Complete Hausa Novels

Abokin Aikina Complete Hausa Novel

Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 43 of 86

A tsaye na bar ta na nufi offis ɗin MD, na tura ƙofar da sallama kai-tsaye na nufi gabansa. Takardun da ke hannuna na ajiye masa na juyo, sai dai bai fasa faɗar maganganun da yake yi a cikin wayar da na taras yana yi ba.
"Ko da Ammin ta ce ki je, to ni na ce ba za ki je ba! Kuma kada ki bari na dawo na taras da ba kya nan, Domin wallahi ba zan lamunci wannan rashin mutuncin da kike ƙoƙarin yi mini ba. Ok tom ki yi yadda kike so kawai tun da d..."

Iya abin da kunnuwana suka jiyo mini kenan tsakanin shiga ta offis ɗin zuwa fitowa ta, hakan ya sa bai bi ta kaina balle ya tanka ni. Bakin gate muka nufa zuciyata cike da tunanin halin matar MD, domin a lafuzzan da yake furzarwa na fahimci mace ce mai yawo, sannan ga kafiyar bala'i ta fito a cikin zancen shi ɓaro-ɓaro.

"Allah ya kyauta!"

Abin da na faɗa kenan bayan na gama nazarin kalaman shi a raina, da kashedin da ta yi mini a wayarsa lokacin da na kira shi. Har mai adaidaita ya ajiye ni ƙofar gida ban daina tunanin MD da matarsa ba, musamman sauyin yanayinsa tamkar ya kai duka a lokacin da yake wayar.

'Abincin wani gubar wani.'

Zancen zucin da na yi kenan ina tura ƙofar gidan, saboda yanayin MD ya nuna ba ƙaramin haƙuri yake yi da halin matarsa ba, kamar yadda nake haƙuri da Mukhtar duhun dare, da hasken safiya zuwa yamma.
Hannuna na bi da kallo saboda fentin da na dangwalo ban sani ba, domin kwata-kwata ban lura da sabon fentin ba har sai da na gan shi a hannuna.
Baki a buɗe nake kallon su Ummu Salma da ke tsakar gidan suna shirin makaranta. Jakunkunansu da komai a wurin suna ƙoƙarin shjryawa, ƙofar falon na bi da kallo saboda ganin ita ma ta sha fenti cement color kalar na ƙyauren ƙofar gidan.

Da gudu suka taso suna ihun murnar gani na, idona a kansu na ce da su,
"A nan kuke shirin yau kuma?"
Haidar ya yi saurin faɗin, "Abbanmu ya ce mu ɗauko duk abin da muke so mu tsaya nan, kada mu ɓata masa fenti."
"Ah! Tabbas ya kyauta, ko ba komai kayanku za su huta da kwasar fentin da za a sha wuyar fitar da shi idan an zo wanki."
Ummu Salma ta ɓata fuska tana faɗin, "Har fa dukan Haidar ya yi, don ya taɓa fentin bai sani ba ya goge wurin."
"Da bai taɓa ba ai ba zai dake shi ba! Ni dai ku yi sauri ku shirya ku tafi makarantar. Kun ci abinci dai ko?"
"Bai bari Aunty Ummu ta dafa mana ba, wai kada a ɓata masa fenti a bari sai gobe idan ya ƙame."
"To me kuka ci?"
Tambayar da na jefo wa Iman kenan saboda ita ce ta ba ni amsar.
"Gari da suga ya siyo mana muka sha. Kuma wallahi ni ban ma ƙoshi ba." Haidar ya faɗa yana turo baki a ƙoƙarin shi na nuna mini haushin da ya ji a kan hakan.
"Oya ku gama shirin kafin na dafa muku Indomie yanzu shaf-shaf!"
Ban jira cewarsu ba na yi ciki da sauri don raina ya yi ƙololuwar ɓaci. Kallo na bi falon da shi saboda ganin yadda aka mayar da kayan cikinsa duka gefe, an shafe falon tas da fenti mai kala biyu sai ƙyalƙyali yake yi. Sannan ƙofofin ɗakunan duka sun sha fenti har maiƙo suke yi.
Ƙofar ɗakina na tura na shiga, shi kam yana nan yadda yake ba a taɓa mini komai ba. Jakata na ajiye tare da cire hijabin da ke jikina na fice zuwa kitchen. A nan ma ya Sha fentin ko'ina fes-fes duk da an hargitsa mini kayan cikinsa.
Cikin mintuna ƙalilan na gama dafa Indomien, na wanko tire na juye duka sannan na fito tsakar gidan. A kan tabarmar da suke kai muka baje, sai da suka ci suka ƙoshi har suka bar mini saura. Sannan na yi musu addu'a kamar yadda na saba suka fice suna faɗin "Mama sai mun dawo."
Da sauri na miƙe saboda alamun zuwan period da na ji a jikina. Wanka na faɗa a gurguje na fito, a nan na ga toilet ɗin ma ya sha fenti har da ƙyauren ƙofar.
Murmushi na yi a raina na ce, 'An zo wurin' Domin har cikin zuciyata ina farincikin auren duk da bai fito ya sanar da ni ba.
Bayan na kimtsa na dawo kitchen na ɗora mana girki dare, saboda time ya tafi biyar har ta wuce. Kasancewar ina da sauran garin semo tuwon shi na yi mana shaf-shaf da miya yauɗi. Na jefa mata ƙwarorin busasshen kifin da ya rage mana nan take ƙamshi ya karaɗe gidan.
Ina tsaka da kaÉ—a miyar Mukhtar ya shigo kitchen É—in, hannuwansa a aljihu ya tsaya bayana bai ce da ni komai ba. Tun kallon farkon da na yi masa ban sake bi ta kan shi ba har sai da ya yi gyaran murya ya ce,
"Girki kike yi?"
"Idonka ya ganar maka ai!"
Amsar da na ba shi kenan, ba tare da na daina abin da nake yi ba.
"Ban so aka yi girki a gidan nan yau ba, saboda fentin nan ba na so a lalace shi tun kafin ya gama ƙamewa."

"Idan kai ka iya hora Yaranka saboda fenti, ni kam ba zan iya barin su da yunwa ba a kan ka yi sabon fentin."
"To shi kenan a bar zancen kawai, daman ina so na sanar da ke auren da zan yi a cikin satin nan mai zuwa. Saboda ba na so ki ji a wani wuri gara ki ji komai a bakina."

Dariya na yi mai sauti sannan na saukar da miyar ina goge wurin da na ɓata na ce, "Wannan ai abin farinciki ne ba kaɗan ba. Da ka faɗa mini da wuri ma ɗakina zan bar wa amaryar na koma ɗakin su Ummu Salma. Saboda sai ta fi jin daɗinsa fiye da ɗakinsu don ya fi shi girma. Amma tun da a can ka fi so ta zauna shi kenan babu damuwa, ina taya ka murna Allah ya kawo ta lafiya, kuma ya ba da zuri'a ɗayyiba a tsakaninku."
Shiru ya yi kawai yana kallo na, ni kam abincina kawai na zuba a plate na raɓa gefen shi na fice. Jikina ya ba ni kallon mamaki ya ni da shi a lokacin da zan bar kitchen ɗin, shigowar su Ummu Salma ya sa na fice tsakar gidan ina cewa da su su je ɗakinmj su cire kayan makarantarsu, su yi shirin sallah.
Kujerar roba na janyo na zauna a tsakar gidan ina ta cin abincin ina 'yan waƙe-waƙena. Tsayuwar shi kawai na ji a gabana yana huci ya ce,
"Ko ba ki yi hakan ba, na san yanzu ba kya so na, to ki sha kuruminki in dai ni ne sai na nuna miki na fi ki rashin mutunci. Kuma ki sani ban ji zafin kin daina kishina ba, tun da zan auro mai sona tsakani da Allah kuma wadda ta san zafina. Ki je ki ci gaba da ƙuncinki ni ko a jikina wallahi, don ba ke kaɗai Allah ya ba ni damar aure ba balle ki nemi wulaƙanta ni a banza."

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.