Complete Hausa Novels

Abin Cikin Wai Complete Hausa Novel

Reading file: ABIN_CIKIN_WAI_COMPLETE_HAUSA_NOVEL.txt

Chapter 67 of 90

"Bilal ka yi haƙuri da maganar dazan faɗa maka akan matarka Jidda,kada ka ɗaga hankalinka abanza don idan ma ka ɗaga babu amfanin da zaiyi maka,jidda dai yarinyar Alhaji Damass ce ma'ana farkarsa". . ...tun kafin ya ƙarasa Bilal ya cukumo Captain ya ce"dont say anything captain,bana son in ƙara jin irin wannan maganar don Allah".yana faɗar hakan ya saki ƙwalar rigar captain ɗin,ya gyara wuyar rigarsa sannan ya ce"Bilal bakaji na ce ka yi haƙuri da maganar da zan faɗa maka ba?to nasan daman baza ka taɓa yarda ba,tunda ƴar gaban goshinka ce,amman kalli wannsn hoton da kyau ka faɗamin ƙarya na yi maka"?.

Da sauri Bilal ya kalli hoton,ya yi saurin ture kansa gefe yana hawaye,Jidda ce da Alhaji Damass suna shaye-shaye.kuma daga ganin hoton ba wai an É—auka bane don a haÉ—a,a'ah hoto ne na ainihi,Bilal ya fara ambaton sunan Allah da duk addu'ar da ta zo bakinsa.

Captain ya dafa kafaɗar aminin nasa ya ce"ka yi haƙuri Bilal nasan abin da zafi amman ka nutsu kasan inda zaka kama,ina faɗa maka sharri aka yiwa khairat amman ka ƙi yarda,kuma ka ƙi yin bincike ka tafi a haka,yanzu kaga ta yi maka babu wan babu ƙanin kaga yanzu sai kasan matakin da zaka ɗauka akan wannan muguwar matar ta ka".

Bai gama jin abinda captain zai faɗa masa ba fuu ya fita daga cikin motar captain ɗin,ya shiga tashi motar ya tayar da ita cikin fushi,Allah kaɗai yasan yadda ya ke jin zuciyarsa kamar zata fito waje,Jidda daya bawa ragamar sonta da ƙarfinsa amman yau itace zata yi masa haka?har yanzu shike kula da komai na iyayenta baya ga gidan daya danƙara musu,ashe ba haka kawai yaji ya tsani jidda yanzu ba,ashe ha'intarsa take da kuma cin amanarsa.

Ko da ya koma gida kai tsaye ɓangaren jidda ya yi,ya hau saman bane maimakon ya taka step ɗin ɗai ɗai to uku uku ya ke hawa saboda ya yi saurin hawa da wuri,ƙofar ɗakin ta arufe take alamar bata nan ya dawo farlo ya yi tagumi yana xaman jiranta,ai kuwa kamar haɗin baki sai gata ta shigo ko kallonta bai yi ba kansa na ƙasa yana tunanin mugun hali da rashin imani irin na jidda.

Ta shigo duk jikinta ya yi mugun yin sanyi ganinsa ya yi tagumi,kuma gashi ko amsa sallamarta ma baiyi ba,hankalinta ya tashi sosai ta É—an samu waje ta zauna ta ce"Love dafatan na sameka lafiya?daman. . . ."da sauri Bilal ya É—aga mata hannu,ya isa inda take tsaye ya buÉ—e wayarsa ya fara neman wani vedio,daman kuma kafin yabar wajen Ahmad É—in ya tura wannan vedion don kada ta yi masa musu.

Tun kafin ya buɗe vedion taji gabanta na tsananta faɗuwa sosai,ya buɗe vedion ya nuno mata fuskarsa babbar wayar tasa,da sauri ta dafe ƙirjinta tana fito da ido waje,dan danan sai ta fara haɗa gumi sosai kunsan mara gaskiya sai kuwa ta ce"wa. .wa. .wallahi ba ni bace sharri aka yimin".wani irin mugun mari ya wanka mata wanda sai daya tara mata taruwar jini a gefen idonta sannan ya nuna ta da yatsansa ya ce"ki ka yarda ki ka ƙara magana wallahi Jidda zan iya shaƙeki ki mutu kowa ya huta".ya nuna mata ɗan yatsansa alamar shittt.

Jikinta ne ya hau rawa sannan ya ce"Jidda ni dai babu abinda zance miki sai dai ince Allah ya isa na,kin rabani da matata sanyin idaniyata,kinyi mata sharrin zina,ashe kece babbar mazinaciya me cin amanar mutum abayan idonsa,yanzu zan nuna miki kalar muguntata jidda,zaki san ke baki iya komai na rashin imani ba,ni da nayi soja ai kinga baki isa ki nunamin kalar mugunta ba".ya faÉ—i hakan yana É—aukar wayarsa.ba'afi minti talatin ba sai ga sojoji sun kusan ishirin sun shigo gidan.

********

Hamza ɗaya daga cikin masu gadin gidanne,suna zaune da matarsa ya yi tagumi sosai,Hafsat matarsa ta tsaya da cin abincin da take ta ce"miji na lafiua kuwa naga duk hankalinka a tashe idanuwanka sunyi jawur kamar ma ka yi kuka"?.ɗan murmushi ya yi wanda ake ce masa yafi kuka ciwo ya ce"Hmm Hafsa ina cikin mummunar matsala wadda ban taɓa shiga makamanciyar irinta arayuwa ta ba.Hafsa ni ɗinnan da ki ke gani na yi wata mata sharrin an kamata da ƙwarto."

da sauri Hafsa ta miƙe ta rufe bakinta da tafin hannunta tuni hawaye suka fara zubo mata ta ce"Anya kuwa mijina Hamza ne agaba na?miji na me gaskiya da sanin ya kamata?anya kuwa kai ne"?.da sauri ya tashi ya riƙe hannayen Hafsa yana kuka ya bawa Hafsa labarin duk abinda ya ke faruwa.

Yana gama faɗa mata taja hannunsa tana tafiya cikin fushi yana tambayarta ina za suje amma ko kallo bai ishe taba ta shiga mota ta ce"ka taho mu tafi".babu yadda ya iya da Hafsa don yana matuƙar sonta sosai.

*********

Waje ya haɗu ga jidda,ga Bilal,ga khairat,ga hajiya kaka,ga masu gadin gidan Bilal sojoji,duk mutanen gidansu Bilal suna wajen,bayan sojojin sunzo wajen Bilal suka tafi gidansu Khairat ɗin,Baba Ƙasim ya ce suzo babban hall ɗinsu na gidan za'ayi meeting,to shine aka taru.

Khairat kanta na ƙasa,cikinta ya fito yanzu sosai kowa yana ganinsa,tuni Bilal ya ruɗe ganin cikin jikin khairat,yaji wani mugun sonta yana yawo acikin zuciyarsa,Allah sarki ashe harda guzurin ciki ajikin khairat ɗinsa,to tabbas aurensu bai ƙare ba,tunda ba'a sakin me ciki.

Baba Ƙasim ya ce"Bilal ka taramu anan wajen kuma bamu san me ya faru ba?ga matarka tana kuka ga kuma sojoji?Allah dai yasa lafiya ko"?.

babu abinda Bilal ya ɓoye musu na dangane da duk abinda ya faru har sharrin da aka yi wa Khairat.

Sosai kowa ya yi mamakin hakan aja shiga kallon kallo,Hajiya kaka ta nisa ta ce"oh yau ina ganin ikon Allah to meye kuka tsattsare ni da ido?gaskiya ce ai ta bayyana,anyi wa yarinya sharrin ƙazafin zina har sau biyu,yanzu gashi Allah ya wanke ta aguda ɗaya saura ɗaya".

Da sauri Maher ƙanina ya ce"a'ah kaka kin faɗi ba dai dai ba,guda ɗayan ma yanzu zai tonu don bazan yarda a gurɓatawa Yaya ta suna ba".yana faɗar hakan ya fito da wayarsa ya buɗe wani vedio,da sauri Hajiya Iklima ta miƙe tana rarraba idanuwa,Abbana ya kalleta da wani irin kallo.

Hajiya Iklima aka nuno ajikin wannan vedio ɗin ita da Anty kishirya ƙuru-ƙuru,Hajiya Iklima ta ce"hmm yanzu kinga mun gama da khairat harda uwarta saura wannan munafukar tsohuwar".

*MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_

3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
Badi'at Ibrahim
_Mrs Bukhari_

5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨
_Miss Hajo_

Guda biyar 1k
Guda huÉ—u N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda É—aya N300

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.