Abin Cikin Wai Complete Hausa Novel
Reading file: ABIN_CIKIN_WAI_COMPLETE_HAUSA_NOVEL.txt
Chapter 84 of 90
Ya faɗi hakan yana girgiza kansa,Bilal ya ce"captain ita rayuwar nan cike take da darasi sosai,duk wanda kuma ya yi me kyau zai ga me kyau,ni dai yanzu kaga Jidda ita ce ta yi sanadin rabani da khairat,rabuwa ta har abada wallahi captain zuciyata gab take da bugawa,ina ji ina gani khairat ta yi aurenta,ko kallon arziƙi bai haɗani da ita idan ta ganni ma captain yadda kasan taga wani dodo,Allah kamarin khairat har mamaki ya ke bani"
Ɗan murmushi captain ya yi sannan ya ce"Tabbas Bilal nima da kaina na yadda rayuwa cike take da ƙalubale,Bilal aƙwai wani laifi wanda ka yi wa khairat wanda aduk sanda ta ganka sai taji bata son ko haɗa ido da kai saboda girman laifin da ka yi mata.
Na farko shine ka zargeta da laifin da ba ita ce ta aikata sa ba,na biyu kuma shine rashin binciken da baka yiba alokacin da abin ya faru,wanda Darasin daya kamata ka fuskanta anan shine shi saurin fushi yana haifar da dana sani,don haka shiyasa ya ke da kyau duk abinda zamuyi mu dinga bincike kafin mu aikata,koma koda mutum yana cikin fushi bai kamats ace ya saki matarsa har saki uku ba,ai addini bai ce haka ba Bilal."
Idanuwan Bilal sunyi jawur ya juyo ya ce"Hmm captain baza ka gane abinda naji alokacin ba,duk abinda zan ƙwatanta maka dashi to tabbas ya wuce hakan,ina da matsanancin kishi sosai,musamman ma akan khairat,yarinyar da tun tana cikin mahaifiyarta na ke azabar sonta,amman dubi abinda khairat ta yimin yanzu".
Yana faÉ—ar hakan ya dafe sai tin zuciyarsa ya ce"captain ina jin wani abu acan cikin zuciyata yana yimin yawo,tabbas zuciyata saura kaÉ—an ta buga,captain ka kaini gida yanzu bazan iya zuwa ba".ya faÉ—i hakan yana dafe saitin zuciyarsa wanda ya kejinsa kamar zai fito waje,ga wani irin zafi da ya keji acan cikin zuciyar tashi.
Sosai Captain ya tsorata ya koma mazaunin Bilal ɗin ya tuƙa motar cikin gaggawa,asibiti ya kaisa don a halin daya ga Bilal bazai iya kaisa gida ba,shima captain ɗin hawaye ne ke fitowa daga cikin idanuwansa,yana riƙe da hannun Bilal ɗin guda ɗaya,Allah ne dai ya kawosu asibiti lafiya.
Likitocin suka amshesa suma duk hankalinsu a tashe don tuni har ya sume ma,aka shiga dashi emargency.Captain sai hawaye ya ke da sauri ya kira wayar Alhaji Abdullahi mahaifin Aliyu,ya sanar masa duk abinda ke faruwa shima hankalinsa ya tashi sosai,tuni ya sanarwa da Æ´an uwansa suka taho tare,amman ba'a gayawa Hajiya kaka ba,harma da mahaifiyar Bilal É—in bata sani ba.
Sosai hankalinsu ya tashi da jin abibda likita ya faÉ—a,cewar jininsa ya yi mugun hawa wanda idan ba'a basa abinda ya keso ba komai zai i'ya faruwa,sosai hankalinsu ya tashi to me Bilal É—in ya keso wanda ba'a yi masa É—in ba?suka zauna jigum jigum.Baba Usman ya ce"to yaya ko kasan abinda ke damunsa ne?wanda mu bamu sani ba?".
KaÉ—a kai Alhaji Abdullahi ya yi sannan ya ce"wallahi Usman ni kai na bazance maka ga abinda ke damun Bilal ba,amman ni dai naga yanzu idan ya dawo sai kaga duk ya rame,ko alokacin ma na tambayesa ko ba shida lafiya ne?amman sai ya ce min babu komai.kasan shi Bilal ba mutum ne me magana ba,ga miskilanci shiyasa ni ban gane konai ba".
Ko da suka ga rashin faÉ—an rashin lafiyar Bilal zai iya janyo wata matsalar sai suka yanke shawarar kawai gwara su faÉ—a agida,don haryanxu bai farka ba,wai numfashinsa ne bai koma normal ba.
Sosai gidan kowa ya ruɗe da rashin lafiyar Bilal,sai gasu sun cika asibiti kowa hankalinsa atashe Hajiya kaka sai kuka take tana ce wa"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un yanzu Bilal sai da ka saka wannan damuwar aranka?yanzu gashi nan har ta kaika ga ƙwanciya a asibiti"?.
Baba na ya ce"a'ah umma daman kinsan abinda ke damunsa"?.da sauri ta ce eh ƙwarai nasan abinda ke damunsa saboda ɗiyar wajenka khairat shiyasa duk hakan ta faru,to wallahi tallahi ka faɗawa ƴarka ta fitar min har jika na,tun kafin ranta ya yi masifar ɓaci".
Da sauri baba na ya ce"a'ah Umma kin kullemin kai baki ɗaya?don Allah ki faɗamin wata ɗiya ta ce"?.da sauri ta kallesa sannan ta wurga masa harara ta ce"ban sani ba khairat ƴar wajenka ita na ke nufi,rannan da ta zo da mijinta tana da ciki ya riƙe mata jaka,kamar akanta aka fara ciki shine taga ɗan wajenta Audu Irfan kenan shine ta-yi ta-yi yazo wajenta ya ƙi zuwa,to shine fa daya ƙi zuwa ta ce wai ubansu ne ya zugasa,shine yaje ya gayawa uban nasa yazo,wallahi yarinyar nan khairat babu ko kunyar ƴan uwantaka ta buɗe bakinta ta zagesa tsaf zagi na rashin mutunci.har da ce wa wai ta tsanesa tsana mafi muni.to sai me don ta tsanesa ai muma muna sonsa don haka taje ta ƙarata.tabar ganin mijinta na bani kuɗi to duk ta banzar don ni a'i jika na yafi min wannan farar fatar wacce ke ruɗar ƴarka".
Sosai abin ya yi wa kowa ciwo akan abinda khairat ta yi wa Bilal,Rashida taji nan da nan khairat ta sare mata akai,don ita tun kan yadda take zaginsu irfan ta fake da zaginsu alhali kuma Bilal É—in take zagi sai taji duk ta sare mata aranta.
Mamana da ke wajen ta sumkuyar da kanta don har zuciyarta ba taji daÉ—in abinda khairat É—in ta yi wa Bilal ba,don ko babu komai ai É—an uwanta ne uban Æ´aÆ´anta,da ya ke ranar da khairat É—in tazo ranar bikin Æ´ar gidan Baba Hamza ne kuma an tafi dinner shiyasa ba kowa ne ya san zancen ba,Sai Hajiya kaka uwar Æ´an kunne duk da ta tsufa tsam kunnenta na nan daram don ko gulmarta ka yi to babu abinda baza taji ba.
Babu wanda ya kirani ya ce Bilal bai da lafiya hatta mama na bata faÉ—amin ba,kullum dai idan na buga mata waya zance ta bani su Haidar muyi waya amman irfan sam bai ko kallon inda wayar take,idan ma aka ce masa mamansa ta bugo sai ya ce waishi ba mamansa ba ce.
Ranar dana ji hakan da kunnena ranar na yi kuka sosai,tambayar duniya Shahid ya tambayeni abinda ke faruwa na ce masa babu komai.haka dai ya sakani agaba har na samu naci abinci.sosai Shahid ke kula dani babu abinda na nema na rasa na rayuwa,ko tagumi idan shahid yaga na yi to hankalinsa yanzu zai tashi.
Ammi mahaifiyarsa yanzu ita ke yini a sashe na,saboda taga duk yanda na rame naƙi sakin jiki na kamar da,shima Shahid ɗin yanzu idan ya tafi aiki mai makon da baya dawowa sai maghrib amman yanzu la'asar na yi zai dawo.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.