ta hada Rayyan baya sha sam.

Bata san ba abinda yasha bane yake dawainiya da shi sai yanzun, bata dauka Maryama na bibiyarta da yaranta ba har yanzun sai yau

"Minna, Neja da Bidda ma ubansu yayi kadan wallahi, balle kuma wata yar banufiya da uwar rikon ta..."

Cewar Ayya, bacin rai da tunanin barkatai na maye gurbin tsoronta, tana murna yaronta ya sami gurbin karatu a jami'ar da ake ji da ita a fadin Najeriya, kuma Abbu sai alfahari yake da fannin da zai karanta shine ake neman kassara shi

"Wallahi da sake..."

Ayya ta furta tana samu taja kafafuwanta da sukai mata mugun nauyi tana komawa daki, kanta harya fara sarawa da tashin hankalin da take tunanin ya kunno mata kai.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 14, 2020

08

Da wani yace mishi zai iya shekara daya a wani gari daban, nesa da Bilal, nesa da Layla da bai taba tunanin kewarta zata danne shi haka ba zai karyata. Dare da yawa ya sha farkawa ko shan ruwa da yakan yawan yi ko kuma wani abu daban ya tsinci kan shi da kasa komawa bacci, saboda kawai yana tunanin Layla. Yana tunanin ko tana kewar shi ko batayi, ranar da zai tafi bata neme shi ba sam, yafi mintina talatin a tsaye kofar daki yaki fitowa yana jira ko zata shigo tayi mishi sallama, amman shiru, sai da ya taka ya sameta har bangaren Mami, duk da bai shiga ba a bakin kofa ya tsaya yana kwala mata kira, ko da ta fito sai ya rasa abinda zaice mata.

Lokutta da dama yakan zabi shiru saboda kalaman shi basu da yawa, baisan yanda zai fadi abinda yakeji ba, baisan me ya kamata yace mata ba, shisa ya zabi

"Tafiya zanyi..."

Kai ta dan daga mishi

"Allah ya tsare... Zaka dinga zuwa kaman Hamma Haris?"

Dan daga mata kafadu yayi, yana rasa amsar da ta dace ya bata, abubuwa ne masu tarin yawa a ran shi, ya motsa labban shi kenan ta dago idanuwanta tana saka zuciyar shi dokawa. Ya kasa sabawa da kalar su, kamar yanda ko kan hanya yaga giccin mage sai yayi da gaske ne baya zurawa da gudu. Sanin da wahala ya kara cewa komai ya sata yin murmushi

"Allah ya saukeka lafiya. Banda fada da mutane"

Baisan murmushi ya kwace mishi ba sai da tace

"Inalillahi... Hamma...murmushi kayi ko wani abune ya fadamun a ido"

Kai kawai ya girgiza wannan karin har zuciyar shi da yake ji cike da wani irin duhu a lokutta da dama yaji murmushin

"Kin rainani ko?"

Dariya tayi mai sauti

"Ni na isa"

Numfashi ya sauke mai nauyin gaske, yana kokarin kallon cikin idanuwan ta wannan karin. Ya rasa kalaman da zaiyi amfani da su wajen misalta asalin abinda yake ji. Dakyar ya iya jan kafafuwan shi ya juya yana tafiya. Sanda ya sake waiwayowa sai yaga bata nan. Abin ya mishi wani iri sosai. Yaso ace ta tsaya, yaso ace ta jira shi harya bace mata, amman batayi hakan ba. Bayan tafiyar shi yanayin yana yawan fado mishi a rai, musamman idan yayi kewarta.

A cikin shekara dayan, kusan idan ba karatu bane yayi mishi zafi, duk watan duniya yana hanyar Kano, kawai ya kula da abu dayane a shekarar game da Ayya. Batason yawan zuwan da yakeyi, da ta ganshi zai ga tsoro a cikin idanuwan ta, har magana tayi mishi wani zuwa

"Rayyan ba zaka natsu waje daya ba ko? Taya zaka fahimci karatu kullum kana hanya?"

Cikin idanuwa ya kalleta, yaso ya fahimci dalilin canzawarta lokaci daya amman ya kasa, yawan magana na saka shi ciwon baki wasu lokuttan, kuma idan maganar tai tsayi zaiji ta fara hau mishi kai, shisa baice mata komai ba, har tayi mitar ta gama. Sai da ya mikene tukunna yace

"Zan gaisheki ne daman"

Yana juyawa

"Allah ya shiryeka..."

Shine kalamanta da yaji kafin ya fice daga dakin. Bai fasa zuwa ba, gajiyar da yayi jiya ita ta hana mishi tafiya gida, da ciwon kai na gaske ya fito daga wajen jarabawar shi ta kare shekarar farko a jami'ar. Amman a daren ya hada kayan shi yana ajiyewa, yaji dadin hakan dan yana dawowa masallaci wanka ya shiga. Lokacin da yaje babu yanda Haris baiyi dashi ba da su zauna tare a gida daya, amman yaki. Shi sun kama gidane anan Layin Kasuwa. Da Rayyan ya tashi sai ya nema a Rufasi.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.