Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 86 of 125
"Idan har ba zaku iya ajiye haukan nan ku san muna cikin matsalar da ta fishi girma ba ku fitar mun daga gida, dan Allah ku duka ku fitar mun daga gida inji da abu daya"
Daga zuciyar shi yayi maganar, ba zasu kara daga mishi hankali fiye da wanda yake ciki ba, saboda a duniya baisan akwai irin wannan tashin hankalin ba, duk yanda yake dauka labaran kalar shi na taba shi, bai kai yanzun ba sam, ta ina zai fara? Yar shi da rayuwarta gabaki daya ta sauya? Amanar daya kasa rikewa? Ko kuma Rayyan da Mami take alakantawa da wannan barnar? Dan mutane basu dame shi ba, abinda zasuce bashi bane a gaban shi a yanzun. Yanda zai fara daukar wannan matsalar balle ya nemi mafitarta.
Wasu hawaye masu zafi Mami taji sun zubo mata. Ayya ma ji tayi kafafuwanta sun kasa daukarta, har ranta taji zafin abinda Mami ta fadi akan Rayyan, badan tasan halayen shi ba, amman zuciyarta ba zata taba yarda shi yayi wannan barnar ba. Kallon Layla tayi da ta saka fuskarta cikin hannuwanta tana wani irin kuka. Abinda duka yara suka kasa ganewa kenan, abinda in da yanda zatayi zata bi yara wanda suka kai Layla, wanda basu kaita ba, wanda suka girmeta daya bayan daya ta hasko musu wannan ranar, ta nuna musu tashin hankalin da zai biyo bayan kuskure kwara daya.
Abinda duk suke dauka wayewa aikin banza ce in har ta kasance ba'a karkashin inuwar aure ba. Jin dadin wani lokaci zai iya zama barazana da sauran zaman lafiyar da ya rage musu a duniya. Kuskure daya zai jefa wasu wasi a zukatan mutane kan Martabar su, da ta duk wani ahali nasu, kuskuren su zasu aikata, amman zunuban zasu raba da duk wani daya damu dasu ne. Sai da tsikar jikin Ayya ta mike gabaki daya da ta hasaso faruwar abin nan akan Rukayya, wani irin tsoro marar misaltuwa na dirar mata. Kafin ta tuna ta kula da Layla, sai taji kamar ba huruminta bane bincike saboda Layla ce, saboda ta tsane ta, ta kuma tsani Mami, ga shi yanzun abin ya samu wajen zama a kirjinta yana sakata jin daukar wani bangare a kason tashin hankalin da suke ciki.
"Ta fadi komai Ahmadi, komai banda dorawa Rayyan laifin nan"
Ayya tayi maganar cike da roko, kirjinta kamar ana hura wuta. Saboda batasan ya zatayi ba idan akace dan daya fito daga cikinta ne yayi wannan aikin
"Baki san na gansu rungume da juna ba? Ya zaki ce mun bashi bane ba?"
Mami ta tambaya tana kallon Ayya da take mata wani irin kallo itama
"Rayyan da Layla kika gani rungume da juna?"
Cewar Ayya, Mami na jinjina mata kai
"Saboda baki da mafadi ko rashin hankali shine kika sake barin ta kusa da shi? Maryama sai kika barta a kusa dashi in har kin gansu da idanuwan ki kamar yanda kika fada... Baki da hankali ashe? Auren mijin mutane ne kawai abinda kika iya, baki iya kula da tilon yarinyar da kike da ita ba?"
Ayya take maganar yau tana jin da tana kusa da Mami din sai ta dauketa da mari, tana jin yanda komai ya koma gefe sai kalaman Mami din, tana jin yanda har zuciyarta ta shafe mata matsayin Rayyan, so take taji me abinda ya kwance akan Mami tabar Layla ta sake komawa Zaria in har da gaske ta ga Rayyan rungume da ita. Saboda daga ranar da ta ga maganar banza a wayar Rukayya tsakaninta da wani a makaranta, ko duniyar zata hade waje daya tabar makarantar kenan, saboda bata da iko da yaron balle ta hana mishi bibiyar mata yarinya, amman zatayi ikon da Allah ya saka a karkashinta ta nisanta yarinyarta da shi.
"Ya ma za ayi ace tana da ciki baki kula ba? Ki kwana daki daya da ita ki tashi daki daya da ita kice mun baki kula wani abu ya canza a tare da ita ba? Sakarar ina ce ke?"
Daga Mami har Abbu sun kasa cewa komai, maganganunta ne suke shigar su, musamman Mami da take jin Ayya na zakulo kasawarta a matsayinta na uwa, yau matar da take dauka ta tsaneta, bata kaunar ta ganta ce take fada mata gaskiyar da bata da mai gaya mata ita, duk da gaskiyar tazo a kurarren lokaci.
"Kasan ta gansu rungume da juna? Ahmadi ka sani?"
Ayya ta tambaya tana kallon Abbu daya kara sadda kan shi kasa, bayason hada ido da ita, so yake dai labban shi su motsa ya roketa da tayi shiru, karta saka zakulo mishi nashi laifin, amman lokaci ya kure musu gabaki daya
"Ka sani kenan..."
Ayya ta fadi, shirun shi na tabbatar mata da ya sani, mikewa tayi tana wani irin maida numfashi, yau da yaranta ne sai ta hadasu ta zane su gabaki daya.
"Sai kaima kabarta ta koma ko? Saboda ba yarku bace ba"
Su duka suka kalleta lokaci daya
"Maimuna..."
Cewar Abbu, kai ta girgiza mishi
"Baka son ji nasani, amman ka duba zuciyarka Ahmadi, idan Rukayya ce zaka bari ta koma? Me yasa kabar Layla? Ni me yasa baku fadamun kun gan su tare da juna ba?"
Saboda tana da tabbacin zatayi tashin hankalin da ba zasu bar Layla ta koma ba, ko dan ta nisanta yarinyar da Rayyan. Amman sai suka barta, saboda suna ganin ita din marainiya ce, kamar komawar ne gatan da zasuyi mata, barinta da zabinta shine cikar soyayyar su. Juyawa Ayya tayi da nufin barin wajen ta hango Rayyan da jaka a kafadar shi, har ya kama hannun kofar dakin su, hayaniyar da yake ji ta rinjaye shi zuwa cikin gidan saboda muryar Ayya yake jiyowa. Tana ganin shi kuwa ta karasa ta kamo hannun shi
"Zo ka fada musu Rayyan, suji da kunnuwan su"
Binta yakeyi, amman idanuwan shi na kafe kan hannunta da yake rike da nashi, so yake yaji yanayin nan da yake ji duk idan tayi kusa da shi haka, amman babu, bayajin komai sai Ayya, sai yanda kusanci da ita bai saka zuciyar shi ciwo ba. Kamar mai yawo a duniyar mafarki haka yake jin shi, lokacin daya dauke idanuwan shi daga nata yana mayarwa kan Abbu da yake zaune
"Abbu..."
Rayyan ya kira a cikin sauki, a karo na farko a tsayin rayuwar shi. Wani murmushi mai sauti ya kwace mishi, ya sake kallon Abbu yana jiran sanannen yanayin nan ya taso mishi, yaji iskar wajen gabaki daya tayi mishi kadan, amman babu, sam bayajin kamar zai mutu idan ya kalli Abbu, ko sun kasance a waje daya kamar haka, shisa bai ga tashin hankalin da suke ba, yau baya ma ganin komai banda iyayen shi.
Waje daya Bappa ya samar musu inda suke bautar kasar
"Akwai gidan Uncle dina, Autan su da yake karatune a ciki da abokin shi, daki ukune amman, akwai extra daki da zamu iya rabawa da kai..."
Cikin ido ya kalli Bappa ba zai manta ba
"Ban tuna na fada maka ina son zama waje daya da kai ba"
Ya amsa yana saka dariya kwacewa Bappa
"Allah ya bada sa'ar neman gidan haya a garin Kaduna, zama dani ne saukin ka, kuma ina da mota"
Wani irin kallo Rayyan yake mishi, banda Bilal bai taba kwana daki daya da wani ba, sai dai Ayya lokacin da yana yaro. Amman da hankalin shi ko na rana daya, sai ranar daya kwana a Bauchi da Bappa din, yanzun kuma ba zai zamana kwana daya ba.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.