Abokin Aikina Complete Hausa Novel
Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 31 of 86
"Yanzu miye fa'idar wannan abin da kuka aikata? Tukunna ma ke me ya kawo ki wurin nan har cikin ofishinta?"
MD ya yi magana cikin sanyin murya mai ɗauke da tsananin ɓacin rai, na ƙwace daga riƙon da Amina ta yi mini na koma kujerata ina gyara zaman mayafina, wanda ya saɓule a jikina yayin damben ba tare da na sani ba.
"Ai dole ka ga laifina yanzu, bayan ka gama kai ta har gidana a matsayin kwartuwarka kun ci amanata. Shi ne ka matsa mini a kan na je jinyar Ammi don ka ji daɗin sheƙe ayarka son ranka da ita. To Allah ya toni asirinku daga kai har ita, saboda ta bar mini shaidar da zan gane ta zo gidan, domin ta nuna mini ta fi ni matsayi a wurinka. Wallahi sai Allah ya saka mini a kan tozarcin da ka yi mini Aliyu, kuma daga kai har ita ba zan taɓa yafe muku cin amanar da kuka yi wa aurena ba."
Tana ƙare faɗar maganganun ta juya fuu za ta fice daga ofishin, kamar zautacciya ta ƙara dawowa tana nuna ni da hannu ta ce,
"Sai na nuna miki na fi ki iya karuwanci wallahi. Don sai kin raina kanki a kan wannan abin da kika aikata mini."
Tana ƙare faɗar hakan ta fice tana ci gaba da masifa cikin ɗaga murya, ƙawarta ta rufa mata baya sum-sum cikin takun munafukai. Ajiyar zuciya MD ya yi sannan cikin sanyin murya ya ce da ni,
"Ki yi haƙuri don Allah! Wani lokaci tana yin wasu abubuwa tamkar akwai wani abu saman kanta. Ban san za ta zo ba da ban bari ta fito daga gida ba wallahi, don haka duk da ban san dalilin da ya sa ta yi miki hakan ba, ina ƙara ba ki haƙuri don Allah ki yafe mata."
Kallo ma bai ishe ni ba balle na tanka masa, Amina ce kawai ta ce da shi,
"Muna zaune kawai muka ga sun shigo ita da ƙawarta suna ci mata zarafi. Mamakina ma yadda aka yi ta haɗu da wallet ɗin Zaituna, wanda kusan shi ne musabbin duk wannan jidalin."
"Ranar Alhamis ta manta shi a nan, Baba masinja ya kawo mini shi na karɓa da zummar na ajiye mata har yau na ba ta. Shi ne fa na manta shi a gida ban fito da shi ba, wataƙila dalilin da ya sa ta zargi wani abu kenan ta zo wurinta da wannan sifar. Ki ƙara ba ta haƙuri in sha Allah hakan ba za ta sake faruwa ba matuƙar da gaske ni ne mijinta."
Zantukan shi ko kaɗan ba su burge ni ba, duk da ya yi ƙoƙarin binne gaskiyar abin da ya faru, a ƙoƙarin shi na gudun zargin da za a yi mana tare da ɓacin sunanmu daga ni har shi.
Bayan ya fice Amina ta zauna ci masa albasa, tana ta ba ni baki a kan na yi haƙuri ko don shi. Ƙanzil ban ce mata ba, domin duk maganar da zan yi a lokacin sai na zubar da ruwan hawaye, kuma ba na so ta ga kasawa ta gudun ta yi tunanin matar MD ta yi nasara kaina.
Jugum-jugum muka yi daga ni har ita babu mai magana, bayan ta gama ba ni haƙuri da maganganu masu daɗin da suka rage mini takaicin MD da matar shi.
Da lokacin tashi ya yi muka fito zuwa bakin gate, sai dai mamakin da na yi duk inda muka wulga zancen faÉ—an ake yi da an hango mu a yi shiru.
Muna gaf da ficewa muka jiyo muryar Sara tana ƙwala wa Amina kira, tare muka juya bayan mun tsaya har ta ƙaraso inda muke. Kafaɗar Amina ta dafa tana dariyar shaƙiyanci ta ce,
"Ashe abin da ya faru kenan a yau? Gaskiya dai abin bai yi daɗi ba, don babu kyau abin da mutum yake yi a ɓoye a fito da shi fili a yi masa terere kowa ya gani. Ubangiji dai ya ƙara tsare tsautsayi, da ranar tonuwar asirin da ya fi wanda aka yi yau."
Ta ƙare maganar tare da yi mini wani kallon rainin hankali ta yi gaba, Amina ta yi hanzarin janyo mayafinta a fusace tana faɗin,
"Duk wanda ya faɗa miki wannan tatsuniyar gizo da ƙoƙin bai san yadda gaskiyar abin yake ba. Domin ita kanta matar MD ta yi ne a rashin sani, amman idan kina tantama ki je wurin shi ki ji gaskiyar komai daga bak..."
"Zo mu je Amina, kin san shi mutum mai mummunan zato da jiran ƙiris, komai za ki faɗa masa gaskiya ba zai hankalta ba. Idan ma abin da take tunanin gaskiya ne ita ta je ta yi idan fitsari banza ne."
Abin da na faɗa kenan bayan na yi gaba na bar su a nan, saboda na sha ganin MD yana kyarar ta ba sau ɗaya ba. A ƙarshe ya yi mata iyaka da ofishin shi komai uzuri, idan ma wani abu ne sai dai ta bai wa wani ya kai masa.
"Allah ya raba ni aikata fasadi da aurena. Ke dai da kika ji za ki iya ki je ki yi ta yi akwai ranar ƙin dillanci."
Maganarta ta sa na juyo a fusace na shaƙo wuyanta, Amina ta shiga ɓanɓare hannuna tare da faɗin a kawo mata ɗauki. Saboda ganin na kai maƙurar ɓacin ran da komai zan iya aikatwa a lokacin, domin zafafan maganganunta sun dakar mini zuciya ba kaɗan ba, wanɗanda nake ji tamkar ta ɗana mini garwashin wuta a cikin zuciyar ta fara cin wuta.
Taro aka yi mana sosai, bayan an ƙwace ta daga hannuna tana tarin wahala, ana ba ni haƙuri tana sake jifa ta da miyagun maganganu masu zafi bayan ƙazafin da take jifa ta da shi son ranta ni da MD.
Babu wanda ya ga zuwan MD sai marin da ya kwaÉ—a mata a fusace yana nuna ta da hannu ya ce,
"Matuƙar kika sake jingina ƙazafinki a kaina, sai na yi ƙarar ki a kulle ki har makulli ya yi rara, domin na ga wanda zai tsaya miki a faɗin garin nan. Me ya sa ku mutane ba ku da adalci ne? To duk iskancinki kada ki bari ganganci ya sa ki saka ni. Idan ban da ke shashasha ce har ni za ki yi ƙoƙarin manna mana sharri? Kaf faɗin ma'aikatar nan ban da wata alaƙa mai ƙarfi da kowa, idan aka wuce ta aikin da ya haɗa ni da mutum abu ne wanda kowa ya sani. Me ya sa kika manta rawar ƙafar da kike yi a kaina, a kan kawai ki samu na saurare ki na ƙi? To tun da tonon sililin kike so, idan kin manta zan tuna miki yanzu, ko satin da ya wuce sai da na ci zarafinki a kan wannan mugun abin, wanda kike ƙoƙarin manna wa wata a bisa zargi ba tare da kin tabbatar ba."
Soshe-soshen kai Sara ta fara yi tana mutsu-mutsun rashin gaskiya, tare da roƙon shi a wayance a kan ya yi shiru ya daina bankaɗa mata labulen sirri.
Murmushi na ji ya suɓuce mini babu shiri, na yi gaba fuskata a washe saboda fiye da rabin ɓacin raina ya zumame. Ban san ya aka ƙarke ba ni dai na haye adaidaita na yi gida, zuciyata cike da tunanin,
'Ya aka yi na baro wallet É—ina a gidan MD har matar shi ta gani.'
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.