Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Martabar_Mu_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 88 of 125
"Ka fito ga Baba nan"
Bai bashi damar amsawa ba ya sake ficewa, wani irin bugawa Rayyan yaji zuciyar shi nayi, tabbas zai saukema Bappa, saboda ba suyi haka da shi ba, sai ya tsinci kan shi da jin wani irin nauyi, saboda idan har Bappa na mishi kwarjini haka, baisan yanda baban shi zai kasance ba. Tunda yake bai taba sake kayan da suke jikin shi bai kara wanka ba, amman yau manyan kaya ya dauka ya saka, yana nemar hula ya dora a kan shi sannan ya fita. Aikam baiyi mamakin ganin kwarjinin da yake tattare da Sheikh Abdullah ba. A mutunce suka gaisa, Baba na dorawa da
"Bappa yamun bayanin komai, In shaa Allah babu abinda yafi karfin addu'a. Anjima da daddare sai kuzo ku karbi sako, akwai addu'o'in da zan baka kuma, saika daure ka dingayi kullum da safe muga abinda Allah zaiyi nan da kwana bakwai"
Kai Rayyan ya jinjina, sai da Baba yayi musu addu'a sannan ya mike, har bakin kofa suka raka shi, Rayyan ya dawo ya jira Bappa anan falon harya raka Baba waje ya dawo
"Baka da hankali ashe? Me yasa zaka saka Baba yazo?"
Murmushi Bappa yayi
"Ba zan iya daukarka ba, balle in sakaka a mota in kaika, shisa. Kuma karka damu Baba bashi da wata matsala bai dauki hakan komai ba"
Numfashi Rayyan ya sauke, shi ya dauki hakan wani abu, saboda Baba mutum ne Babba, ko bai girmi Abbu ba zasu zo sa'anni. Haka yayita jin wani iri har sanda suka je gidan da Baba ya sauka. Ruwan zam zam ne ya basu roba biyu, daya yace Rayyan din ya samu waje mai tsaf sai ya shafe duka jikin shi, kullum da dare har kwana bakwai, dayan kuma ya dinga zubawa a cikin kofi, ya saka garin habba, sai Ayat as shifa da zai karanta kullum. Sosai ya tsinci kan shi da yiwa Baba godiya, bai barsu sun tafi ba sai da suka ci abincin dare tare da shi, yanda yake ta musu hira na saka Rayyan jin wani iri.
Saboda shine karo na farko da ya zauna da wani babba suna cin abinci. Ko Yaya Ayuba basu taba yin wannan da shi ba, da suka koma gida ma ya kalli Bappa da nufin yi mishi godiyar da baisan ta inda zai fara ba katse shi yayi
"Karka cemun ka gode, get better, shine godiya da zakayi mun, nasan depression Rayyan, na san duhun da yake cikin shi. Kayi kokari dan Allah, sai muje asibiti daga baya kan kwayoyin nan, yanzun ka fito daga duhun da kake ciki"
Kai ya jinjina, ranar kuwa yayi amfani da duka ruwan zam-zam din biyu kamar yanda Baba yace tunda a hanya suka tsaya suka siyi garin Habba din me kyau. Baiji komai ba saida ya kwanta, kamar ana zare mishi rai haka ya dinga ji, jikin shi ya dauki zafi sai kace yana cikin gidan biredi. Zuwa karfe sha daya na dare ya fara galabaita da tuqar amai da take taso mishi, aman daya dinga kwarawa kamar zai fitar da kayan cikin shi. Haka suka kwana, Bappa yaki yin bacci saboda yanata fama da Rayyan suje asibiti amman yaki. Da safe kasa fita masallaci yayi, sai a gida suka tsaya Bappa yaja musu sallah. Har wajen tara yana jin gabaki daya jikin shi ko karfin kirki babu.
Da Bappa ya taba shi ture mishi hannu yayi
"Rayyan kaji jikin ka kuwa? Tsaf zan soya kwai akan goshin ka, ka tashi muje asibiti"
Banza yayi ya kyale shi, amman halin da yake ciki yasa Bappa ya kira Baba yana fada mishi
"Alhamdulillah, abinda nake tunani ne ya tabbata, ka barshi, aman shine saukin shi. Yaci gaba da sha, har Allah ya taimaka ya fitar da abinda yayi karfi a jikin shi"
Cike da tsoro Bappa yace
"Sihiri ne ko Baba?"
Murmushi kawai Baba yayi ta dayan bangaren
"Allah ya bashi lafiya. Allah ya kare mana imanin mu ya nisanta mu da dukkan abin ki"
Numfashi Bappa ya sauke, yana amsawa da
"Amin"
Kafin yayiwa Baba sallamar. Kwanakin da suka biyo bayan ranar ba masu sauki bane ba, dan duk yanda Rayyan din yaki saida Bappa ya kira likita cikin gida aka daura mishi karin ruwa. Kamar ana zuko wani abu a cikin jijiyoyin da suke jikin shi suna hade da zuciyar shi haka yake ji. Bai taba ciwo irin wannan ba, cikin kwanaki bakwai kamar bashi ba, duk ya fita hayyacin shi, wajen aiki ma randa yaje ca sukayi ya koma ya kara hutawa na sati daya sannan. Yayi wata irin ramewa. Baba sai da ya kara aiko mishi da wasu robobin biyu, yace karya daina sha saiya sha sau biyu yaga baiyi amai a cikin kwanakin ba tukunna.
Ba abinda ya dinga bama Rayyan mamaki sai baccin da yake kusan kwana ya wuni yanayi, saiya alakanta hakan da rashin karfin da bashi da shi. Amman a cikin sati na biyu ranar ya tashi da safe yaji shi kamar yana lilo saman iska, kan shi wasai, sai kace an kwashe wani datti daya jima yana taruwa a cikin kan nashi haka yake ji. Da sukayi waya da Layla dariya yaga yanayi, zuciyar shi na dokawa da wani bakon yanayi da bai taba sani ba, kwana wajen hudu yana tashi a tsorace, saboda gani yake kamar yanayin ba mai zama bane ba.
Sam baiwa Bappa gaddama ba sukaje asibiti, wasu magungunan aka dora shi a kai. Yana sha kuma, yana samun bacci, ashe haka baccin dare yake tattare da Rahma, duk da ba duka daren bane tunda ya samu sauki, amman zaiyi bacci wajen sha biyu har safe, sai yake jin shi duk wani sakayau. Ga Bappa baya barin shi ya zauna shi kadai, kullum suna yawon zaga gari, har gidan ball yake jan shi suje kallo, duk da yakan dawo da ciwon kai. Yanzun yake sanin halayen shi akwai wanda basu da alaka da komai, sam bayason mutane, wannan halin shine. Baba bai daina aiko mishi da robobin zam zam ba, a cewar Baba har yanzun yana bukatar su.
Saboda hutun rashin lafiya da suka bashi shisa basu zo Kano ba, sai yau, Bappa ya sauke shi ya wuce, yanata sauri shisa bai karaso da shi ba, yace zaiyi zuwa na musamman idan ya tashi. Da wata irin kewar Layla da Bilal din ya sauka garin Kano, da ita kuma ya shigo gidan har yake tsaye inda yake yana juya kasancewa waje daya da Abbu batare da yaji kamar iskar wajen tayi mishi kadan ba. Yana kuma jin zuciyar shi sakat
"Ka fada musu cikin jikin Layla ba naka bane ba"
Muryar Ayya ta katse mishi tunanin da yakeyi tana dawo da hankalin shi kanta cike da son fahimtar inda zancen ta ya dosa...
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Dec 26, 2020.
25
Maganganun Ayya ne suke mishi yawo, kafin ya zare hannun shi daga cikin nata, yana kallon Layla da jin an kira sunan shi ya sakata bude fuskarta, idanuwanta har sun kumbura saboda kukan da takeyi. Tana jin su, bata san kalar tunanin da ya kamata tayi ba, duniyar duka take ji ta hade mata waje daya. Ta rasa da wanne zata fara, tashin hankalin abinda yake faruwa da ita karon kanta, halin da su Mami suke ciki, Abbu da take ganin ba zuciyar shi kawai ta taba ba, harda Martabar shi, ko kuwa Rayyan da take ji suna lakabama laifin da ba nashi ba?
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.