Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 24 of 86

Minti biyar kacal ta fito riƙe da ƙugun Ummita da ke riƙe da jakata tare da wani matashi hannun shi da ya ɗaga hannun shi sama alamun miƙa wuya. Motar aka watsa su duka sannan aka ba ni jakata bayan na buɗe ta gaban kowa, kuma na tabbatar musu da komai yana ciki yadda na saka.
Motar 'yansandan ta fara barin ƙofar gidan tare da mutanen gidan da suka kwasa, kafin ta MD ta bar wurin tare da ni da ke baya na hakimce ina hurar hanci. Amma duk da hakan nan take gumi ya jiƙa mini fuska, zuciyata ta hau bugawa da sauri tamkar za ta fasa ƙirjina ta fito waje.
Saboda hango Mukhtar dumu-dumu a cikin 'yan kallon da suka zagaye mu suna rabon idon ganin ƙwam. Wanda shi ma nake da tabbacin ya gan ni a lokacin da zan shiga motar MD, na yi mamaki matuƙa da ganin shi wurin, tare da ko-in-kulan da ya yi wa ganina ba tare ya nuna ya san ni ba, balle ya ɗauki mataki a kaina ko a kan MD.

Ban dawo natsuwata ba har sai da na ga mun shiga gidajen Sama road, mamaki ya so kashe ni saboda ganin da na yi ya doshi hanyar da za ta kai mu Bafarawa Estate.
'Ina zai kai ni?'
Ita ce tambayar da na yi wa kaina a zuciya, sai ga amsa tiryan-tiryan ta bayyana kanta. Domin kuwa ƙofar gidan Kawu Sale ya ci birki, gidan da Ummata take rayuwa tun da jajayen sawu har yanzu da girma ya kamata.
"Fita ki je! Kuma ki yi mini sallama da Umma!"
Zancen MD kenan a fusace kuma cikin ɗaga murya. Haka na fito tamkar wadda aka kama ta yi wa Sarki ƙarya. Haka na fito jiki a mace na ja jakar kayana da ta hannuna na yi cikin gidan, ba tare da na waigo ba balle na damu da ce masa na gode.
Saboda har raina ban ji daÉ—in taimakon da ya yi mini ba, tun da har ya kawo ni gidan a maimakon tashar da nake so ya kai ni.
'Tukunna ma wa ya sanar da shi unguwar su Umma da gidan duka?'
Tsaki na ja sannan na faɗa gidan ko sallama babu na yi ɗakin Inna Kulu ina haɗe fuska. Ummata da Inna Kulun duk suna tsakar gidan amma babu wanda na yi wa magana. Saboda tsabar mugun haushin da MD ya cusa mini a zuciya, ji nake yi tamkar na kama da wuta na ƙone ƙurmus kowa ma ya huta.
Ina ji lokacin da wani yaro ya shigo yana sanar da Ummata ana sallama da ita waje. Ban san ya aka yi ba ni dai na ji ta shigo tana balbala faÉ—a tamkar ta ci babu.
Sai ga ta cikin ɗakin tamkar an jefota, ba ta yi ƙasa a gwiwa ba kawai ta fara kai mini duka da hannu bibbiyu tana kuka. Da ƙyar Inna Kulu ta taɓe ni a hannunta bayan ta gama jibga ta son ranta har da gwabra kaina a bango.
Ban haushin abin da ta yi mini ba, domin ba na tantama a kan ta yi hakan ne kawai saboda ta huce haushin da na ba ta a lokacin, wanda ni ko kaÉ—an ban ji dukan ba, don zafin da zuciyata ke yi ya fi dukan da take yi mini linkin.
Inna Kulu ta fitar da ita daga É—akin tana haki, tare da jifa ta da miyagun maganganun da suka tsaya mini a zuciya. WanÉ—anda suka saka ni sabon kuka tare da yi wa Mukhtar Allah ya isa ta fi dubu, saboda shi ne ya shiga tsakanina da ita, kuma sanadin shi ne ta fara kyara ta, tare da jifa ta da miyagun kalamai munana, a duk lokacin da rigima ta haÉ—a ni da shi.

'Ina mafita?'
Tambayar da na yi wa kaina kenan bayan na gama naÉ—e maganganun Umma a kwanyata. Domin babu komai a cikinsu sai muguwar fata gare ni, a kan muddin ban koma gidan Mukhtar na ci gaba da zaman 'ya'yana ba.

Hmmmm! Ana dara ga dare ya yi

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

*LAMBA SHA SHIDA.*

Daga nan ɗakin da nake ina jiyo sautinsu ita da Inna Kulu tar-tar a cikin kunnuwana. "Haba Kulu! Shi kenan kullum abu ɗaya za a dinga yi? Har yaushe Zaituna za ta gano abin da nake lurar da ita? To ni kam a wannan karon, wallahi zan fitar da wuyan hannuna a cikin duk abin da ya shafe ta. Ta je ta yi duk abin da take so tun da ta isa da kanta da rayuwarta, amma wallahi ba zan zauna da ita cikin gidan nan ina ganin wulgawar ta ba. Don duk lokacin da na tuna ta kashe aurenta ta bar 'ya'yanta a wulaƙance sai na ji baƙinciki."
"Ki yi haƙuri Habi, tun da dai hannunka ba ya ruɓewa ka yanke shi ka jefar." Zancen Inna Kulu kenan cikin tausasa murya a ƙoƙarin ta na tausar Ummata, daga mugun fushin da ta shiga tana ta feso hayaƙin maganganu masu nuni da zallar ɓacin ran da ta shiga, sannan kuma masu kama da yi mini baki a fakaice.
"To ke Kulu sau nawa mutum ya sa aka cire masa hannun aka jefar? Ai sai dai idan ba ta kama ba. Don haka ta tashi ta koma gidan mijinta yanzu tun muna shaida juna. Idan kuma zaman gidan take so ni zan bar mata gidan ta zauna, amma ba za mu jeru ni da ita ba"

"Ba za ta zauna gidan nan ba, sai dai ta koma gidan Alhaji Ali tun da daman can shi yake ɗaure mata ƙugu tana iskanci."
Maganar Kawu Sale kenan da na tsinkayo muryar shi a sama alamun shi ma ya É—auki zafi da ni.
Hawayena na share sannan na miƙe ina gyara zaman mayafin da ke jikina, na rataya jakar hannuna, na ja ta kayana na fito ɗakin.
Ƙofar fita gidan na nufa ina sharɓen kuka ba tare da na ce da su ƙanzil ba, "Wallahi muddin kika fita gidan nan a yanzu sai na tsine miki albarka, matuƙar ba gidan Mukhtar za ki koma ki rungumi 'ya'yanki ba."
Turus na yi babu shiri na ja na tsaya, domin a raina babu zancen komawa gidan Mukhtar har abada. Inna Kulu ta zo har inda nake ta karɓi jakata tare da riƙo hannuna muka koma ɗakinta.
Nasiha ta fara yi mini cikin kwantar da murya, tana ƙoƙarin fahimtar da ni muhimmancin yi wa Umma biyayya, da gudun lalacewar tarbiyyar 'ya'yana da take yi. Wanda abu ne a bayyane ko ni na sani Mukhtar ba zai iya ɗora su a kan tarbiyyar da na ba su ba. Domin zai iya dawo da hannun agogo baya kamar yadda na sha yaƙi da shi a kansu, kafin komai ya daidaita ya daina mayar mini da 'ya'ya kishiyoyi. Saboda duk wani aikin da ya dace mata ta yi wa mijinta idan aka cire kwanciyar aure, to shi yake saka su ba tare da ni ya damu da ni balle ya ce na yi masa. A kan haka mun yi faɗa ya fi a ƙirga da ƙyar na samu ya daina, saboda ƙaƙƙarfar iyakar da na yi masa da yarana.
Da wannan tunatarwar Inna Kulu ta samu kaina na rage kukan da nake yi, saboda matuƙar na ce zan tsallake na watsar masa da su, to babu makawa sai ya dawo da bara bana. Idan kuma hakan ta faru to babu amfanin nema wa kaina 'yanci bayan na wargaza tarbiyyar yarana.
"A ce.. ya kawo.. su idan.. na... tashi mu koma.. tare da su..."
Maganar da na faɗa kenan cikin ajiyar zuciya da shesshekar kuka. Domin jikina ya yi sanyi ƙalau musamman da na tuno lokacin da ya rufe su a ɗaki suna kuka, ba tare da ya damu da rarrashin su ba balle ya nuna musu tausayi irin na Uba.
"Tun da sassafe yau ya kira Ummarki yana sanar da ita ba ki kwana gidan ba, shi ma bai san ba ki nan ba har sai da ya zo yi miki ina kwana sannan ya gano ba ki gidan."
Murmushin takaici na yi sannan na ce, "Idan har da gaske ya san ban kwana gidan ba, to dole ne a ce yana sane na fita ko kuma a kan idon shi. Idan kuma har bai san ba na gidan ba har sai da ya zo yi mini ina kwana kamar yadda ya ce. To bai da masaniyar lokacin da na fita balle ya san gidan na kwana ko ba gidan ba. Abu na ƙarshe kuma ni rabon ina kwana ta haɗa ni da shi; na yi masa ko shi ya yi mini an fi shekara uku ko huɗu. Domin ko sallar asubu ba ya tayar da mu daga ni har yaran, balle zuwa ya ga tashin mu idan safiya ta waye."

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.