Trending Hausa Novels

Buzu Book 3 Complete Hausa Novel

Reading file: BUZU BOOK3.txt

Chapter 63 of 99

Hammad ya shiga ɗakin da Nana take, cike da takaicin yadda ta ce, ita ta haƙura da shi, a bata ɗanta ta koma Nigeria, sai dai ya tarar da ita tana kuka.
Ya kwantar da Muhsin da ya yi bacci, ya ƙarasa gabanta ya ce "Meyafaru kuma ki ke kuka?" Ta yi shiru ta ci gaba da kukan.
"Mene ne?" Ya sake tambayarta.
"Sayyid" Ta kira sunan shi a raunane. Ya zauna a kusa da ita ya ce "Mene ne?" Ya yi maganar yana É—ago ta cikin damuwa.
Ta ƙanƙame shi tana kuka ta ce "Sayyid na faɗi haka ne dan su daina yi maka faɗa, amma ina sonka wallahi Sayyid, dan Allah kar su raba ni da kai" Ta yi maganar tana sheshsheƙar kuka.
Shi ma rungumota ya yi sosai da sosai a jikinsa, yana wata irin ajiyar zuciya.
Da kyar ya tattara nutsuwarsa, ya ce "Ki yi haƙuri Ma vie, Ubangijin da ya haɗa mu ne kaɗai zai raba mu. Ni da ke mutu ka raba in sha Allah"
Zata yi magana suka ji ana bubbuga ƙofar ɗakin, Nana ta motsa za ta tashi, amma ya riƙe ta kuma ya yi umarnin a shigo.
Imam Zahradeen ne ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, kunya duk ta kama Nana.
Ya É—an tsaya yana kallonsu ya ce "Kuka ku ke ne?" Nana ta yi saurin tashi tana share hawayenta ta ce "A'a".

Imam Zahradeen ya ce "Ga idonki nan duk hawaye. Wai  me ki ke gaya masa ne, ya sanya duk ya rikice haka a kanki"
Nana ta sunkuyar da kai tana murmushi.
Imam Hammad ya ce "Komai ma gaya mini take yi, shiyasa nake jin tamkar raba ni da ita, raba ni da rayuwata ne"

Zahradeen ya jinjina kai ya ce "Na ga alama ai. Amma dan Allah ku kwantar da hankalinku, ku ci gaba da addu'a, in Allah ya yarda a dalilinki za a sauya tsarin wasu dokokin na Agadez. Yanzu dai Muhsin zan É—auka zamu tafi"
Cikin marairaicewa Nana ta ce "Dan Allah ka bar mini shi a nan" Ta yi maganar tana kallon Imam Zahradeen.
Ya girgiza kai ya ce "A'a barinsa a nan babu tsaro, tsawon lokacin nan yana tare da ni a can gidana, gobe in Allah ya kaimu za a kawo masa maman Mahmoudu. Idan kuma ba a yarda da ni ba, na bar ku abinku"
Nana ta ce "A'a amma dan Allah ka tafi da ni, ina son na zauna tare da shi, kuma na ga Nene."
"Wani irin mugun kallo Hammad ya yi mata"
Zahradeen ya ce "Ai ko ba ki ce komai ba, dole za ki bar gidan nan, taso mu tafi"

Hammad ya ce "Ya haka? Ku tafi ku je ina? Kuma yaya zaka tafi da ita Sultan bai sani ba?"

Imam Zahradeen ya ce "Idan zaka biyo mu ne taso"
Nana kuwa ta yinƙura ta tashi ta ɗauki jakar kayanta dama da hijjabi a jikinta.

Hammad ya miƙe ya ce "Wai bin nasa za ki yi?"

"Ni ba na son zama a nan, na gaji" Nana ta furta tana tura baki.

Imam Zahradeen ya É—auki Muhsin, ya kalli Imam Hammad ya ce "ÆŠaukko mata jakarta"

Zahradeen yana fita, Hammad ya riƙe ta ya ce "Dan me zaki ce za ki bi shi? Meye haka ki ke yi ne?"

"Amma Sayyid na ga yayanka ne fa"

"Ko ma wane ne, dan me za ki bi shi?"

Ta girgiza kai idanunta na cika da hawaye "Ni na gaji da zaman gurin nan? Ni gaba É—aya ma tsoro nake ji"

Sayyid ya ce "Muje kar ki yi mini kuka" Ya saka Nana a gaba, suka bi ta baya, sai ga su a harabar gidan. Zahradeen har ya kwantar da Muhsin a cikin motar.

Hammad ya buÉ—e wa Nana bayan motar, sai hararta yake yi, amma ta basar ta shige cikin motar ta kawar da kai. Haka nan take jin kamar ta fito daga kurku sai wani irin farinciki take ji da nishaÉ—i, a haka ya bar gidan da Nana a cikin motar.

Tafawa kuwa ya ɗauki zafi, ya ci gaba da ziga 'yan majalisar Sultan a kan lallai su sanya ido a hukunta Hamma, sannan ya yi baƙin cikin fito da zoben nan da aka yi.

Matar Imam Zahradeen ita ma haka take kyakykyawar gaske, fara sol da ita, yaransu huɗu, kyawawa su ma. Sai dai Nana ta ga matar ba ta ƙyamace ta ba, ta rungume Nana tana faɗin yau ga Umman Muhsin, baƙar Gimbiya ta farko a kaf faɗin Agadez.
Nana dai ta kasa sakin jiki da matar, dan duk mutanen Agadez É—in tsoro suke bata, kusan kowa ba abin yarda ba ne.
Ganin Nana ba ta sake da ita ba, ya sanya ta bar ta a É—akin da aka sauke ta.

Washegari da sassafe Hammad ya tafi gidan Imam Zahradeen. Zahradeen ya ce ba zai gansu ba sai bayan Azahar, tun da shi ba shi da kara.
Nana tare da Muhsin suka kwana, kasa baccin kirki ta yi ta rungume shi, cikin farin ciki tana shafa shi. Aka kawo mata lafiyayyen Abinci, matar Imam Zahradeen ta kawo mata kaya masu kyau, ta ce ta saka.
Hammad ya din ga yi wa Imam Zahradeen magiya.
Zahradeen ya ce "Ka ga ba fa magana ake ta kai shugabana ne ba, yanzu muna magana ne a matsayin ya da ƙani, dan haka dole ka jira.
Sai da aka yi azahar É—in, suka yi salla, sai ga Mahmoudu tare da Nene.
Hammad suka gaisa da Nene cikin girmamawa.
Sai dai shigowar su Nene babu daÉ—ewa, sai ga Sule shi ma ya zo, tare da wani matashin saurayi.
Mamaki ya kama Mahmoudu, ganin Sule ya zo gidan, sai dai ya yi ta yi wa matashin kallon sani.

Imam Zahradeen ya kalli Hammad ya ce "Ka san wannan?" Ya yi maganar yana nuna masa matashin.
Ya yi shiru yana tsare shi da ido, ya ce "Na san shi, amma na manta a ina, na san dai na taɓa ganinsa"

Imam Zahradeen ya kira wayar matarsa, ya ce ta zo da Nana.

Wani irin kyau Nana ta yi, ɗinki ne na buzaye a jikinta, sai ƙamshin turare take yi ta shigo da sallama. Kasa riƙe farincikinta ta yi, ta nufi Nene da sauri. Sai dai ta yi wani irin wawan burki, bayan yin ido huɗu da matashin saurayin, da girma da kamala suka bayyana a tattare da shi bakinta na rawa ta ce "Imrana!!!"

Wata irin sufa Nana ta yi, ta nufi Imrana a gigice, ta rirriƙe rigarsa tana zaro ido, tana son tabattarwa da gaske shi take gani, ko kuma gizo yake yi mata.
Cikin rikicewa ta ce "Imrana, Imrana kai ne? Imrana dan Allah mafarki nake yi ko kuma kai ne?"
Ya yi murmushi ya rungume ta idanunsa na cika da hawaye ya ce "Ni ne Nana, Imrananki ne"
"Imrana ka tafi ba ka sake nema na ba, ka tafi ka bar ni nikaɗai, Imrana" Toshe mata baki ya yi, a hankali jikinta ya saki ya kuma yi sanyi ƙalau.
Ƙaisar ta hango a bakin teku, yana kallon ruwan, ta ƙarasa inda yake da sauri, ta ce "Ƙaisar kai ne? Ya jikin naka? Ka warke?" Ta yi maganar tana riƙo hannunsa, sai dai maimakon ta ji ta kama tsoka sai ta ji tamkar ta taɓa ƙanƙara wani irin sanyi ƙalau.
Ya dube ta ya ce "Ina taya ki murna"
Ta ce "Murnar me?"

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.