Abokin Aikina Complete Hausa Novel
Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 62 of 86
"Me ya faru da Sarar ne?"
Tambayar da na cillo mata kenan, saboda ina so na ji domin mu tattauna abin da ya kawo ni.
"Sara dai halinta na tumasanci ta aikata, har ta janyo Basiru ya darza mata ɗan banzan kashi. Sannan ya yi mata saki uku ringis, saboda ya kama ta da almajirin gidansu turmi da taɓarya a cikin ɗakinta."
Babu shiri na furta, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Ke duniya ina za ki da mu?"
"Bari kawai! Ta gama aibata ki cikin mutane ta manna miki sharri. Sai ga shi ita kuma abin ya zo kanta, bayan tayar da jijiyoyin wuyan da Basiru ya gama yi a dalilinta. Duk da kuma shi da ita duka kanwar ja ce! Amma dai nata ya fi muni a matsayinta na 'ya mace."
Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce, "Kada ki shiga cikin masu zancen duk abin da namiji ya yi ado ne. Saboda shi kansa rami ne yake haƙa wa kansa da kansa, wanda idan ba Allah ya tsare ba; shi zai rufta cikinsa tare da Iyalansa duka. Saboda shi ya sayi komai da hannunsa kuma zai girbi abin da ya aikata ko da bayan ya manta. Duk da ban san wane ne Basiru ba sai a bakinku, amma ina da cikakken tabbaci a ksn haƙƙin abin da ya yi ne yake bin sa sanadin Sara."
"Ban gane ba! Ita ma fa haka halinta yake kuma ya sani tun kafin su yi auren sun yi rayuwa."
"To kin ji inda tushen matsalar ya samo asali! Daman an ce wanzam ba ya son aska a jikinsa. Ba wai ina goyon bayan abin da Sara ta aikata ba, amma wallahi Basiru shi ne silar komai. Wataƙila akwai haƙƙin wasu da yake bin sa, wanda Allah ya jarrabe shi ta wannan hanyar domin a rama abin da ya aikata. Saboda sau da yawa mutane su suke janyo wa kansu bala'i da hannunsu, don ba zai taɓa yiyuwa ka yi wa 'yar wani kai ma abin ya ƙi zuwa kanka ba. Idan ba ka da 'ya'ya akwai na dangi ko kuma a juye komai a kan matarka. Allah dai ya ƙara kare mu ya kare zuri'armu, amma wallahi maza da yawa suna aikata abin da suke kira ado, daga baya haƙƙi ya bibiye su har ya samu hawa kansu ya zauna daram!"
Murya a sanyaye Amina ta ce, "Na yarda da zancenki Maman Haidar. Don ko shi an ce ta sha kama shi da mata, wai da ta zo aiki sai ya kwashi mata ya kai gidan. Watarana ta mamaye shi ta koma gidan ba lokacin tashi ba, ta kama shi hannu dumu-dumu da macen banza suna lalata."
Murmushi na yi mai sauti sannan na ce, "A tunaninki idan da a ce shi ne ya sha kama ta aurensu zai yi ƙarkon da zai kawo yanzu?"
"Gaskiya ba zai yi ba! Don a tashi guda zai hankaÉ—a ta gida, tare da takardar sakinta kamar yadda ya yi mata yanzu."
"Kenan shi ne kawai mutum ita daga sama ta faɗo? Wallahi sha'anin maza yana ba ni mamaki. Laifi goma suke yi wa mace ta danne ta yi haƙuri, har ma ta yi ƙoƙarin ɓoyewa gudun wani ya ji a yi masa ɗan kallo. Amma shi guda kacal za ta aikata masa ya tona mata asiri ya rabu da ita."
"Wallahi haka ne tabbas! Allah dai ya kyauta kawai, amma maza ba za su iya yin kwatar haƙurin da muke yi da su ba. Miye labari? Don tun da na gan ki na san ruwa ba ya tsami banza."
'Yar dariya na yi sannan na ce, "Kenan dai idan babu dalili ba zan zo ba?"
"Sosai ma! Yan ofishimu har gori suke yi mini a kan zuwan da nake yi wurinki kullum ke ba ki zuwa. Don na san yau sai na sha surutunsu, duk da zuwan naki zai yi amfani, ko ba komai kin wanke mini gorin da suke yi mini koyaushe."
"Su dai mutane ba su raina abin magana." Abin da na faÉ—a kenan ina murmushi tare da gyara zamana na labarta mata komai.
Shiru muka yi dukanmu kafin Amina ta sauke ajiyar zuciya tare da faɗin, "Danƙari!" Dariya muka yi a tare sannan ta ce,
"Gaskiya dole ki shiga tashin hankali a kan wannan lamari. Kuma ba abu ne mai sauƙi ba balle ki faɗa wa Maman Taufiƙ ta sani tun wuri, kafin labari ya dawo kunnenta ta zargi da sa hannunki a ciki."
"Kuma ba zan iya tunkarar ta da wannan batun ba. Domin ba zan taɓa zama sanadin rura wutar bala'i tsakaninta da mijinta ba."
"To ya za ki yi yanzu?"
Tambayar da Amina ta jefo mini kenan tana kallo na, "Sajida ce kawai makamin da zan riƙa domin na hana ta karɓar abin. Sai dai kuma idan Allah ya ƙaddara babu yadda zan yi da ikon Allah!"
"Ni dai da kin bi shawara kin faÉ—a mata komai ki fitar da wuyan hannunki."
Shiru na yi ina tunanin maganganun da muka taɓa yi har tana zancen ina mata fatar kishiya. Ina 'yar dariya na ce, "Ba za a ji mutuwar Sarki a bakina. Zan dai yi iya bakin ƙoƙarina wurin hana Sajida shi."
"To Allah ya kawar da fitinar da ke ciki."
"Amin"
Daga haka muka rabu saboda lokacin tashi ya yi. Har muka je inda muke tsayuwa neman abin hawa ba mu daina zancen ba.
****
Zuciyata cike da damuwa na shiga gida bayan mai adaidaitasahu ya ajiye ni. Na kwashe sauran canjin da suka rage mini na miƙa masa, jakata empty take saboda na yi ƙaf daga gida har daji.
Da guntuwar sallama na shiga falon, saboda sanin yarana ba su gidan. Ban ji motsin komai ba don ɗakin Mukhtar ma a rufe yake ruf alamun ba ya gidan. Har na gota ɗakin Barira na dawo babu shiri na tsaya jikin ƙofar, domin na ji tabbacin abin da kunnena ya jiyo mini.
Sambatu na ji wanda cikin muryoyi biyu masu ɗauke da tsantsar shauƙi. Sai ihu suke yi suna shan yaji tamkar duniyar don su kaɗai aka yi ta.
Cikin tashin hankali na nufi ɗakina saboda zuciyata da ke zargin Mukhtar ne tare da Barira a ɗakin. Amma har na zauna kan gadona ban daina jin sautinsu ƙasa-ƙasa ba, wanda kuma alamu ya tabbatar mini ba Mukhtar ba ne take tare da shi.
Don tun da aka kawo ta gidan ko daren farkonsu ban ji irin wannan ihu da sambatun ba. Haka kawai zuciyata ta kasa natsuwa da hakan, duk da na yi ƙoƙarin ture abin gefe na yi sallah.
Na fito zuwa kitchen sai dai ban ji surutan ba a lokacin, sharp-sharp na girka taliya ƙwaya ɗaya na zabga mata kayan haɗi. Nan take ƙamshi ya karaɗe gidan saboda ni kaina na san za ta yi daɗi ko a ido.
Falo na dawo na zauna, ina cin taliyar na ji ƙarar buɗe ɗakin Barira. Ban damu da kallon wurin ba balle na ga masu fitowa.
Shirun da na ji ya sa na ɗaga kaina na kalli bakin ɗakin, Barira na gani tare da wata ƙawarta sun sha jinin jikinsu. Wataƙila ganin da suka yi mini ya sa suka razana.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.