Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 95 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWALITTAFIN KUDINE YAR UWA DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA PLEASE, , , , , , .
Duk da gakiyan data shana hanya hakan bai hanata shiryawa don zuwa garin zaria ba don da ba wani lalura a gabanta yadda tayi wanan tafiya da tana kwance a wanan lokacin tana hutawa.
Saidai wanan tafiyan yasha bambam da sauran tafiyan data sabayi a kullun don tafiyane na bashiri da ya risketa zuwa zaria din unguwar kusfa.
Gidan wani dadtijo data samu labarin shi a wurin sharan aikin sosai kamar yankar yuka don da wuya yayi aiki ba ai nasara ba akace.
Shine dalilin daya tayar da mami tazo kaduna cikin gagawa don hankalinta a tashe yake har wanan lokacin da tazo kaduna din.
Duk da mutanen da suka cika mata gida hakan bai hanata fita zuwa inda tayi niyar zuwa ba saidai wanan tafiyan daga ita sai yayan ta zasuyi shi bata yarda kowa ya bita cikin makarabanta ba don tafitane na shiri zasuyi kan abinda ya shafi rayuwanta da iyalin ta.
Haka ta fito tana ba mutane hakkuri uzuri ya kamata zata tafi unguwa sai ta dawo zata gansu kafin ta wuce.
Dole kowa ya hakkuru sai kalilan daga cikin danginta yan naci suka tsaya don akwai abinci da abin sha wadattace da aka girka don zuwan nasu.
Nan suka zauna a cikin radhin damuwa suna ci da sha da raha a tsakanin su masu kyashin juna kuma daga cikin su sunayi kamar yadda ake samun hakan a ko wani gidan mai akwai idan mutanen sa sun taru.
Tafiya sukayi na dan lokaci tsakanin kaduna da zaria sai gasu garin zaria din da bin kwatance har suka gano gidan malamin da dama yasan da zuwan su garin.
Basu tsaya wani bin layi ba don sha,anine na kudi akai masu iso suka shiga inda yake ganawa da mutanen sa.
Tare take da ya mamud sai jamal dasu kawai tayi wanan tafiyan don ko jalal da Aisha basu san abinda ke faruwa ba har wanan lokacin.
Bayan dan bayanin daya biyo baya yayi shiru kamar yana nazari a cikin ranshi yana kallon kasan da ke gaban shi zube a cikin wani katon katako.
Ga tasbaha a dayan hannun shi yana wani irin ja a cikin sauri yana kada kai suna gefe zaune sun kura ma abinda yakeyi idanu.
A sanyayye ya dago kai yana fadin lalai kunzo da babban al,amari mai wuyan sha,ani don gaskiya abinda nagani abune mai wuyan magancewa da sauri.
Saidai shi addua da sadaka baibar komai ba don duk yadda abu yake wanan suna rage karfin abu don ba abinda ya gagari ubangiji balle an hada da addu,a ga sadaka.
Musamman ke uwa kece ya kamata ki dage a wurin nemawa wanan yaron mafita daga fitutunun nan na duniya da suka taru sukai mai yawa a kanshi.
A yanzu mu maluma mun daina fadan sanadin abu don irin rigiman da abinda muka gani yake haifarwa daga baya.
Saidai wani hanzari ba gudu ba a wanan zancen ga wata yarinya dake tsaye fiye da kowa ga wanan zancen yar fara mara jiki sosai .
Don tafi kowa shiga damuwa da kuma yawaita yin addua a kullun kan wanan dan naki wanda a yanzu ma kiris take da samuwan warakan wanan al,amarin .
Saidai akwai dan tsaiko da wasi wasin yin hakan a zuciyar ta amma dai bari mu gani ya kara share kasan dake gaban shi yana dan wani tabe tabe a cikin kasan kafin ya nisa yace.
Bari dai mu gwada wanan dinbdon zan iya cewa ba tabbas a cikin lamarin yarinyar a yanzu don haka akwai yadda za ayi aike yaje gareshi..
Allah gafarta malam bamu dade da dawowa can kasan ba duk bamufi sati daya da dawo ba wurinsa yanzu.
Zaiyi wuya yanzu wani ya koma can din tunda har kasan chaina yake zaune tare da iyalin shi.
Tsohon yace na,am to idan har hakane yanzu sai dai aiyi aiki mai kama da aike a gurin shi zan baki addu,oi da zaki dinga yima safe da marance .
Zaifi kyau ace yasha wani abu daga cikin abinda zamu hada mai ya shiga cikin sa don ya ratsa jikin sa.
Ya mamud ya karbe da fadin malam zaizo nan kasan saidai ba lokaci amma munyi dashi zaizo ba dada dadewa ba in Allah ya yarda.
To duk lokacin da yazo din zaku iya kawo shi nan don akwai maganan da nake son muyi dashi ido da ido dashi.
Nan dai ya basu abinda zai basu suka fito suna godiya har lokacin ran mami ba dadi don ita tafi son ayi aikin gagawa wanda zai dakatar mata da dan nata daga aikata duk wani abin alfasha.
Ga tsohon kamar yana da magana a bakin shi don yace ba zai fada mata dalilin shigan dan nata wanan halin ba yayi mata magana ta baibai data kasa fahinta sai juya zancen take a cikin ranta har suka shigo garin kaduna.
Ta samu gidan nata a cike da mutane kamar yadda ta barsu kan ta tafi yanzu ma haka ta samu gidan saidai yau yan zuwa wurin nata sam basu ganewa hjyn tasu ba don fuskanta babu walwala.
Haka take amsa masu gaisuwan su tana wucewa don jin kanta takeyi kamar ba ita bace saboda damuwa da yayi mata yawa sosai a lokacin.
Saidai ganin anty Safiya tare da yar uwanta yasa ta dan ja ta tsaya tana fadin Safiya ina kika shige kwana biyu bamu haduwa ?
Jin hakan da gani da anty safiya tayi mami tayi mata magana cikin sakin fuska da hahaba a cikin mutane wanda rabon data samu ganin sakin fuskan mami wurin ta tun faruwan rikicin auren mu da jafar ta daina sake masu fuska haka yasa mijin ta cewa ai ba dole bane ta rabu da ita mana idan ta sauya mata.
Basu daddara ba yanzu ma suka zo yi mata sannu da zuwa don kawai wai tana gaba dasu suke mata biyayya a cewan su.
Don mami ta kasace mace ce mai yawan aikata alheri shiyasa ake yawan zuwa wurinta da zaran anji tana gari har wanda bata sani ba suna zuwa da koken su.
Har ta wuce kowa sai kuma ta juyo don ganin anty safiya da hannu ta nunata tana fadin ke wai kina kasan nan dama.
Ba anty safiya ba kowa dake wurin yayi makmakin hanka a yadda ta shigo bata kula kowa ba sai ganin anty din ta dan ja ta tsaya.
Ita ko anty safiya mamakine ya kamata sosai ganin yau yadda ta tsaya ta kulata a bainan jama,a sabani tun lokacin auren mu da ya jafar data tsani kowa nawa harda anty din data kawoni wurin ta.
Tana ganin itace sanadin komai a lokacin yasa ta rufe da ita gaba daya wullakanci iri iri sun sha shi wirin mami har suka gaji suka dauke kafansu a wurinta.
Yanzu dai di sunzo ne don cewa da akayi bata da lafiya tunda ta dawo chaina gashi kuma tazo garin kaduna sukace bari suzo su gaida ita kunsan abu ga maishi.
Da hannu ta yafutu ta tana ci gaba da tafiya da sauri anty din ta mike tabi bayan mami din suka shiga part din ta tare.
Safiya kin dauke kafan ki ko nazo garin nan yanzu baki zuwa ko wani abin ne ya faru tana zama take fadan hakan tare da cire gyalen data yafa a jikinta lokacin.
Anty safiya tace bawai hakana bane aiko ina zuwa wani lokaci dai bama ganin kine ko munzo.
Ok ta fada tana daukan wayan ta tace Ramatu akawo min abinci mana su mamud ma na part din shi akai masu nasu ta dago bayan ta aje wayan tana fadin.
Diyarki ce ko kanwar ki tana can yanzu idan kinganta ai ba zaki ganeta ba ma don gaba daya ta canza wallahi .
Ikon Allah suna dai lafiya anty ta fada tana gudun ta fadi wani magana tayi baranbarama a gaban mami din.
Mami ta amsa a kasalance lafiya kalau halan baku waya da itane yanzu ta fada tana dago ido don kallon anty din .
Ina ganin bata da layina nima haka don tunda suka tafi bamuyi waya ba gaskiya don yadda na falfale ta akan auren kamar yadda kika umurceni in mata din.
Kai ai komai ya wuce yanzu suna can zaune kalau abinsu sai karatun da takeyi tana gab da gamawa yanzu haka da munzo tare ai taga gida don sun dade basu zo gida ba, har kanwarta da suke tare a can.
Au da yarinyar ta tafi ashe gaskiya jafar yayi kokari sosai Allah dai ya saka da alherin sa don ba karamin kokari yayi ba yin hakan.
Aka toro kofan mai abinci ta shigo da abincin mama Ramatu na biye da ita a baya suka sauke abincin saman dan table din dake karamin falon.
Tare aka zuba masu da anty sai wani kallo mama Ramatu ke bin anty Safiya dashi duk da tagani bata damu da hakan ba.
Kowa yayi mamakin jin a ranan zasu koma ashe karfe nakwai na dare saida ta gana da wasu daga cikin jama,an wasu kuma aka basu hakuri sai gaba.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.