Trending Hausa Novels

Buzu Book 3 Complete Hausa Novel

Reading file: BUZU BOOK3.txt

Chapter 38 of 99

"Alhamdillah, yanzu da ya dawo ya ka ke ji?"

"Murna nake yi mara misaltuwa, da jin cewa zan iya yin komai, dan na ga bai sake yin nesa da ni bax

Sarkin baka ya ce "Alhamdillah, ka yi bayani dai-dai da abin da nake son ka faɗa. Wannan yarinyar da ɗanka ba za su rayu guri daban-daban ba. Idan haka ta kasance kuma ɗaya zai rayu cikin wahala. Saboda alaƙarsu akwai tasirin soyayyar uba da ɗa a tsakaninsu"

Cikin rashin fahimta Sultan ya kalli Sarkin baka ya ce "Me ka ke nufi?"

"Aljanin da aka yi wa ɗanka asiri da shi, ɗansa ne a kanta yake ta ɗawainiya da ita saboda ta yarda ta yi masa wani aiki. Ya ɗauki tsawon shekaru ba sa tare, kwatsam da aka ba shi aiki a kan ɗanka, ya yo Nigeria da shi, suka haɗu da ita. Dan haka duk abin da zai faru, duk rashin jituwar da ke tsakaninsu, uban ba zai bari ɗansa ya ƙara nesa da shi ba. Saboda shi ne ɗa mafi soyuwa a gare shi"

Sultan ya yi shiru cike da mamaki, yana bin Nana da Hammad da kallo.

Ya ce "To yanzu babu yadda za ayi, a karya sihirin?"

"Ni ba na ƙarya dan a so ni, ban san waye ya yi masa asiri ba, ban kuma san a daidai ina aka yi ba, balle na ce kai tsaye ga gurin a je a tona ba. Kuma ba zan yi karambani ba saboda aljanin shu'umi ne zai iya halaka ni. Amma ita tun da ɗansa yana tare da ita, ban sani ba ko ya samu sassauci ko makarin abin a dalilnta ba"

Sultan ya yi shiru yana kallon su, lallai biri ya yi kama da mutum, duba da yadda lokaci guda take iya sarrafa shi, idan ciwon nan ya tashi.

Sultan ya ce "Yanzu mene ne abin yi?"

"Abin yi ɗaya, a ci gaba da addu'a, kuma ku ƙara taka tsantsan, sannan ban sani ba ko uwar gijiyata za ta nema mana alfarmar shugaba, ko akwai abin da zai iya yi a kan lamarin"
Nana ta É—an tsuke fuska tana mazewa.

"Wa za ta roƙa mana " Sultan ya yi maganar cikin damuwa.

"ÆŠan nasa mana, ai hadiminta ne, kuma babu abin da za ta saka shi, ya kasa yi mata"

Sultan ya kalli Nana ya ce "To ko za ki roƙa mana ɗin, duba da mawuyacin halin da yake shiga idan ciwon ya tashi" Nana ta yi shiru ta sunkuyar da kanta.

Sarkin baka ya ce "Kar a yi gaggwa, a bi ta a sannu tukuna, ta yanke hukunci da kanta"

Sultan ya ce "Shikenan, a mayar da kai masauki, kafin na kuma nemanka"

Nana ta ce "Allah ya baka nasara, dan Allah zan yi magana da shi, idan babu matsala a hakan" Sultan ya ce "Babu damuwa"

Hammad ya haÉ—e rai, amma Nana ta tashi ta bi shi waje.

Ta ce "Sarkin baka, dama kana raye? Ƙaisar ya ce mini kashe ka zai yi"

"Nana Asma'u, uban duƙusa bai kashe ni ba, sai dai na ji jiki kamar ba zan rayu ba. Shi ya kawo mini magani ma, sannan ya ƙara yi mini kashedi sosai a kanki. Daga nan ma har wasu magungunan ya sanar da ni"

Ta ce "Ikon Allah, sarki ya magunguna ya marasa lafiya? Ina Salamatu da wannan aljanar taka"

Ya yi dariya ya ce "Duk su na nan ƙalau"

"To ya aka yi ka san cewa asiri aka yi wa Sayyid?"

Ya harare ta ya ce "Halinki dai yana nan uwar ɗakina. Mutum mai hankali zai yi abin da mijinki yake yi ne? Abin da nake so da ke, ki ƙara addu'a kar ki yarda da kowa, kunnuwanki da idanunki su zama a buɗe komai na iya faruwa idan Allah ya taimake ki wataƙila ya samu lafiya ta hannunki"

Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Ƙaisar ya nuna mini abubuwa da dama, sai dai ba na son gazgatawa ne, na shiga ruɗani, amma har yadda asirin yake na gani, to amma idan ya rabu da Giyaz iya samun lafiya duka?"

"Ba na ce ba, tun da ban san a kan me da me aka ba shi aikin ba. Kuma ba shi da fuskar da zan tambaye shi. Amma ina jakar da na baki?"

Kafin ta amsa, Sayyid ya fizgi hannunta da ƙarfi ya yi gaba da ita.

Bai tsaya da ita ko ina ba, sai da suka je ɗakin da yake jinya. Idanunsa jawur ya ce "Dan wulaƙanci kawai ki je ki tsaya ki na surutun banza da mutumin da ba muharraminki ba"

Ta marairaice ta ce "Haba Shugaba, wa nake da shi a nan daga ƙasarmu, yaushe rabon da na ga wani wanda na sani? Kuma Sarkin baka duk da yana wasu abubuwan da nake tantama a kansu, mutum ne da ba zan taɓa mantawa da shi ba. Bayan tafiyarka daga gidansa, abubuwa da yawa sun faru, ni a gidan nasa a ka bar ni"

"Ba na son jin koma mene ne ya faru" ya yi maganar yana tsuke fuska.

Ta ce "Haba Shugaba, kar ka manta, maganinsa ya taka muhimmiyar rawa lokacin da ka yi rashin lafiya"

Yayi mata shiru yana huci, tabbas a rayuwarsu da shi a Nigeria ta san shi da azabar kishi.

Ta kwantar da murya, tana shafa bayansa ta ce "Haba Shugaba, dama mutum zai iya fushi da rayuwarsa, tuba nake É—an manyan mutane, kuma babban mutum" ÆŠan guntun murmushi ya saki, ita ma ta yi masa murmushin.

Ya ce "Yauwwa, ki yi mini addu'a, in ajima za a sanar da Asal da iyayenta, matsayinki a gurina.

Nana ta kwaɓe baki ta ce "Na yi maka addu'a, ta mutu mana, nima ban mutu ba da kishiyata ta mayar da ni baiwa saboda tana da kuɗi, ga kuma mijina ina kallonsu tare, amma ban isa na ce komai ba".

Tsam ya miƙe, saboda ya san idan aka ci gaba da jan maganar faɗa za su yi. Ya ce "Ki shirya, idan na dawo yau komai dare, za mu je gurin kayan tarihi na Agadez, kuma zan baki labarin duk abubuwan da suka faru"
Ta yi masa shiru ta cika ta yi fam, kamar za ta fashe.

Ya tausasa murya ya ce "Na san kin yi haƙuri, amma ina sake baki haƙuri, dan Allah ki saki fuskarki"

"Ni ka rabu da ni, ka je ku lallaɓa matar so, da al'adarku ta yarda da ita, ni kuma ka sake ni ku kora ni ƙasarmu" Ta yi maganar har da ƙwallar baƙin ciki.

Ya yi murmushi ya ce "Duk wata matar so a bayanki take Gimbiya Ma vie. Kin ci Agadez kin ci Nigeria" ta murguÉ—a masa baki, ya shammace ta ya yi kissing É—in bakinta.

****

Asal ce a gaban Sultan, da Matawalle da Sardauna, ga kuma Tafawa sai Imam Asadullahi, da Imam Hammad sai Mahmoudu.

Matawalle ya ce "Na san za ku yi mamakin dalilin da ya sanya, muka neme ku a yammacin nan, bayan sallar magariba haka.
Mun san za ku ji abin wani banbarakwai, amma mu ma haka nan ya zo mana. Duk ana kan dambarwar É—a da Imam Hammad yake da shi, wani abu ya sake faruwa da dole mu yi muku bayani, domin babu yadda muka iya mu ma, sai dai mu na kan tunanin matakin da za mu É—auka."

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.