Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 1 of 139

🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

1️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

BISSIMILLAHI RAHAMSNIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI INA GODIYA GA ALLAH DAYA BAN DAMAN FARA WANAN LITTAFIN, UBAGIJI INA ROKON KA YADDA MUKA FARA A SA,A MU KARASA SHI CIKIN FARIN CIKI DA JIN DADIN JUNAN MU.
YAN UWA MASOYANA HAR KULLUN INA MAI KARA BAKU HAKKURI DA KUYI HAKKURI DA ZAMAN TARE ZOMU ZAUNA ZOMU SABA DA FATAN ZAMU FAHINCI JUNA DAKU DON SAI KUN KARA HAKKURI DANI SAMA DA FARKO A YANZU KASANCEWA ZAN HADA TAURA BIYU A BAKI LOKACI GUDA.
BADON KOWA BA NAI HAKA DON KUNE MASOYA NA MASU KAUNATA A KULLUN FARIN CIKIN KU SHINE NAMU DON DA BAZAN KU MUKE RAWA A KODA YAUSHE.
FADA KARWAN DAKE CIKIN LABARIN NAN UBANGIJI YASA MU AN FANA DASHI AKAN MU DA YAYAYEN MU ALLAHUMA AMIN.
DARI UKUNE HAR YANZU BAN KARA BA IDAN KINA SO SAI KU TUNTUBENI A LAYINA DON HAR YANZU DASHI NAKE AMFANI BUT ONLY TEXT DON DA WUYA KIRA YA SHIGO MIN A NAN YANZU.
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MTN KO EIRTEL NAGODE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMIN SHI AMIN.

A hankali take saukowa daga matakalan jirgin jirgin mai tambarin Nigeria Air way daya sauka a filin jirgin malam Aminu kano.
Fuskanta yana saye da bakin glass din ido sai takunkumin dake saye a fuskan nata bayan ta yan samari biyu ne masu tsanin kama suna mara mata baya.
Doguwar rigace baka a jikin ta sai gyalen shi data yafe har zuwa kanta takalman dake kafanta flat ne basu da wani tudu sosai .
Sai handback din hannun ta data riko wanda ba wani babba bane sosai dan madaidaici dashi.
Kallo daya zakai mata ka gane hamshakiyace ita din don siffan shigar da tayi kawai ya isa ya nunama hakan.
Hjy Iyami ke nan matar tsohon Ambasardor din kasar America wanda ya wakilci Nigeria a 1986 zuwa 93 .
A hankali ta runtse idanuwan ta kafin ta bude su ta kara kallon yanayin kasan nata na haihuwa wanda a yanzu ya zama mata abin kallo.
Duk da dadewan da tayi bata a cikin kasan hakan bai hanata ganin wasu abubuwan da ta bari ba a tsawon shekarun data kwashe bata kasan.
Da mamaki irin halin gwauntin kasan ta Nigeria a ranta taci gaba da saukowa a matakalan jirgin sannu a hankali duk da yanayin kasan nata hakan bai hanata son ganin ta dawo kasan ta na gado ta zauna tare da iyalan ta ba.
Easy hajjajo daya daga cikin samarin dake bayan ta ya fada don ganin irin yadda take bin ko ina da kallon mamaki don rashin ganin wani cigaba da da kasan tayi sosai a zuwa nan lokacin data dawo.
Don tun bayan barin mijin ta aiki sai take can da iyalinta dake kararu inda itama take aiki da wani company a can hakan ne ya dauke mata hankali da gida sosai.
Sai yanzu take ganin dacewan dawowa gidan a cikin yan uwa da abokan arzikin su da suka bari badon komai ba sai don tarbiyan yaran ta da jikokin ta dake tasowa yanzu.
Saboda yawan haramtatacen al,adan da yanzu ya mamaye duniya sai take ganin namu tarbiyan na malam bahaushen kamar daban yake da sauran tarbiyan wasu al,umman na duniya a yanzu .
Don shi malam bahaushe yana mayar da al,ada ya zama addini sosai a gareshi balle kuma abinda addini din ya koyar damu.
Duk da lalacewan duniya a yanzu malam bahaushe yayi kokari wurin ingata wasu tarbiyan da su koma kamar addini a garshi wanda yake taimakon al,umma a yanzu.
Hakan yasa ta yanke shawara ba tare da zaunawa ta shawarci kowa daga cikin a halin nata ba a yanzu da take shugaba a gidan ga baki daya.
Ba karamin tashin hankali ta fuskanta ba a gurin yaya da jikokin ta don jin zancen komawa sun gida Nigeria da sukayi.
Wanda hakan yasa ta rufe ido taciwa kowa daga cikin su mutumci kan umurni ta bayar ba rokon su takeyi ba.
Hajiya Iyami bata fada ma kowa ba saida komai ya gama kammala daga banhareta a yadda take son komai yazo mata daidai idan sun dawo.
Gama daga gyaran gida zuwa company da sauran abubuwan rayuwa ta rigada ta kammala komai yadda zai tafi mata idan sun zo ba tare da sun sha wahalan komai ba tunda akwai kudin su ta fitar aka aiwatar masu da komai yadda take bukatan shi.
Har zuwa yanzu da Allah ya nufa sun tataro sun dawo Nigerian da zama inda duk tawagan nata suke ransu a bace don suna ganin ta rabosu da rayuwan inda suka saba dashi yanzu ta kwasosu zuwa kasan da duhun kai da jahilci yayi katutu a ko ina.
Alhamdullahi a bangaren hjy don ta isa da kowa na ahalin nata daga mazan su har matan su babu mai iya musa mata ga bukatan nata idan ta fada.
Haka yasa abin ya kara zuwa mata da sauki sosai don bata samu tangarada a kowan su ba sai gun babban danta koshi ta daga mai kafa saboda irin aikin shi ne a can don shi tun gama karatun shi yake zaune a kasan chaina inda yake aiki tare dasu.
Ta yarda da imanin shi dari bisa dari don ta auna shi taga yana da riko da addinin shi yana kan tarbiyan da suka bashi tun farko.
Wanan dalilin yasa ta yarda ta barshi a can inda yake aikin wanda a yanzu zamuce shine dauke da nauyin komai da kowa na ahalin don iya sarrafa na,uran computer daya iya da wasu fasahana zamani kasan na chaina ta dauke shi yake aiki tare dasu dama wasu company na kere keren zamani.
Motocine a jere a da suka zo daukan su wanda duk gaba daya nasu ne da aka saye da sunanyen kowa a gidan.
Baya bo ba fallasa fuskan hjy iyami a dan sake tana farin cikin ganin yan uwanta dana mijin ta da sukazo filin jirgin don tarbon su.
Aka dan gagaisa a gurguje inda kowa ke son nuna kulawan shi a garesu kamar dai yadda akeyi ga kowani mai hali a cikin zuria,
Bayan shigar su motane inda sai a lokacin ta fata samun natsuwa a hankali ta runtse idanuwanta tana mai tuno da mijin ta marigayi Alh ma,azu ambasado.
Wanda shine dalilin gatansu a yanzu har suka kai hakan ga Allah ya azurta yaran su da ma wasu dake zaune a karkashin inuwan su ta sanadiyar shi.
Saidai ubangiji bai nufi yaga wanan baiwan ta yayan nasa ba a duniya don yanzu shekara kusan goma ke nan da Allah ya karbi rayuwan mijin nata.
Duk da hakan suna zaune a can waje kamar yadda suke zaune tun farko da yake raye rasuwan shi bai sa sun dawo gida ba tun wanan lokacin saboda aikin ta dana yayan ta da sukeyi a can.
Dan tafiya sukayi kasancew nisan kano da kaduna ba wani tazara mai tsawo bane sosai yasa basu kara wani wahala ba sosai.
Duk hjy na cikin halin tunanen irin rayuwan da zasuyi a nan din yanzu cikin yan uwa da abokan arziki a haka suka shigo garin kadunan don ita bata ga wani nisan tafiyan da yaran nata keta faman jan tsukin nisan sa ba .
A nan ma sun samu dandazom yan uwa na kusa da suka cika gidan suna murna da zuwan wanan family din.
Anci ansha an gagaisa tare da tambayan bayan rabo inda yaran nata da duk mazane sai autar ta da matar danta dayayi aure saidai bata yarda ya auri yar can ba yar nan cikin dagi ta aura mashi aka kai mata ita can suke zaune lafiya da ita don iya zama da sarakuwar nata da ta iya.
Tun wanan ranan rayuwa ta koma masu sabo a gidan ga yan uwa na nisa da kusa dasuke zuwa taron su da murnan dawowan su gida lafiya.
Dawowan ta kasan yasa ta dauko diyan yan uwa mijin ta mata biyu ta hada da yarta suke zaune a tare.
Saidai asali ba itace ta dauko su ba sudin ne dai sukaga wurin zama suka zauna a gidan tare dasu.
Hajiya bata nuna komai ba illa kara jan su a jikin da tayi suka zauna a tare da sai yar sister daya suka cike su hudu yan mata a gidan.
Rayuwa na jin dadi da sakewa sukeyi don hjy iyami na tsaye da saka ido ga motsin kowa a gidan.
Saidai ta fanin karatu da jin dadin rayuwa a cikin gida duk abinda suke so a ransu tana ganin ta kawar masu da shi don kawai kada su gani ga wani har su saka rai sukai ga dauko mata magana.
Ta farko itace salma yar gurin kanin mijin nata dake kula da duk wani al,amarin su daya shafi gida don shi suke sakawa a gaba tankar maigidan nata yana raye don mutumin yana da fahinta dakuma biyayya daya dace.
Sai Rufaida diyar autar su maigidan nata dake aure a jos a can suke zaune da mijin ta da yaranta Rufaidace yarta ta biyu itama dawowan hjy nan kasan .
Daga zuwa da sunan hutu tun lokacin bata koma ba take zaune tare dasu don jin dadin irin rayuwan da ake a gidan.
Sai ta uku jamila ke nan diyar autan su hjy da ita kanta hjy ta dauko ta don ta sahalewa yar uwan nata nauyin yaran da suke a gaban ta zata debe mata wani kewan itama a matsayinta na yar yar, uwan haihuta.
Tankar yar cikin ta take ganin ta a wurin ta don hakan ta daukesu gaba dayan su tankar diyan data haifa a cikin ta suma ba laifi a nasu bangaren hakan suke kokarin nuna mata kamar yadda itama din take kokarin nuna masu duk daya suke a wurin ta.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.