Abokin Aikina Complete Hausa Novel
Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 54 of 86
Sai da na fashe da dariya sannan na ce, "Allah na tuba ka yafe ni! Wane dare ne jemage bai gani ba?"
"Na ranar mutuwarsa!"
"Idan haka ne kuwa babu abin da zai sa na damu da barazanar da iyakacinta a baki. Da ma a ce kai namijin gaske ne mai iya gamsar da mace ya cire mata kwaɗayin wasu mazan; da zan ji zafin aurenka da wannan daren da kake tinƙaho yanzu. Amma abu kamar lagwani ranar me za ta yi mini balle na ji haushin masu zuwa aro?"
Laaaa!😱ðŸ¤ðŸƒðŸ»â€â™€ï¸
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*TALATIN DA BIYU.*
"Iyyeeeee! Ke Ni kike faÉ—a wa magana irin haka mai kama da cin zarafi?"
"Ina da tabbacin babu ƙarya a cikin maganganun da na faɗa. Kai ma idan za ka yi wa kanka adalci; ka san ƙarin aure na masu cikakkiyar lafiya ne ba irinka ba. Don na sha faɗa maka mace ɗaya ma ta yi maka yawa, amma ka kasa ganewa. To ka yi auren ga ka ga amaryar, muna daga gefe mu ga kalar wainar da za a toya, don duk wanda bai ji bari ba ai ya ji hoho!"
Takowa ya yi a fusace ya tsaya gabana, nuna ni yske yi da hannu tamkar zai kai mini duka, ƙwafa ya yi ya nufi hanyar fita ɗakin yana faɗin,
"Idan ma burinki ɓata mini daren amarci ne; to haƙar ki ba za ta cim ma ruwan ba."
Ya fice tare da bugo mini ƙofa da ƙarfi. Harara na aika wa ƙofar sannan na miƙe da nufin rufewa da makulli. Sautin maganganun da na ji ya sa na yi riƙe hannun ƙofar ba tare da na bar wurin ba.
"Don Allah ki yi haƙuri, wallahi ba hirar arziƙi ce muka yi ni da ita ba."
"Ka je kawai ka kwanta ni ina nan, don wallahi ba zan bari ka taɓa jikina ba bayan ka gama holewa da uwargidanka."
Dariya ta suɓuce mini duk da mugun haushin maganganun amarya da na ji. barin ƙofar kawai na yi na kwanta, zuciyata cike da tunani tare da tausayin Barira a raina.
Saboda ko maƙiyiyata ba na mata fatar auren Mukhtar, balle irinta da tashi ɗaya na fahimci rawar kan da take yi a kansa.
Ban san ya suka ƙarge ba saboda addu'o'in baccin da na karanta, sun yi tasiri wurin mantar da ni komai a dalilin nannauyan barcin da ya ɗebe ni.
Da safe na tashi da wuri na shirya mana breakfast, saboda na taras da doya da kiret ɗin ƙwai har biyu a kitchen. Hakan ya sa na fahimci abin da yake so a yi kenan, Ummu Salma ta taya ni muka kammala.
Namu muka ci sannan suka tafi islamiyya, na koma ɗakina na kwanta ina huce gajiya. Ba tare da na kalli ƙofar ɗakin amarya ba balle na nemi inda take, saboda maganganun jiya da kunnuwana suka jiyo sun sa na ji ta sire mini. Sannan gargaɗin da Mukhtar ya yi mini ya ƙara tunzura ni na tsaya inda Allah ya ajiye ni.
Misalin ƙarfe goma saura na ji an fara ƙwanƙwasa mini ƙofar ɗaki. Sanin cewa ba su Haidar ba ne; na miƙe jikina babu ƙarfi saboda baccin da ya kwashe ni, a kasalance na buɗe ƙofar.
"Ina kwana Aunty?"
"Lafiya lau!"
Na amsa mata a gajarce, tana wasa da yatsun hannunta ta sake cewa,
"Abin karinmu ya ce na karɓo"
"Ki je Kitchen za ki ga komai a kan table. Na zaci bacci kuke yi shi ya sa ban yi karambanin tayar da ku ba."
Na ƙare maganar ina murmushin yaƙe, "Hmm! Aunty ai tun ɗazu idonmu biyu."
"Ok tom! Ki je ki É—auka."
Ta juya na bi shamulallen ƙugunta da kallo ina ƙumshe dariya, saboda yadda take ƙoƙarin karkaɗa shi ta ƙarfi amma ko motsi babu balle su taka rawar disko.
Wanka na faɗa sharp-sharp na shirya cikin riga da wandon atamfa, wadda ta zamo half gown da falalin wandonta ya baje a ƙasa. Na kafa ɗaurin ture ka ga tsiya na koma kitchen da zummar ɗora girkin rana. Shigowar su Ummu Salma suna ihun Mama mun dawo, ya sa na yi saurim ƙwala wa Haidar kira. Saboda shi ne mara jin cikinsu kuma ba na so ya ce zai je ɗakin amarya, gudun ya gano abin da ya fi ƙarfin idonsa.
Ya gida suka fara yi mini, sannan na ce da su kada wanda ya shiga É—akin amarya. Su jira idan ta fito su gaishe ta, ficewa suka yi bayan sun tabbatar mini da ba za su je ba.
Hankalina a kwance na kammala girkin cikin É—an lokaci, zuba wa tsuntsayen soyayya na yi a kula na ajiye gefe. Sannan na zuba namu a tire É—aya muka baje tsakiyar kujeruna.
Muna tsaka da cin abincin, na ji sallamar wani a bakin ƙofar falonmu. Haidar ya amsa ya miƙe ya isa inda mai sallamar da gudu, domin ya ji mana abin da ya kawo shi.
"Ka faÉ—a wa babanka ga ni na zo!"
"Mama Nura mai Chemist ne yake neman Abbanmu!"
"Nura kuma? To waye bai da lafiya a gidan nan?"
Tambayar da na yi kenan a zuciyata ashe ta fito fili. Tsintar muryar Barira na yi bayan ta buÉ—e É—akinta tana faÉ—in,
"Romiyo ne yake zazzaɓi! Shi ne ya kira likita domin a zo a yi masa allura."
'Romiyo?'
Na jefi kaina da faÉ—ar sunan a zuciyata, a take na faÉ—aÉ—a fuskata da murmushi na ce.
"Allah Sarki! Haidar je ka ce da Nuran ya shigo"
Bayan na gama ba shi umurnin na ci gaba da cin abincina. Haidar a gaba Nuran yana bayansa suka doshi É—akin Barira, na yi hanzarin cewa da shi,
"To kai Alhaji zo mu kammala cin abincin kai muke jira." Saboda ba na so ya shiga É—akin.
Ya dawo ya zauna muka ci gaba da cin abincinmu, Barira ta juya ta koma É—akinta ta bar ni da mamakin ciwon Mukhtar a farkon daren amaryarsa. Saboda sanin da na yi masa shekara yake yi bai kwanta ciwo ba, domin Allah ya wadata masa lafiya ba kamar ni mai yawan laulayin ciwo kala-kala ba.
Mintuna a tsakani Nuran ya fito Barira a bayansa yana faÉ—in,
"Don Allah kada a dame shi a bar shi ya huta sosai."
Muƙus na ga ta yi ba tare da ta tanka masa ba, alamunta ya nuna a zahiri ba ta ji daɗin maganarsa ba.
Kitchen na ga ta wuce, ɗan lokaci a tsakani ta fito da kulolin da na saka musu abinci, ta yi ɗakinta tare da rufo ƙofa. tun daga lokacin ban sake jin motsinsu ba daga ita har shi.
Baƙinta ma da ke zuwa haƙura suke yi su tafi idan sun gaji da zama, saboda ta ƙi buɗe ɗaƙin balle ta fito ta bi kan 'yan taya ta murnar auren. A taƙaice dai ranar Mukhtar bai fito ba har sai da aka yi sallar Asr. Sannan ya fito dafe da ƙugu yana tafiya tamkar mai tata, sai nishi yake yi yana faɗin,
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.