Abokin Aikina Complete Hausa Novel
Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 75 of 86
"Aunty kin ga yadda na koma ko?"
"Daina kuka, karɓi maganinki ki sha. In sha Allah za ki ji sauƙi kwanan nan ki dawo yadda kike."
Da kaina na karɓi maganin na ba ta, ganin ta ƙi barin kukan, matar tana murmushi ta ce da ni,
"Kanwar nan naki, tana son ki sosai. Tun jiya take zancen ba ki zo ba, ta damu ta gan ki da yawa."
"Allah Sarki! To ga ni na zo. Me kike so na je na kawo miki?"
"Babu komai Aunty! Daman magana ce nake son mu yi ni da ke..."
"Babu wata magana da za ki sake yi da ita! Baƙar natau mai baƙin nacin tsiya. Macen da ta haɗa kai da ƙawarta suka nemi salwantar miki da rayuwa kike wani rawar jiki a kanta. To wallahi in dai ni ce na haife ki, na raba ki da wannan azzalumar matar, kilibabba, mai fuskar munafukan farko. Allah ya isa tsakaninmu da ke Zaituna, daga ke har Uwarki da ba ta san darajar surukuntaka ba. Wai har ita za ta saka hannu ta daki Mukhtar a gaban kuliya, kuma don an mayar da shi banza a ɗauki yara a miƙa miki. To wallahi ko giwa ta faɗi ta fi ƙarfin karnukan farauta ire-irenku azzalumai, ya ku haram, ya ku halas!"
Sakato na yi ina kallonta tamkar wata doluwa, saboda gaskiya ta sa ban san me zan faɗa wanda zai zo daidai da lafuzzanta ba. Jakata kawai na saɓa a kafaɗa ina murmushin yaƙe na ce da Sajida.
"Ni zan tafi! Ubangiji Allah ya ba ki lafiya."
"Idan ke kike da lafiyar ki hana ta."
Zancen da ta raka ni da shi kenan, har na yi gaba na dawo baya saboda ina so na san halin da Aminu yake ciki.
"Amm! Jikin Aminu fa? Shi ma da sauƙi ko?"
Sajida tana goge hawaye a kan fuskarta da ta sha baƙi tamkar an yi mata fentin gawayi ta ce,
"Yana ɓangaren maza, ya ƙone da yawa ba kamar ni ba."
"Ya Salam!"
Ita ce kalmar da na iya furtawa, ina ƙoƙarin juyawa idona a rufe na ci karo da mutum. Babu zato na ji saukar mari a kan fuskata,
'Tau!!!'
Gabaɗaya kallon mutane ya dawo kanmu. Daga ni har wanda ya yi gangancin saka kuturun hannunsa ya mare ni. Dafe da gefen da na sha marin nake kallon shi tamkar a ranar na taɓa ganin shi a rayuwata. Zuciyata cike da tunanin abin da zan yi na rama tozarcin da ya yi mini a cikin mutane.
Hannuna na ware iya ƙarfina na sauke masa nawa marin, sannan na duƙa a lokacin da zai dawo mini da wani marin, na kai wa jarumarsa kutuball da ƙafa.
Sai ga shi ƙasa dafe da gaban shi yana ihun na kashe shi, mutane suka yo kansa aka rirriƙe shi. Yayin da ni ma wasu mata suka fitar da ni cikin ɗakin ina ƙoƙarin tirjewa. A kan babu inda zan je sai na ga ƙarshen rashin mutuncin da yake taƙama da shi.
Muryar Yaya Maimuna na tsinkayo tana aiko mini zagi, tare da boren da take yi wa mutane a sake ta sai ta kashe ni.
Da ƙyar wannan ma'aikaciyar ta shawo kaina na amince zan tafi. Saboda na kafe a kan babu inda zan je sai Yaya Maimuna ta zo ta kashe ni, kamar yadda take ta ihun faɗa ana tausar ta.
Matar ta raka ni har compaund É—in Asibitin inda ake ajiye motoci, sannan ta fara sauke numfashi tana faÉ—in,
"Na fa'imci kuna da masala a sakaninku. Saboda tun jiya ita yarinyar nata take ta zancenki ita kuma tana ta zagin ta. Dun Allah kada ki daina kula ta wallahi tana kaunar ki da yawa. Mamar ce kawai ke da masala amma ita ma za ta daina ne ki yi akuri."
Zaman jakata kawai na gyara tare da ɗaga mata hannu na fice Asibitin zuciyata tana ƙuna. Saboda zagin da Yaya Maimuna ta yi wa Ummata na shanye albarkacin Sajida ban rama ba. Da kuma takaicin marin lusarin maza, namijin ho-ti-hon da ya yi wa mazan duniya rakiya a tsugunne.
Shin wane ne wannan? ðŸ¤â€Ã°Å¸Â¥Â² Yaya Maimuna dai ta hana mu ji maganar da Sajida take son faÉ—a wa ZaitunaðŸ™Â😟
D. AUTA CEâœÂðŸÂ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*AM BACK MY FANS.*
*ARBA'IN DA UKU.*
Ban iya zuwa wurin aiki a lokacin, sai gida na koma saboda babu kuɗi a jakata. Kuma ban ce da Najib ya jira ni ba sannan ba na so na kira shi, gudun na katse masa uzurin da yake yi. A ƙafa na yi tattaki tun daga cikin asibitin har zuwa har bakin gate, dalla-dallan motocin alfarma suna ta shiga da fice a cikin Asibtin tamkar ana gasar gwadin ranttsun motocin da suka ji gishiri.
Idan na ga mace da mijinta cikin mota suna hira ko dariya sai na ji sun burge ni. Saboda rabon da na yi hirar arziƙi da Mukhtar mu yi raha da dariya har na manta. Kullum faɗa masifa ne yake haɗa ni da shi mu yi doguwar magana, ba ya shawara da ni, ban san komai a kansa ba duniya, idan ba shi da nake gani da ido ba.
Shigarsa fitarsa duka bai damu da sanar da ni ba, domin wani lokaci ba na sanin ya shigo gida kuma ba na sanin fitarsa. Matuƙar ba ina tsakar gida ko falo ba, wanda babu yadda za mu yi dole mu ga juna ko ba ma so.
Da tunanin na shiga gidan Kawu Sale, na karɓi kuɗin mai adaidaitasahu na kai masa sannan na dawo. Tun kafin na zauna Inna Kulu da Ummata suka fara jefo mini tambayoyin.
"Lafiya kika dawo yanzu?... Ko yau ba a aikin ne?"
Wuri na samu a kan kujerar tsugunno na yi tagumi, sannan na sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi na ce da su.
"Asibiti na fito ban je wurin aikin ba."
"Ya jikin Sajidar? Allah dai ya sa lafiya?"
Tambayar Inna Kulu kenan, na amsa mata cikin yaƙe na ce,
"Ita kam da sauƙi, amma mijin nata ne aka ce ya ƙone da yawa. Na so zuwa duba shi na manta shaf sai bayan na fito asibitin na tuna."
"To Allah ya ba su lafiya duka, kuma ya ƙara tsare gaba."
"Amin" na ce, sannan na ciro wayata na fara neman lambar Maman TaufiÆ™, duk da cikakken sanin da nake da shi a kan da wuya na same ta. Haka na yi ta jera mata kira kamar wadda aka saka dole, saboda duk kiran da na yi sai an sanar da ni a kashe wayar take.
"Wai wa kike kira?"
Umma ta jefo mini tambaya tana sheƙa ruwan sanyi, a cikin kunun zaƙin da take ƙoƙarin haɗawa.
"Lambar Maman TaufiÆ™ ce nake gwadawa ko za a dace ta shiga."
"Ke ma dai kin fiye saka abu a ranki wallahi, ki bar ta kawai, daman gyaÉ—a idan ta ji zafi ita ke fitar da mai da kanta ba sai an matsa ba."
"Wallahi Umma ban ji daɗin abin da ta aikata ba, don na san ita ma abin zai dame ta muddin hankalinta ya dawo jikinta." Na ƙare maganar cikin sanyin jiki da na murya, Inna Kulu da ke wanke shinkafa a bakin makwarara ta ce,
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.