Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 69 of 86

Kashe wayar kawai na yi ina Safa da Marwa a cikin ɗakin rungume da hannuna a ƙirji. Wayar na fara bubbugawa a bakina sannan na ce da Ummata,
"Don Allah Umma ki kai Sajida gidansu ki damƙa wa Mamarta ita hannu da hannu, gudun ta ƙi komawa gidan a ce mu ne muka ba ta ƙofar guduwa."

"Me ya faru?"

Tambayar da Inna Kulu ta yi mini kenan a ruÉ—e, zama na yi a bakin gadon Umma sannan na ce da su.
"Yaya Maimuna tana yunƙurin tsine wa Sajida muddin ba ta koma gida yanzu ba. Don haka yana da kyau a mayar da ita gudun ta tsine mata a kan banza."

"Lalle kin yi magana mai ma'ana. To bari na watsa ruwa sai mu tafi. Amma ba zan iya shiga gidan ba gudun wata matsala ta biyo bayan hakan."
"Inna Kulu ku tafi tare don Allah! Ke ki shiga da ita har gidan ki miƙa wa Mamarta ita ki fito ko ba ki ce komai ba."

Zancen da na yi kenan cikin sanyin jiki saboda na kai maƙurar ɓacin rai da damuwa. Ban iya cewa Sajida komai ba har Umma ta shirya. Inna Kulu ta shigo ta riƙa hannunta suka fita ɗakin, Umma ma ta fita jiki babu kuzari na bi su baya har ƙofar gida. I ta faman share hawayen da ke ta fareti a kan dandamalin fuskata.

Babu zato sai ga wata adaidaitasahu ta tsaya a ƙofar gidan, Maman Taufiƙ na ga ta fito tana biyan mai adaidaitasahun kuɗinsa. Sajida ta ƙwace daga riƙon da Inna Kulu ta yi mata ta zunduma ihu iya ƙarfinta.
Ni ma ganin ta a lokacin da ban yi tsammani ba; sai da na ji cikina ya murɗa hanjina sun dunƙule wuri ɗaya. Da gudu na koma gidan na faɗa bayi, zawo na dinga kwararawa tamkar zallar ruwa ne kawai nake fesowa shaaaa!

Wayyo🥲

D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

*Commenters, masu share, 'yan Allah ya ƙara basira, da masu danno mini sticker's da emoji idan na yi posting, har ma da wanda karatu ne kawai na shi ba ya motsi. Dukanku Allah ya saka muku da mafificin alherinsa. Ina son ku gabaɗaya, kuma ina yi maku fatar rayuwa mai kyau tare da gamawa duniya lafiya.👏🏻*

*LAMBA ARBA'IN.*

Jiki babu kuzari na fito daga bayin, ƙirjina yana dakan luguden uku-uku. Takalman Maman Taufiƙ na hango a ƙofar ɗakin Umma, hakan ya tabbatar mini da har ta shigo gidan, su sun tafi.
Haka kawai na tsinci zuciyata wasai, fargabar da nake ciki fiye da rabinta ya zumame. Daidaita natsuwata na yi sannan na shiga ɗakin, fuskata ɗauke da murmushin yaƙe na fara faɗin,
"Sannu matar mijinta, shi ne za a zo mini babu sanarwa?" Na ƙare maganar tare da zama kusa da ita ina ƙoƙarin karantar yanayinta.
"Ke ce da sannu Maman Haidar! Saboda ke kika yi abin da dole sai na zo ba tare da kin sani ba. Kin ci sa'a ma da ban yi tsuntsuwa na dire saman kanki ba, domin na yi ta tsige miki gashin kai har sai kin gama tattara komatsanki mun juya tare."
Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi, tamkar an sauke mini ƙaton dutsen da ya danne mini zuciya. Saboda lafuzzanta sun tabbatar mini har yanzu ba ta san wainar da ake toyawa ba.

"Idan ma kin tsige gashin, ke za ki tsinto shi ki dawo ki mayar da shi inda kika gan shi."

Na ƙare maganar ina 'yar dariya, Maman Taufiƙ ta gyara zamanta sannan ta ce da ni,
"Wallahi ko kaɗan ban ji daɗin abin da ya faru ba, abin haushin ma ban san da rikicin ba kwata-kwata sai yau. Saboda kwana biyun nan duka wani masifaffen bacci nake yi tamkar wata 'yar maye. Sai yau da safe Amini yake sanar da ni wai ba kya gidan, ashe shi ma sun zo biko gidan nan Umma ta hana su ke? To ni dai don Allah kada ki ba ni kunya. Don na gama cika baki a kan zan shawo kanki, na rarrashi Umma ta yi haƙuri ki dawo gidanki ko don yaranki."

"To ki furzar da abin da kika cika bakin da shi Hajiyata! Don ni kam sai dai idan gawata za a sake kaiwa gidan Mukhtar. Daman can zaman Umma nake yi a gidan ba don ina so ba, yanzu kuma tun da ita ma ta gaji ni me zai sa na koma?"
Na ƙare maganar idona a kanta, tagumi ta cire sannan ta yi shiru na ɗan lokaci. Mintuna a tsakani ta ce,
"Yanzu ke za ki iya barin yaranki a hannun waccan ballagazar yarinyar, wadda ko ita yana da kyau a ce har yanzu ba a gama ba ta tarbiyar ba. Yanzu haka da zan fito na gan ta ƙofar gidan tana siyen kifin Malami Sabo, ga wani garjejen ƙato sai hira suke yi tana cin kifin a gabansa tamkar wani ɗan gidansu."

"Tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa kan doka! Saboda ban ci nanin ba, nanin ba za ta faɗo mini ba. Shi ya ji zai iya da ita ne shi ya sa ya nemi a kassara ni saboda ita. Wai har ni za a turowa 'yan daba da wasu karuwai har gida su dake ni, sannan shi don bai san darajar kansa da ta wanda yake tare da shi ba; ya ba da ƙofar su halaka ni don bai da asara. To na bar masa gidan kenan har abada, daman can kamar a saman ƙaya nake zaune ba don ina so ba."
"Ban gane ba! Kina nufin wasu suka zo har gidan za su dake ki? To me kika yi musu?" Murmushi kawai na yi mai sauti ina kallon ƙwayar idonta, sannan na miƙe na fice ɗakin tare da faɗin,
"Ni dai jira ni na kawo miki ruwa ki sha, tun da kin saka mu zuba daga zuwan ki tamkar 'ya'yan kanya."
"Dole ne ai! Don haka ki je ki dawo a yi ta ƙare, haƙuri za ki yi ki koma tun da kin saba da halinsa."
Ruwa na dire mata da kunun ayar da Umma take sayarwa, sannan na zauna ƙasa ina faɗin,
"Allah dai ya ƙara shiga tsakanin nagari da mugu. Amma ni kam na kammala rayuwa gidan Mukhtar daga wannan karon."
Sakato ta yi tana kallon na ba tare da ta ce komai ba, sannan ta miƙe tana gyara zaman jakarta ta ce,
"To ni zan tafi! Tun da zuwan nawa bai da wani amfani. Idan Umma ta zo ki ce zan dawo ganin ta wani lokaci, amma ke ko a hanya na gan ki ba zan nuna na san ki ba."

Na miƙe ina faɗin, "Ya za ki tafi ba ki sha ruwan ba?"
"Ba zan sha ba!"
Tana ƙare faɗar hakan ta fice tana saka takalminta. Har ta yi gaba ta juyo tana faɗin, "Ke! Ji na manta ban tambaye ki ba! Na ga 'yar gidanki a hargitse da na zo, me ya same ta?"

"Aljanunta ne suka tashi. Shi ya sa su Umma za su kai ta gida." Na ƙare maganar ina murmushi.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.