Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 80 of 86

"Komai na kwashe!"

"To zo mu je waje mu jira shi ya dawo a kwashe mu gabaÉ—aya"

Bayanta na bi ina ƙoƙarin goge ƙwallar da ta cika mini kurmin ido, saboda kwata-kwata na rasa me ke mini daɗi. Har ga Allah ba na son zama da Mukhtar, amma kuma ba na son rabuwa da gidan. Don na yi sabon da ba na jin daɗin zama ko'ina idan ba shi ba, ko gidan Kawu Sale da nake ban rasa komai ba amma zaman da na yi kwana biyun ba na jin daɗinsa.
Muna ƙoƙarin fitowa falon muka yi kiciɓis da Barira, fuskarta a cure tana yi mana wani irin kallon da na kasa fassara ma'anarsa. Ta gefenta kawai muka raɓa za mu fice gidan, a sama na tsinkayo muryarta tana faɗin,

"Allah dai ya sa ba a haÉ—a da kayan masu gidan ba!"

To fa! Su waye masu gidan🤭😹

D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

*Ina jin daɗin yadda kuke bin alƙalamina sau da ƙafa! Na gode sosai da addu'o'in da kuke yi mini, saboda kyakkyawar Addu'arku gare ni tana faranta mini rai sosai, matuƙa gaya😍 alherin Allah ya kai muku duk inda kuke, kuma a inda kuka kasance. Much luv you all😘*

*ARBA'IN DA BIYAR.*

"Ke! Ɗebabbiyar albarka ki shiga taitayinki baƙar almura. Figai-figai da ke amma kin iya haɗa kitifiri da salon makirci kala-kala! To ba kayan masu gida muka haɗa da su ba; rayuwarsu muka kwashe gabaɗaya za mu tafi da ita. Ban da ma kike daƙiƙiya ba ki da ƙwai balle dunge a cikin gidan, amma kike tinƙaho da shi? To buɗe kunnenki da kyau ki ji; da gidan uba ake ado saboda shi ne tabbatacce ba gidan miji ba. Mijin ma irin Mukhtar da ko kansa bai taimaka ba, balle ya taimake ki ku gyara gidan da ke barazanar mutuwa da ƙazanta!"
Zancen Umma kenan tana nuna Barira da hannu cikin ƙololuwar ɓacin rai. Janyo Umma na yi da nufin mu tafi, don ba na so a sake yin wani abu a ce mu ne da laifi. Barira sai kallon banza take aiko mana tun lokacin da Umma ta fara magana, tana wurgo mana hararar sama da ƙasa riƙe da ƙugunta har da murguɗa baki.
Zuciya ta so ingiza ni na kifar da ita, domin ban san lokacin da na saki Umma na isa wurinta ina nuna ta da hannu ba. Amma bakina yana rawa na kasa furta ko kalma ɗaya saboda tunanin kalar dukan da zan yi mata. Duk da bandejin da na gani damɓare a gefen kanta ya nashe da jini.
Umma ta yi hanzarin cewa da ni, "Zo mu je kada ki biye wannan shashashar da ko uwarta ba ta ragawa balle uwar wasu. Ko da yake ma abin a nono aka tsotso, don barewa ba ta gudu ɗanta ya yi rarrafe! Ladi cinnaka ce banza ko Amadu Ƙwambo"
Ƙwafa kawai na yi raina a ɓace na juya, bayan na gama yi mata kashedi da ido tamkar na rufe ta da duka. Muna gaf da fita gidan na tsinkayo muryarta a sama tana faɗin,
"Allah dai ya raba mu da gayyar jaraba a gida. Yanzu mutum ya sakata ya wala babu mai takura shi ko a saka masa ido ana neman tona masa asiri. Wuuuu! Allah ya raka taki gona!"

Raina ya zo wuya na juyo da nufin nuna mata tawa kala, Umma ta yi saurin riƙe ni tana faɗin, "Kada ki ƙarasa gawar da ba taki ba! Na fahimci inda ta dosa abokin mutuwa kawai take nema. Mu tafi kawai kowa halinsa ya cece shi khairan ko sharran!"
Har muka shiga mota Barira ba ta daina jefo mana magana ba, bayan sowar da take yi tana faÉ—in gaba gaibu. Inna Kulu ta zuro hannu tana faÉ—in,
"Ke arrr! Tabbatacciya mara É—a'a! In dai gidan miji ne ke ma ba ki da cikakken garantin zama a cikinsa."
Ina hangen ta ta madubi bayan motar ta juya, har da tiƙar rawa take yi tana dafe kai domin ta nuna mana jin daɗinta a fili. Muna gaf da ficewa layin na hango Taufiƙ cikin sauri na ƙwala masa kira, sannan na ce da mai motar don Allah ya ɗan tsaya.
Da sauri ya iso jikin motar yana gaishe mu fuskarsa babu walwala. Nan take na ji hawaye ya cika mini ido saboda ramar da na gani ta bayyana a kan fuskarsa.

"Ya jikin Baban naka?"

"Da sauƙi!"

"Don Allah ka yi masa sannu da jiki kafin mu zo. Allah ya ƙara lafiya."

"Amin." Ya faÉ—a sannan ya bar jikin motar hannunsa É—aya a kai, ban san lokacin da na ce da shi ba,

"Mamarka ta kira ka?"

Hawaye ya sharce sannan ya girgiza kai ya bar wurin hannunsa ɗaya a aljihu, ɗaya yana shafar fuskarsa da jikina ya ba ni kuka ne yake yi. Kuka ya suɓuce mini na ɓalle murfin motar na fito, kiran shi na yi cikin muryar kuka ya waigo ba tare da ya dawo ba. Na yi tattaki da kaina na isa inda yake, hawaye shaɓe-shaɓe a kan fuskata na ce da shi,

"Ba ni lambarka za mu yi waya!"

Ya faÉ—o mini na yi saving a wayata sannan na ce da shi,
"Mutanen Kano sun san abin da ke faruwa?"
Hawaye ya sharce sannan ya É—aga mini kai ba tare da ya yi magana ba.
"Ok tom! Ina Bafarawa Estate! Idan akwai wani abu da kake buƙata ka same ni a can. Zan kira ka a waya sai ka yi saving lambata. Allah ya kawo mana sauƙi a cikin al'amurranmu duka."
"Amin" kawai ya ce sannan ya yi gaba, na koma motar muka fice layin zuciyata cike da ƙunci. Don ganin sa ya haifar mini da damuwar da Barira ba ta yi nasarar saka ni cikinta ba.

"Yaron nan ya ba ni tausayi matuƙa wallahi! Ubangiji ya zama gatansa ya dawo masa da uwarsa kusa."

Zancen Inna Kulu kenan da ya taɓa mini zuciya sosai, saboda mummunar ƙaddara ce kawai ta hau kan Maman Taufiƙ. Ta bar yaronta a gantale bayan ta illata masa Mahaifi balle ya rage masa zafin rashin ta kusa da shi.
Kiran shi na yi tana shiga na ce da shi ni ce, sannan na jaddada masa idan akwai wani abu ya kira ni. Haƙuri na dinga ba shi saboda na ji sautin sharɓen kukan da yake yi a cikin wayar.
Umma da ta cire tagumin da ta yi ta ce,
"Yaro da gatansa an mayar da shi marayan ƙarfi da yaji. Ubangiji ya karkato hankalinta ta dawo gida tun kafin lokaci ya ƙure mata."

"Amin" muka haÉ—a baki wurin faÉ—a, sannan shiru ya ratsa tsakani babu wanda ya sake cewa komai tsawon lokaci. Inna Kulu ce ta kawar da shirun da sauke ajiyar zuciya ta ce,
"Allah ya kare mu da tsaka mai wuya. Don duk kishin da zai rufe mana ido mu aikata ba daidai ba; ya zame mana musibar da za mu roƙi Ubangiji ya shiga tsakaninmu da ita! Allah ka dawo da ita hanyar gaskiya ko don yaronta"

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.