Abokin Aikina Complete Hausa Novel
Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 66 of 86
Haidar ya faɗa yana wata tafiyar gayu hannuwansa duka a aljihu. Daga ni har Inna Kulu dariya muka yi, saboda har da doro yake haɗawa yayin tafiyar yana jefa ƙafa tamkar wani sabon gurgu.
Duk abin da muke yi Umma tana cikin É—akinta ba tare da ta ce da mu komai ba.
Inna Kulu ta shimfiɗa mini tabarma a tsakar gidan na zauna, sannan ta kawo mini tuwon dawa da miyar kuka ta sha nama. Na zauna ina ci tare da Haidar tana tsokanar shi da sunan acici ba ya ƙoshi.
Daga nan inda muke na jiyo sautin Umma cikin fushi tana faɗin, "Babu wata gaisuwar ka da nake buƙata. Ka yi gaggawar kawo mata takardar sakinta cikin mutunci, ko kuma kotu ta raba mu da kai cikin tsiya."
Ban san me aka ce da ita cikin wayar ba, amma tabbas wani sanyin daÉ—i ya ziyarci zuciyata. Domin na tabbatar Mukhtar ne take waya da shi, kuma matakin da ta É—auka a kan aurenmu ya yi mini daÉ—i sosai.
"Babu wani daɗin bakinka da zai yi tasiri gare ni a wannan karon. Abin da nake so da kai kenan, ko da arziƙi ko da tsiya-tsiya."
Shiru muka yi dukanmu, ina ta juya maganganun Umma cikin raina. Inna Kulu ta miƙe ta yi ɗakin, Mintuna a tsakani na ji ta fara faɗin,
"Kada ki yanke hukunci cikin fushi Habi. Ki bari a bi komai a hanka..."
"Babu wani hankali da zan bi Mukhtar da shi yanzu! Allah ya tsine wa damarmakin da aka ba shi a baya yana fatali da su cikin izgilanci. Ko ya ɗauka neman kai nake yi da ita ne? Shi ya sa yake abin da ya ga dama ana ƙyale shi don albarkacin 'ya'yan shi. To wannan karon; ko ɗa dubu ne a tsakaninsu sai ya ba ta takardarta. Idan kuma ya ƙi bi ta lallami; zan nuna masa na fi shi zafin kai. Har yaushe zai dinga dawo mana da hannun agogo baya? Sai an yi gaba a dawo baya! Kullum da sabuwar matsala yake zuwa. To idan na danne ta cikin gidansa yana cusguna mata; wallahi a wannan karon ba zan zaunar da ita ta ƙara fuskantar baƙincikin kishiya ba."
Daga nan inda nake zaune, ban san lokacin da na juya gabas na yi Sujudu shukur ba. Saboda tsabar farincikin da ya lulluɓe zuciya, bayan wani sabon kuzarin da na ji ya shiga jikina.
Tuwon da ke gabana na ture gefe, sannan na miƙe na nufi ɗakin Umma cike da karsashi na zauna. Inna Kulu tana ci gaba da tausar ta amma ƙanzil ba ta ce da ita ba. Hakan ya sa na yi gyaran murya na ce,
"Umma ki daina ɓata ranki a kan banza. Ki bar ni da su daga shi har matarsa na fi ƙarfinsu wallahi. Don da kin ga amaryar tasa ma ba za ki ji haushin komai ba, saboda ko matsayin 'yar aiki ba zan ɗauke ta ba balle matsayin kishiya."
"Kishiya ko ta 'yar tsana ce sunanta kishiya! Ke ba ki san ire-iren waɗannan matan sun fi komai iya kissa da kisisina ba? To ki bar raina allura ƙarfe ce! Don tuggun da za ta haɗa ke ba za ki iya yin sa ba."
Abin da Umma ta faÉ—a kenan idonta a kaina. "Hmmmm!" Ajiyar zuciyar da na sauke kenan ba tare da na sake furta komai ba. Tagumi Inna Kulu ta cire tana faÉ—in,
"Ko dai ya abin yake don Allah kada a yanke hukunci cikin fushi. A bi abin a hankali ko don yaran nan da suka fito daga jikinsa."
"Yanzu da a ce gayyar marasa albarkar nan sun illata ta ko sun taɓa lafiyarta; me zai ce? Ai ya san da zuwan su amma bai hana ba! Kenan duk abin da za su yi mata su yi kawai ya ba da ƙofa! To wallahi ko ɗiyar riƙo ce na san zafinta, balle ni na durƙusa ƙasa na haifo ta wata tara da kwana tara. Idan ma ya gaji ai babu dole! Ya sauwaƙe mata kawai tun da ba shi ne autan maza ba."
"Ke kuma ke da wa kike ta masifa har ƙofar gida ana jin sautinki?"
Zancen Kawu Sale kenan da carbi a hannunsa yana ja, alamun daga masallaci ya fito.
"Ni da mara mutuncin can Mukhtar mana! Don haka ka sani ka ƙara sani; wannan karon babu mai raba ni da shi sai Allah! Sai na nuna masa na fi shi ɗibar albarka da duk abin da yake taƙama da shi!"
Umma ta ƙare maganar a zafafe tare da ɗaga murya. "To ki fara shawo kan matsalar yaransa da ke nan ƙofar ɗakinki suna kuka. Tun da ke kullum ba ki bari a bi komai a hankali sai kin yi faɗa da tashin hankali!"
Yana ƙare faɗar hakan ya bar jikin ƙofar yana ci gaba da surutai. Umma ta yi wani mere sannan ta ce,
"Komai za ka faɗa ka faɗa kawai! Amma wannan karon ba zan ɗaga wa Mukhtar ƙafa ba! Idan kuma ka matsa sai na tattara kayana na bar maka gidanka. Na fi so na kama haya na zauna tare da ita da yaranta duka. Amma ba zan taɓa barin ta cikin baƙincikinsa ya kashe ta ba wallahi!"
"Wannan kuma naki ra'ayi ne! Don ba ki ji na ce komai a kan zamanta gidan nan ba. Idan ma zatonki don ba na so ta zauna mini ne nake so ta zauna gidan mijinta; to ki yi haƙuri na daina daga yau. Ga gida nan ta zauna daga yanzu har mahadi ya bayyana babu mai korar ta."
Ya ƙare maganar hannunsa riƙe da ƙofar ɗakinta, don har ya tafi ya dawo domin ya mayar mata da raddi. Inda da sabo mun saba ganin rikicinsu, wanda sai sun hau sama ita da shi su faɗo ƙasa su shirya kamar ba su ba.
Shi ya sa Inna Kulu da 'ya'yanta suke burge ni, saboda babu ruwansu da shiga faɗansu. Ni ma a baya idan na ga suna yi kuka nake yi, na yi ta bin su ina ba su haƙuri, amma Inna ta fahimtar da ni ba a shiga tsakaninsu kunya ake ji.
Na gasgata hakan don sai sun gama faÉ—an suna cikin fushi Umma ta ce da ni,
'Ke ni ma fa faɗan ƙarfin hali ne kawai nake yi da Salenmu. Don duniya kaf ban da kamar shi shi ma bai da kama ta.'
Murmushi na yi kawai saboda tuno zancen Ummar. Fuskata a sake na ce,
"Yanzu dai Umma don Allah ku bar maganar nan. Saboda Mukhtar bai kai darajar da zai dinga haɗa ki faɗa da ɗan'uwanki ba. Idan ta ni ce ma ko yanzu na koma gidan na ci gaba da haƙurin da nake yi. Don na san komai daren daɗewa gaskiya za ta yi halinta."
"Ba za ki koma gidansa ba! Idan kuma so kike yi a raunata ki ki je ki jira dawowar masu farautar rayuwarki!"
"Yi haƙuri Umm..."
Sallamar da muka jiyo ana rafkawa a ƙofar gida, hakan ya sa Kawu Sale ya amsa sannan ya fice. Mintuna a tsakani muka yi zaman jugum-jugum har ya dawo yana faɗin,
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.