Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 74 of 86

"Ki yi shiru Zaituna! Kada ki bari damuwa ta saka ki yin saɓo ba tare da kin sani ba. Ki yi imani da cewa Allah yana son ki kuma yana sane da duk wani halin da kike ciki. Sannan ki ƙara yi masa godiya a kan tarin ni'imomin da ya mallaka miki. Ke musulma ce kuma mumina mai kishin addini da ibada daidai gwargwado. Sannan kina da cikakkiyar lafiya kuma kina da halitta mai kyau, irin wadda ba kowa yake samu ba. Ya arzuta ki da 'ya'ya har guda uku reras, wanɗanda wasu suna can suna nema ido rufe amma ba su samu ba. Mahaifiyarki tana raye kuma koyaushe tana tausaya miki, tana saka miki albarka babu dare babu rana. A duk wani motsinta sunanki ne a bakinta, bayan addu'o'in da kuɗin duniya ba za su iya mallaka miki rabin abin da take roƙar miki ba. Shin ko iya hakan bai sa ki gano Allah ya fifita ki da miliyan ba? Saboda yana son ki kuma yana tare da duk wani mai haƙuri a ko'ina ya jefa ƙafarsa. To ki bar wa Allah ragamarki, domin ya ja ki ya kai ki inda ƙwaƙwalwarki ba ta taɓa tunanin kai wa ba."

Sosai maganganun Inna Kulu sun ratsa jikina, haka ma sun saka ni jin wani sanyi ya tsirga mini a cikin zuciya. Tsoron Allah da tsantsar imani da tawakkali a kan komai ya zauna mini daram a cikin raina. Ajiyar zuciya na shiga saukewa wata bayan wata kafin na fara shesshekar kukan da na ci lokaci bayan lokaci.

"FaÉ—a mini, me kika gani a cikin wayar wanda ya tayar miki da hankali har haka da yawa?"

Majinar kuka na zuƙe tamkar ƙaramar yarinya, sannan na ce da ita, "Maman Taufiƙ ce ta saka wa Sajida da mijinta wuta. Sannan ta ce ba za a sake jin ɗuriyarta ba a faɗin duniya, kada a neme ta don wani idon sani ba zai taɓa ganin ta ba."

"Subhanallah! Wai me mata suka ɗauki kishi ne? Yanzu irin wannan aika-aikar da ta aikata; kuma ta tsallake ta tsere. Shin a tunaninta don ta yi hakan zai dawo mata da farincikin da ta rasa? Ko kuma zai iya canza wa ƙadddararta suna ne ta dawo kanar ba a yi ba? Kai jama'a! Duniya ina za ki da mu? A kan kishi ka nemi halaka wasu ka halaka kanka a banza!"

Ɗakin ya ɗauki shiru na tsawon lokaci babu wanda ya yi dogon motsi. Umma ta tashi zaune tana ƙare mana kallo ɗaya bayan ɗaya sannan ta tsayar da kallon ta a kaina ta ce,

"Ina Mukhtar É—in? Ya ba ki takardarki?"

Murmushin yaƙe kawai na yi mata, sannan na saka hannu na goge ruwan hawayen da ke gangaro mini a kan fuska.
"Ba na son kukan nan! FaÉ—a mini ya ba ki takardar sakinki ko a'a?"

Abin da ta faɗa kenan fuskarta a haɗe bayan ta ƙure manejin kallonta a kaina. Idonta a kan fuskata na ce,
"Bai ba ni ba! Amma dai zai ba ni idan muka koma."
Zumbur ta miƙe tana zarar ido, na yi hanzarin tashi tsaye na riƙe ta, cikin sigar rarrashi na ce da ita,
"Ki yi haƙuri Umma! In sha Allah komai ya zo ƙarshe a tsakanina da shi. Don kafin mu baro kotun sai da Alƙalin ya sanar da ni; idan muka dawo za a saka shi a sauwaƙe mini ko da ba ya so."

"Yaushe za a koma?" Tambayar da ta yi mini kenana har lokacin idonta a kaina.
"Bayan kwana biyu ya ce mu koma."

Sannan ta koma ta zauna dafe da kanta, wanda alamunta ya nuna mini ciwo yake yi mata. Duba da yadda take yamutsa fuska tana girgiza kan nata idonta a rufe.
Ficewa na yi daga ɗakin jikina babu kuzari, saboda magriba ta gabato amma ko sallar Zuhur ban yi ba balle Asr. Ban bi ta kan yarana da na hango ɗakin Inna Kulu ba, arwala kawai na ɗora na koma na shimfiɗa carpet na fara sallah. Raka'ar ƙarshe ta sallar Asr aka fara kiran magrib. Hattama su na yi duka sannan na buɗe hannuna sama ina roƙon sauƙi da sassauci a wurin Ubangiji.
Na jima a kan sallayar har aka kira Isha ban tashi ba, sannan na ajiye carbin da ke hannuna na gabatar da ita.
Zama na yi ina ta zuba addu'o'i'n da ba zan iya kawo su duka a kaina ba. Saboda tunanin Maman Taufiƙ da inda za ta shiga a faɗin duniya idan ta bar gidan mijinta, kuma ta ƙi komawa gidansu ko wurin wasu 'yan'uwanta.
Inna Kulu ta kawo mini tuwo kuma ta matsa sai da na tsakura. Ina zaune a wurin su Aunty Asabe suka zo yi mini sallama za su tafi gidajensu. Sai da safe muka yi suka tafi suna mini addu'ar samun sauyi a cikin rayuwata.

****
Daren ranar daga ni har Umma kwana rabi da rabi muka yi, saboda duk na motsa sai na ji ta ce, "Lafiya?" Na ce da ita babu komai sannan na gyara kwanciyata.
Da safe bayan mun karya ni da yaran, Umma ta ce su yi zaman su kada su je makaranta. Na ce da ita ta bari su je in sha Allah babu abin da zai faru.
Tare da su muka fito Najib ya ajiye su bakin makarantar. Na fita da kaina muka gaisa da maigadinsu na ce da shi,
"Don Allah Baba kada a bari wani ya sake zuwa ya É—auke su, idan ba wannan da ya saba zuwa É—aukar su ba kullum."

"Kada ki damu Hajiya. In sha Allah hakan ba za ta sake faruwa ba. Wannan karon ma don ban san yadda tsarin naku yake ba."

Ɗari biyun da Umma ta ba ni na fito da ita a jaka na miƙa masa. Ya karɓa yana ta godiya muka juya. Shiru ya ratsa tsakani bayan barin mu wurin Najib ya ce da ni,

"Don Allah ki yi haƙuri Maman Haidar, ban ji daɗin abin da ya faru ba."

"Kada ka damu! Ai ba laifinka ba ne. Kawai dai ka yi ƙoƙarin zuwa da an tashi ka ɗauke su."

Daga haka na ja bakina na tsuke, bayan na ce da shi ya kai ni Asibitin Uduth. Kaina tsaye na doshi ɓangaren masu wuta, saboda babu inda ban sani ba a cikin asibitin. Domin awo da wasu ciwukanmu ni da yara duka a nan muke zuwa.
Tun da na tunkari doguwar barandar ƙirjina yake bugawa, na ciro wayata na kira layin da Sajida ta kira ni da shi jiya. Wanda ta sanar da ni wutar ba ta ƙone ta ba, kira ɗaya biyu aka ɗauka.

"Hello!"

"Don Allah Sajida nake nema, wadda ta kira ni da wannan layin."

"Sajida!?"

"E, wadda ta ƙone da wuta."

"Ok! Ke ce Auntynta kenan? To karaso ina dakin nasu yanzu na zo ba su magani."

Maganarta cikin rashin cikakkiyar Hausa ya sa na gano yare ce ita, kuma ga dukkan alama matar ma'aikaciyar asibitin ce.
Da kuzarina na shiga dogon É—akin, ina ta faman gayar da marasa lafiyar da ke kwance suna jin jiki, gwanin ban tausayi.
Na wuce ɗakin na faɗa wani sannan na hango Sajida a kan wani gadon da ke ƙarshen ɗakin. Wani sanyin daɗi ya shige ni saboda gani ɗaya da na yi mata na hango sauƙi. Duk da jikinta da fuskarta duka sun yi baƙi tamkar gawayi, da sauri na isa bakin gadon murmushi a kan fuskata ina jera mata sannu.
Gani na ya sa ta ƙi karɓar maganin da ma'aikaciyar jinyar ke miƙa mata, ta fashe da kuka tana faɗin,

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.