Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 96 of 125
Ya karanta wasikar yafi sau ashirin kafin asalin ma'anar ta ya zauna mishi, cikin wani irin tashin hankali ya fito daga dakin, tun daga bakin kofar yake fadin
"Ayya!"
Yana kara kwala mata kira harya karasa bakin kofar dakinta inda suka hade saboda daman ba bacci takeyi ba, kiran shi ne ya sata mikewa tana tahowa da sauri, ko da yana yaro kome yake bukata bai taba mata irin wannan kiran ba, yana ganinta kafafuwan shi na kasa daukar shi
"Ayya ya tafi... Ayya tafiya yayi... Bilal tafiya yayi ya bar ni... Dan ba zan yafe mishi ba sai nace ya tafi? Me yasa zai tafi? Ina ya tafi Ayya?"
Duka zancen shi a baibai take jin shi, jijjigata Rayyan ya fara yi, saboda yasan babu inda Bilal zaice bai fada mata ba, gara ta gaya mishi ya bishi ya dawo da shi.
"Ki fadamun inda ya tafi Ayya... Kinga ni me yace mun..."
Wasikar Ayya ta karanta, fahimtarta ne yake mata wahala saboda babu yanda Bilal zai tafi wani waje bata sani ba, balle ace irin wannan tafiyar, ture Rayyan tayi tana nufar dakin su ya rufa mata baya, kayan Bilal ne tagani a zube, batayi magana ba ta sake fitowa tana jin Rayyan na biye da ita har cikin dakinta inda ta dauki wayarta, tana mamakin yanda komai yayi mata shiru, lambar Bilal ta kira a kashe, duka lambobin shi a kashe, Rayyan ta kalla da shima yaji a kashe ne, kai dai kawai yake girgiza mata, duniyar na kara hargitse mishi, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su da wani irin matsananincin tsoro daya ziyarce shi
"Ayya dan Allah..."
Cewar Rayyan yana dafa bango ya sulale kasa, a cikin daki yake, amman duniyar duka yake ji tayi mishi fili, babu kowa a cikinta sai shi kadai, bai san inda zai nufa batare da Bilal ba
"Ayya ki ce mun bai tafi ba, dan Allah kice ya dawo"
Rayyan yake fadi yana jin iska ta daina kaiwa cikin kan shi, kafin wani irin duhu ya rufe mishi idanuwa ruf, yana saka Ayya tsugunnawa ta riko shi kafin ya karasa kaiwa kasa, kan shi a jikinta yake da wani nauyi da batayi zato ba, nata kan ta dora a na shi, tunda take bata san akwai tashin hankali makamancin wannan ba, a wahalce ta dago, muryar da zatayi amfani da ita wajen neman taimako take nema ta rasa yau.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 1, 2021.
27
Ko sallamar Abbu daya dawo daga masallaci kan shi tsaye ya nufo bangaren ta bataji ba. Zuciyar shi na wata irin dokawa ganin ta rike da Rayyan din
"Rayyan..."
Ya kira muryar shi na fitowa yar karama saboda tsoron da yake ciki.
"Me ya same shi? Me ya faru?"
Saboda ya ga fitar Rayyan din daga dakin shi, kuma lafiya kalau ya gan shi. Baisan me yake a kwance haka kamar gawa ba. Ayya da sai lokacin hawaye masu zafin gaske suka zubo mata ta dago tana kallon Abbu, bakinta take so ta bude tayi magana amman ta kasa, saboda zafin da zuciyarta takeyi. Ta dauka raba soyayyar Abbu shine abu mafi daci da zata dandana a zaman duniyarta gabaki daya. Saboda Abbu ne komai nata, sai yanzun da take tunanin inda Bilal ya nufa a cikin duniyar da babu aminci, a rayuwar da naka ma da wahala ya taimaka maka balle wanda baka sani ba.
Kafafuwan Abbu har rawa yake sanda ya kara bandaki ya dibo ruwa ya dawo. Da kan shi ya tsugunna yana dibar ruwan a hannun shi ya shafama Rayyan a fuskar shi, sai da yayi hakan kusan sau biyar sannan Rayyan din yaja wani irin numfashi mai nauyi yana mikewa gabaki daya
"Bilal"
Ya kira daga lungun zuciyar shi yana kallon Abbu
"Abbu tafiya yayi... Bilal tafiya yayi"
Cike da rashin fahimta Abbu yake kallon Rayyan din, kafin ya maida duban shi kan Ayya da ta saka fuskarta cikin tafukan hannunta tana wani irin kuka marar sauti, bayani yake so wani yayi mishi yanda zai fahimta. Dube-dube Rayyan yayi yana dauko takardar da Bilal ya bar mishi da take can gefe ya mikawa Abbu, sai da ya karanta babu adadi kafin kalaman su zauna mishi. Baiyi magana ba ya mike tsaye, aljihun shi ya laluba yana zaro wayar shi da sabo ya saka shi daukarta ya zira bayan yayi alwala zai fita masallaci.
Jikin shi babu inda baya bari, dakyar ya iya saka lambobin sirri ya bude wayar. Sakkoni ya gani da hannun shi ya dangwalo batare da yayi niyya ba. Ganin sakon Bilal a sama ya saka shi saurin budewa:
"Kayi hakuri Abbu, ka yafe mun dan Allah, watakila zan samu sauki a duk inda rayuwa zata jefani. Ka yafe mun ban rike amanar da ka bani ba, ban kula da Layla yanda nai maka alkawari ba. Nagode da karbata da kayi, nagode da yanda ban taba jin maraici a karkashin kulawar ka ba. Ina fatan nisan da zanyi ya saukaka muku komai"
Sosai Abbu yake jin kan shi na sarawa
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Ya furta yana saka Rayyan saurin fadin
"Menene Abbu? Ya fada maka inda yaje?"
Ya karasa yana mika hannu ya karbi wayar da Abbu ya miko mishi, karanta sakon yakeyi wani abu na tattarowa yayi mishi tsaye a kirjin shi, dago idanuwa yayi yana kallon Abbu cike da wani yanayi
"Amana ka bashi Abbu? Me yasa?"
Saboda bai ga dalilin da zai sa Abbu yace ya bashi amanar Layla ba, sun san yanda Bilal yake, su dukan su kowa yasan raunin Bilal,yanda bashi da wani aiki sai kula da kowa, furta kalaman ba zaiyi komai ba sai dora ma Bilal din wani nauyi da Rayyan bayajin Abbu ya fahimta
"Abbu ko bakace ba, ko baka furta da bakin ka ba Bilal zai kula da ita da duka zuciyar shi, me yasa ka dora mishi nauyin nan? Kaga ya tafi, saboda yana tunanin ya kasa sauke nauyin amanar daka bashi ya tafi... Kasa ya barni"
Yanda Rayyan din yake magana kamar ba a cikin hayyacin shi yake ba, wanda zai dora ma alhakin tafiyar Bilal yake nema, bai sami kowa ba sai Abbu a yanzun. Dube-dube yakeyi ganin Abbu ya sadda kan shi kasa ya kasa cewa komai, har saida ya hango wayar Ayya sannan.
Idan Bilal ya turoma Abbu sako, tabbas itama yasan ya tura mata, watakila ya fada mata inda zashi ita. Yana dauka yaga ko password babu ita, dan haka kanshi tsaye wajen sakkoni ya shiga, ya kuwa ga Bilal din ya turo mata itama:
"Ki yafe mun Ayya, zanyi kewar ki da yawa"
Dariya Rayyan yayi da bata da alaka da nishadi, saboda ko shi zai fita duk yanda magana mai tsayi bata hadasu da Ayya, iya abinda zai tura mata kenan. Bai taba sanin Bilal bashi da hankali ba sai yau. Wayar ya ajiye gefe yana samu ya mike
"Ina zaka je?"
Abbu ya bukata, amman Rayyan din bai kula shi ba ya wuce. Tsintar kafafuwan shi yayi da bin Rayyan din, kafin shima ya tafi, jin takun Abbu a bayan shi ya saka shi juyawa
"Abbu ba inda zanje, ka koma dan Allah... Ba inda zani"
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.