Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 16 of 86

_Shiru kawai na yi domin har zucina natsuwar shi ta burge ni, sai dai a lokacin ba aure ne a gabana ba domin farkon shiga ta Jami'a kenan. Kuma ina da burin karatun shi ya sa ba na kula samari ko a Kebbi duk da takurar da suke yi mini. Don asali ma akwai wani da muke soyayya da shi sai dai Baba Ali bai yi na'am da shi ba. Hakan ya sa duk nacin da yake yi a kan ya turo Iyayen shi a tsayar da magana bai amince da hakan ba. Dalilin da ya sa na fuskanci karatun da kyau domin na samu abin da na je nema._

_Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce,_ "Ka yi haƙuri da abin da na yi, saboda ba na tsayawa magana a titi. Musamman irin Polo club da ta zamo mahaɗar kasuwanci da dandazon mutane..."
"Hakan ma ya tabbatar mini na yi zaɓen matar aure a inda ya dace. Amsar ki kawai nake buƙata yanzu domin ita ce abu ma fi muhimmanci a wurina".

_Shiru muka yi daga ni har shi ina wasa da gefen hijabina amma jikina a mace saboda daburcewar da na yi na rasa me zan ce. Ga kuma jikina ya ba ni idon shi duka a kaina suke, na yi jarumtar ɗagowa domin na saci kallon shi. Caraf muka haɗa idanuwa na yi saurin janye nawa ina masa kallon gefen ido, amma shi kafe ni ya yi da kallo ko ƙyaftawa ba ya yi. Na kawar da kaina gefe tare da rungume hannu a ƙirji na ce,_
"Ka ba ni lokaci zan sanar da kai idan na gama shawara".
Shiru ya yi na É—an lokaci sannan cikin sanyin murya ya ce, "Kamar zuwa yaushe za ki gama shawarar?"
"Sati É—aya"
Na ba shi amsa ina É—an murmushi, ya maraice murya yana faÉ—in "Kafin lokacin na zama gawa ai".

_Dariya ta suɓuce minu saboda sosai zancen shi ya ba ni dariya, domin yanayin da ya yi maganar yana karye wuya tamkar yaron da aka ƙwace wa alawa yana tsaka da jin zaƙinta._
"Kwana uku ai ya yi ko?"

"Kwana ɗaya tak zan iya juriya, ko shi zan kasance cikin wasiwasi da ƙididdigar lokaci. Don haka ki taimake ni ki sanar da ni yanzun nan ko don na fita fargabar da nake ciki..."
"Ka kwantar da hankalinka in Sha Allah alheri ne".

_Daga haka ya ci gaba da ja na da hira har duhun magrib ya kawo jiki. Sallama muka yi da shi bayan na ba shi lambar wayata, domin ya kira ya ji amsar shi gare ni._

***
_Abu kamar wasa soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanina da Mukhtar. Saboda ƙarfin da Umma take ƙara wa abin a ƙoƙarinta na son na yi aure Sokoto ko don na dawo kusa da ita. Amma Baba Ali bai karɓi abin kamar yadda Umma ta ɗauke shi da muhimmanci ba.
Familyn su Mukhtar sananne a cikin garin Sokoto, shi ya sa ba a sha wuya ba yayin binciken asalin shi, wane ne shi a idon mutane._

_An ɗauki lokaci muna soyayya da Mukhtar, kuma Baba Ali bai hana shi zuwa wurina ba kamar yadda ya yi mini iyaka da Jafar. Saboda ya nuna ƙarara ba zai ba shi ni ba, saboda asalin tushen shi Rundawa ne su. Kuma a cewar shi abin kunya ne da Allah-wadai ga Bafulatanin da ya haɗa zuri'ar shi da masu Fawa. Duk da wasu daga cikin 'yan'uwanmu sun tunatar da shi Allah bai haramta ba, amma ko kaɗan bai yi amanna da hakan ba. A ƙarshe ma fitowa ya yi a fili ya sanar shi ya yi mini miji ya yi haƙuri._
_Sosai na ji tausayin Jafar saboda na san kalar son da yake yi mini marar algus. Duk da a lokacin ni kaina zuciyata ta fi karkata da son Mukhtar fiye da shi. Dalilin hakan na tattara shi gabaɗaya na ajiye gefe, na bai wa Mukhtar matsayi mai girma a raina. Bayan lokacina da na sadaukar masa, amma ban bari ƙaunar da nake yi masa ta shafi karatuna ba. Kasancewar doka ce ta musamman Baba Ali ya gindaya mini, duba da yadda na yi nisan kiwon da ba na jin kira a kan soyayyar Mukhtar._

***
_Zancen aure na da Mukhtar ya kankama har an kawo sadakina. Domin ƙa'ida ce a wurin Baba Ali ba ya bari a yi wa 'ya'yan shi lefe, duk da yake ɗan boko kayan fitar biki kawai yake ɗora wa wanda zai auri 'yar shi. Saboda ba a kaina aka fara ba shi ya sa ban wani damu ba. Amma Ummata ta ji haushin hakan kasancewar ni kaɗai ce gare ta har lokacin. Duk da ta yi aure biyu bayan mutuwar Babana amma babu inda ta haifu._
_Mukhtar ya nuna mini jin haushin shi sosai dangane da soke lefen da Baba Ali ya yi. Domin ya sanar da ni har ya gama haɗa komai lokacin kawo mini kawai ya rage a saka, amma hakan ba zai hana shi ajiye mini ba idan na zo sai ya ba ni. Na yi farinciki sosai da maganar ta shi, kuma zuciyata ta ƙara tabbatar mini ƙololuwar ƙaunar da yake yi mini. Ummata ma ta ji daɗi a lokacin da ta ji labarin lefe na zai tarbe ni a gidan Mukhtar._

_Ba a yi bikin ba sai da na kammala digirina, amma tun a lokacin ya nuna mini ba zai bari na yi aiki ba. Kasancewar ina son shi ban kalli hakan a matsayin wani abu ba. Baba Ali ma da ya yi masa zancen aikin ni na ba shi shawarar ya ce masa ya amince. Saboda gudun matsala ta biyo baya ga shi a lokacin ba zan iya juriyar rashin shi ba. Kuma hakan ta kasance a lokacin da ya kira shi takanas domin su yi magana a kan aikin nawa. Baba Ali ya ji daɗin hakan kuma ya ƙara nuna farincikin shi a kan halin yakamatan da ya hango ga Mukhtar._

_Sadaki sai kayan fitar biki kala biyar Mukhtar ya gabatar a yayin neman aurena. Aka yi bikinmu cikin mutunta juna aka kai ni gidan su Mukhtar da ke unguwar Sokoto Silma. 'Yan'uwan shi da abokan arziƙi duk wanda ya gan ni sai ya ce ma sha Allah, saboda kyakkyawar halittar da Allah ya mallaka mini. Kasancewa ta farar bafulatana mai dirarren jiki da yalwar faffaɗan ƙugu ga cikar ƙirji._

***
_Daren ranar babu komai da ya shiga tsakanina da shi, kasancewar wasu daga cikin ƙawayena da danginmu na Kebbi a nan suka kwana. Sai ta ta biyu ya karɓi budurcina ba tare da na san me ya faru a lokacin ba. Domin har yanzu da nake bayar da labari ba zan iya kawo me ya faru a darena na farko da Mukhtar ba. Da asuba na farka na tsinci kaina cikin sabon sauyi, tuna abin da ya faru ni da ni kafin ya shiga jikina. Ya sa na rufe fuskata cike da jin kunyar kaina a cikin idanuwana. Na miƙe ban gan shi a ɗakin ba na yi toilet ɗinmu da ke cikin ɗakin, tsarkake jikina na yi sannan na yi wankan tsarki na fito. Sallaya na shimfiɗa na yi sallah na yi addu'o'in zaman lafiya ni da angona Mukhtar. Sannan na yi karatun Qur'ani da na gama na yi azkar ɗina kamar yadda na saba. Domin gidan Baba Ali ba a wasa da sallah sosai ake riƙo da addinin Islama. Mun samu ilimin muhammadiyya daidai gwargwado, mun yi saukar Qur'ani kuma mun haddace littafai da dama._

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.