Abokin Aikina Complete Hausa Novel
Reading file: Abokin_Aikina_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 26 of 86
Zancen zucin da na yi kenan kafin na ji ɗaci ya ziyarci kan harshena, a sanadiyyar muryar Baba Sale da na ji yana faɗin, "Ke Habi ba haka ake sulhu ba, yadda ya kawo ƙara ya dace ki tsaya a saurari ta bakin..."
"Babu abin da zan tsaya sauraro daga gare shi Sale, don magana ta gaskiya kai kanka ka san Zaituna ta sha wahalar auren shi. Kuma ba wai mun rasa inda za ta zauna ba ne ko abincin da za mu ba ta, balle ya zargi neman kai muke yi da ita shi ya sa muke tauye ta zama da shi koyaushe. Don haka idan har ya gaji babu dole ba sai ya yi ta ɗora mata ƙazafi ba, ya sake ta kawai gari da yawa maye ba zai ci kan shi ba wallahi. Amma ba ita ba ni kaina na gaji da matsalolin shi, idan bai gyara ba a wannan karon; to zan bai wa Babanta Ali dama ya raba auren kowa ya huta. Don daman can ni na hana da yanzu duk mai sha ta sha komai ya zama labari. Miji goma ai ba Uba goma ba ne."
Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi tamkar an sauke mini ƙaton dutsi a saman kaina, domin yau kaɗai Umma ta tabbatar mini da lalle ita ce ta haife ni. Saɓanin baya da nake tantamar hakan a duk lokacin da ta ɗauki gaskiya ta miƙa wa Mukhtar. Ko idan ta kawar da kai ga duk matsalolin shi idan na rattaba mata, a matsayin kare kaina daga wani laifin da ya ƙaƙaba mini ban ji ban gani ba, ko faɗan da take yi mini a kan boren da nake yi wa auren lokaci bayan lokaci.
"Wallahi Umma ban san ta fita ba, sai bayan na farka tsakar dare na ga ƙofar gidanmu a buɗe. Kuma na yi ta kiran lambarta ban samu ba, haka ma sai da na biyo sawunta kafin na sake rufe gidan. Ke ce kawai ban yi tunanin kira ba sai da safe gudun na tayar miki da hankalin."
"Ai da zafi-zafi ake bugun ƙarfe ba sai ya huce ba, domin da ka kira ni a lokacin dole mu fita neman ta mu da muka san zafinta. Saɓanin kai da rashin ganin ta bai hana ka komawa gidanka ka rufe ba, saboda ba ka da asara ko mutuwa ta yi akwai mata da yawa a gari har waɗanda suka fi ta."
Cikin kakkausan sauti na ji Umma ta ba shi amsa mai harshen damo. Babu shiri na maka wa ƙofar harara saboda maganar da na ji yana faɗi daga bakin shi cike da yaudara da daɗin baki,
"Yanzu dai don Allah Umma ku yi haƙuri, in Sha Allah hakan ba za ta sake faruwa ba. Domin Wallahi gabana har faɗuwa yake yi a duk lokacin da na ji ana zancen sakin nan. Saboda ko maƙiyina ba na fatar ya saki matar shi balle ni na aikata. Kada Allah ya nuna mini ranar da zan furta wannan mummunar kalmar daga bakina zuwa ga Zaituna."
To ni ma dai ga tawa harara🙄haɗi da tsaki😼 zuwa ga Muntari😂
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA SHA BAKWAI.*
Shiru na ji ya ratsa tsakani bayan maganar Mukhtar, sannan na ji muryar Kawu Sale yana faɗin, "Yanzu ke Habi tun da ya gano laifin shi, yana da kyau a ƙara ba shi wata dama. Idan har ya kiyaye abubuwan da ke janyo musu rikici shi kenan matsala ta kau, saboda haka ki zubar da komai a daina bitar abin da ya wuce. Kai kuma tsakani da Allah matuƙar ba ka gyara halinka ba, to duk abin da ya ƙara tasowa a gaba kada ka ga laifin kowa kai ka janyo. Abu na ƙarshe kuma ka daina zargi, domin muddin ka tsayu a kan zargin matarka to ba za ka taɓa jin daɗin zama da ita ba. A wani ƙaulin Malamai ma an tabbatar da cewa zargi yana ɓata aure."
"Ni a wurina komai ya wuce Kawu, amma maganar gaskiya aikin nan da take zuwa, ko kaɗan ban da natsuwa da shi. Saboda mutumin nan babu komai a ran shi face buƙatar kashe mata aure domin ya aure ta."
Maganar shi nan take ta saka idona rufewa, ta yadda ban san lokacin da na yi wuf na faɗa ɗakin ba. Cikin ƙunar zuciya na fara nuna shi da hannu ina cewa,
"Kai dai baƙin munafuki ne ƙarshen bugun lamba. To wallahi ko za ka mutu ba zan fasa zuwa aik..."
"Yi mana shiru Zaituna!" Babu shiri na gantsara saboda tsawar Baba Sale da carbin da ya watsa mini a jiki, na durƙushe ƙasa ina sosa wurin tare da aika wa Mukhtar harara ta gefen ido. Kafin Baba Sale ya ci gaba da magana cikin fushi tamkar ya dake ni.
"Me ya kawo ki nan balle ki saka mana baki? Ko kin ji an kira ki da za ki zo kina yi wa mutane hauka? Wannan rashin mutuncin naki yana daga cikin abin da ke ƙara lalata muku zaman lafi..."
"Wallahi ko a gaban yara haka take yi mini ba ta shayin komai. Na sha faɗa mata duk abin da za ta yi mini zan jure matuƙar ba gaban wasu ko 'ya'yana ba. Domin yanzu silar hakan har yaran sun fara yi da ni a tsakaninsu. Ko yau da safe ina jin Haidar yana faɗin; shi ya gaji da kukan da nake saka Mamarsu, Idan ban bari ba shi ma zai rama mata a kaina. Ka ga a nan ta yi ƙoƙarin cusa musu ƙiyayyata tun kafin su mallaki hanka...'"
"Wannan kuma ba laifinta ba ne kai ka janyo. Don a irin halinka babu abin da 'ya'yanku ba za su yi ba, matuƙar aka biye doron da kake ajiye tsarin gidanka a kan shi. Yana da kyau ka fahimci matsalar taki ce duka ba ta mutum guda ba, yadda kake da laifi ita ma tana da shi. Don haka ku taru ku gyara dukanku ko don tarbiyyar yaranku. Ke kuma ki ji tsoron Allah ki daina cin zarafin mijinki don komai lalacewar shi miji miji ne, kuma yana sama da ke ko babu auratayya balle aure ya haɗa da 'ya'ya a tsakani."
Zancen Mukhtar da Ummata kenan a lokacin da ya so goga mini laifi, ta yi hanzarin toshe komai ta hanyar ankarad da shi domin ya hankalta.
Daga ni har shi suka rufe mu da faɗa, a kan mu zauna lafiya mu daina raba wa kanmu abin faɗa. Da nufin a bar wanda aka yi baya a matsayin ya wuce a fuskanci gaba, sannan batun aikina ma ba a hana ni zuwa ba kamar yadda yake da buƙata. Sai dai sun tunantar da ni abubuwan da baƙinciki ya sa nake ƙoƙarin aikatawa, ba don na manta da hukuncin laifi ba a musulunce ko a al'ada ba.
Sannan aka tashi zaman sasancin da zummar da dare zan koma gidan shi, bayan an saka ni dole sai da na ba shi haƙuri ba don na so ba.
Ina gunguni na fito ɗakin saboda ko kaɗan hukuncin bai yi wa zuciyata daɗi ba. Domin ni a rayuwata ban da wani buri a lokacin; face ya tsinke igiyon aurensa da suka yi mini mugun ɗaurin talala a jiki. Saboda ina so na kasance free babu aure ko da zan mori sauran rayuwar da ta rage mini a duniya. Domin na yi nagartacciyar ibada irin wadda zan samu natsuwar zuciya, saboda ina so na daina aikata alfashar da nake yi a ƙoƙarin kaucewa zinar zahiri.
Inna Kulu ta dinga ba ni haƙuri domin na rungumi ƙaddarata har zuwa lokacin da Allah zai kawo mini ƙarshenta. Sauraron ta kawai nake yi, amma ba don babu abin da take faɗa mini zai yi tasiri a zuciya ba, matuƙar ba za ta goya mini bayan rabuwa da auren Mukhtar ba.
Ƙarfe huɗu da minti goma na rana, bayan na gama sallar Asr ina kan sallaya da carbi a hannuna ina ja. Na jiyo sallamar Amina a tsakar gidan. Tana tambayar inda nake tare da yi wa su Umma bayanin ni ta zo dubawa, har da yi musu ya jikina suka amsa mata tamkar da gaske ciwon nake yi. Inna Kulu ta fara shigowa ɗakin sannan Amina a bayanta har inda nake zaune.
Murmushi muka yi wa juna ni da Amina sannan ta zauna tana faɗin, "Kai matar nan, ashe ma ciwon da sauƙi MD ya tsorata mu da cewa ciwon ya sa aka dawo da ke gida. Wataƙila ma lamɓo ne kawai gidan kika yi marmari, shi ya sa kika dawo don ki saka su Umma aiki."
Murmushi na yi mata da jajayen idanuwana, waɗanda har lokacin ba su gama washewa ba a kan kukan da na sha. Baki har kunne na ce da ita, "Ciwon kaina ne ya motsa, ban san lokacin da aka kawo ni gidan nan ba. Amma yanzu Alhmdulillah da sauƙi komai ya lafa."
"Allah ya ƙara lafiya, amma ki daina cin abin da ke tayar miki da ulcer, sannan ki dinga shan magani saboda ki samu ta lafa miki ki huta."
"In Sha Allah!"
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.