Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 71 of 86

****

Daren ranar bacci rabi da rabi na yi, saboda na yi ta kiran wayar Sajida domin na ji halin da take ciki. Amma duk kiran da na yi babu wanda na samu wayar kashe ake cewa.
Jiki babu kuzari muka shirya ni da yara kamar koyaushe, Najib ya kwashe mu ya ajiye su ni ma ya kai ni wurin aiki.
Ban yi wani aikin kirki ba ranar saboda ban da natsuwar zuciya, a ƙarshe ma tattara komai na yi na tura drowar teburina. Saboda ƙwaƙwalwata ta toshe ba na gane komai face tunanin Sajida da Maman Taufiƙ. Sai tashin hankalin da zai biyo baya ita da Amininta idan ta ji labarin yankan bayan da ya yi mata.

Misalin ƙarfe ɗaya da rabi kiran Najib ya shigo wayata, duk da ban san me zai faɗa mini ba; sai da gabana ya buga da ƙarfi kafin na ɗaga wayar numfashina yana sama da ƙasa.
"Maman Haidar, na je makaranta tun ƙarfe ɗaya ban ga su Ummu Salma ba, gabana aka watse makarantar amma ban ga sun fito ba. Har maigadin na tambaya ya ce da ni wani ya zo ya ɗauke su da mashin. Na je Bafarawa Estate a can ma an ce ba su koma gidan ba."
Dam-dam-dum! Shi ne sautin luguden da zuciyata ke yi tamkar ta fasa ƙirjina ta fito. Ban san lokacin da na zabura na miƙe tsaye ina ta maimaita faɗin, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un!" A bakina ba.

Waya a kunnena na fito da gudu na yi bakin gate, ban ma san ya katse kiran ba har sai da wani kiran ya sake shigowa.
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un! Wayyo Aunty wuta! Ki zo ki cece ni wuta! La'i'laha illallah Muhammadur Rasulullah! Shi kenan!!!! ÆŠakin duka ya kama da wu..."

Muryar Sajida kenan da na ji a cikin waya, da wata sabuwar lambar da ban san ta ba, kafin kiran ya katse. A gigice, na durfafi saman titi idona a rufe ba na gane komai da kowa a lokacin, balle na hango abin da ke gabana. Odar mota na ji 'Ɗiiiiiiiiiiiiiii!' A cikin kunnuwana tamkar za a fasa mini dodon kunne. Cak! Na tsaya sai jin na yi an ture ni na faɗi gefen titin, daga ni har wayar mun ɗaiɗaya. Yunƙurin miƙewa na fara yi na ji an riƙa ni da hannu biyu na tashi, sai sannu ake jera mini ba tare da na shaida muryoyin mutanen ba sai ta mutum ɗaya waton MD.
Ruɗu da firgici ya sa na zama tamkar wata zararriya ina faɗin, "Yarana sun ɓata! Wuta ta canye Sajida! Don Allah ku taimaka mini zan mutu idan na rasa yarana da Sajida. Zan mutu idan na rasa yarana su ne rayuwata."

Hannuna na ji an ja ban tirje ba na bi, aka saka ni cikin mota sannan aka rufe. Fisgar motar aka yi da ƙarfi idona a rufe ina ta zunduma ihu, tare da kiran sunan Sajida da yarana tamkar wata mahaukaciya sabon kamu.

Hmmmmm! Laifin daɗi ƙarewa. A nan muka kawo ƙarshen ABOKIN AIKINA littafi na ɗaya. Idan Allah ya ara mana lokaci an yi sallah lafiya za mu ɗora da wani sabon salon kafcen. A cikin littafi na biyu mai tsayawa a zuciya. Ubangiji ya albarkace mu da ganin wannan wata mai tarin falala waton Ramadan.

Fatan alheri gare ku gabaɗaya luv u all😘

D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

*AM BACK MY FANS.*

*ARBA'IN DA ÆŠAYA.*

'Ƙiiiii' Shi ne kalar birkin da MD ya ja, a daidai ƙofar gidan Kawu Sale. Saboda hanzarin fisgo ni da ya yi na faɗa jikinsa a haukace babu shiri, a dalilin bai gama tsayuwa ba na nemi ɓalle murfin motar na fice.
Kallon-kallo muka dinga yi wa juna, kafin na yunƙura kamar wata zakanya, na fisge daga riƙon da ya yi mini na fice motar aguje ina ƙwala wa su Umma kira. Gidan na faɗa a sukwane tare da faɗin,

"Umma! Umma ki zo an sace su Haidar! Wayyo Zuciyata za ta buga!"

A tsakiyar gidan na zube ina gunjin kuka cikin sauti tare da É—aga murya. Inna Kulu da Umma har rige-rigen isowa wurina suke yi tare da jero mini tambayoyi. Ban bi ta kan tambayoyinsu ba, illa ihun kiran sunayen yarana da nake yi tare da Sajida a haukace.
Ruwa na ji Umma ta watsa mini a jiki da ƙarfi, na zabura ina ƙoƙarin ficewa gidan tamkar wata zautacciya. Inna Kulu ta damƙe ni Umma ta fara girgiza ni tare da faɗin,
"Ki dawo! Hankalinki! Na ce!"

Tsawar da ta yi mini sosai ta shiga jikina, cikin sauri na faɗa jikinta ina kuka na ce, "Haidar, Ummu Salma da Iman duka sun ɓace! Ita ma Sajida wuta ta ƙone..."

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un! Me ke shirin faruwa da mu ne haka?"

Zancen Inna Kulu kenan, kafin Umma ta ja hannuna mu fito gidan, motar MD na hango a inda na bar ta. Hakan ya sa na tuna ashe shi ne ya kawo ni gidan, har mun yi gaba ya biyo mu yana gayar da Umma. Fuskarta a haɗe ta amsa masa sannan ta ƙara jan hannuna muka yi gaba.
Biyo mu ya yi da motar yana roƙon Umma ta shigo ya kai mu inda za mu je, amma haƙuri kawai ta ba shi sannan ta tare mana wata adaidaita muka shige. Tafiya adaidaitar take yi ina sharɓar kukana mai ɗauke gunji kala-kala.

'Wuuuuuuummmmmh!! Ummmmmm!'

High Court Juduciary na ga an rubuta, a jikin bangon allon saman bakin babbar kotun da ke Sokoto.

"Kotu kuma? Me ya kawo mu kotu?"

Tambayar da na yi kenan bakina yana rawa. Yanayin da nake ciki bai hana ni kai kallona a kan fuskar Umma ba. Wadda ta É—auke kanta kamar ba ta fahimci halin da nake ciki ba.
Kuɗi kawai ta ciro a jaka tana miƙa wa mai adaidaitansahun, na fito ina faman wara ido. Saboda ganin tsarin kotun da girman ta ya sa zuciyata ta hau bugawa, 'Ɓal-ɓal!' da sauri da sauri.
Duk da ba ranar ne karon farko da na taɓa ganin ta ba, amma wannan karon ya sha banbam da na saura. Saboda iyakaci na bi ta gaban gate ɗin kotun na wuce idan an biyo da ni ta Sama road, ko kuma idan na hau titin Hause of Assembly da ke gidan Gwamnatin Sokoto.

Umma tana gaba ina bin ta a baya har harabar kotun, bayan mun gaisa da masu gadin wurin sun yi mana wasu 'yan tambayoyi Umma ta amsa musu a taƙaice.
Kai-tsaye aka yi mana jagora har ofishin wani mutumi mai harÉ—aÉ—É—iyar fuska. Zama muka yi daga ni har Umma a kan kujerun da ke ofishin. Sai da ya gama rubuce-rubucen shi a jikin wani file sannan ya cire gilashi ya fuskance mu.

"Me ke tafe da ku?"

"Mijin 'yata na kawo ƙara!"

Zancen Umma kenan kanta tsaye ba tare da shayi ko rawar murya ba.
"A kan me kika zo?"
Mutumin ya sake jefo mata wata tambaya, sai da ta gyara zamanta sannan ta ce,
"Ina so ya sakar mini yarinyata, kuma ya ba ta yaranta da ya sace a makaranta."

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.