Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 135 of 139

ZAINABASSALAMU ALAIKUM JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI ALHERIN DAKE CIKIN RANAN NAN ALLAH YA SADAMU DASHI.

INAWA YAN UWA TUNI GA YAWAITA ADDU,A A WANAN RANAN ALLAH UBANGIJI YASA MU DACE AMIN, , , , ,

Mun idar da sallah kowa na saman sallaya a zaune yana addu,a kafin mami ta shafa ta juyo tana bin dakin da kallo ta ko ina kafin muryan ta ya biyo baya tana fadin.
Zainab nasan zakiyi mamakin ganin saukowa na haka da sauri cikin dan lokacin da bakiyi tsamanin hakan ba ko ?
Kallon ta kawai nayi duk da gabana yana faduwa daga yanayin da take kallona din hakan baisa na katse addu,an da nakeyi ba a lokacin .
Saidai kawai kan dana kadawa mami din a lokacin alaman naji taci gaba da fadin kada ki dauki hakan wani dama a gareki yanzu da zaki ga kin kai wani ko kinfi wani ne a yanzu a gida na zainab.
Kada wanan dama ya saki dauka na manta me kukai min a baya duk ina fada maki wanan zancen ne ki san matsayin ki a cikin mu.
Don ban shirya dana ya ma zauna zaman aure dake ba balle a kaiga haifan jikokin da basu da usulin da nake so.
A raina nace ashe shiyasa kika aurowa ya mamud Nuriya take garaku yadda take so itin hakan kike so ke ko ?
Ganin na fara shiga dogon nazarin kan zancen dake fita a bakinta din ko ina mamakin abinda take fada min din yasa taci gaba da fadin kwarai zainab.
Na sani kin yi kokari kan jafar din fine dama ai duk mace da take hasashen wani abu dolene ta dage ga abinda take so har ta cinma burin ta.
Bance bakiyi kokari ba kamar yadda ya fada kinyi kokari kowa ya sani amma wanan bashine dama a gareki ba.
Allah ya gani ba irin ki nake so da dana ba zainab nafida son diyana su auro min wa yanda ke da asali don hakane ma bani kaunan ki hada shimfida da jafar a yanzu.
Wani kallon mamaki nayiwa mami din har lokacin ban samu bakin magana a gare ta ba don mamaki tace kwarai kuwa zainab don.
Kin fi kowa sanin son da nakewa jafar cikin diyan dana haifa kuma nake dasu a yanzu a duniya.
So da kaunan da nakewa danane yasa na nuna a gaban kowa komai ya wuce a wurina har na gane kurena don gudun halin da zai sake fadawa nan gaba kan hakan, shiyasa na daure nayi hakan don fitar shi cikin halaka.
Wanda nasan bani kadaine wanan abin zai shafa ba a yanzu har ke da kike kirarin matarsa ce ke, don Allah kadai yasan abinda kikawa jafar a yanzu yake mutuwar a gareki haka.
Murmushi na sake a nan, don na kasa hade maganan da take fada min a lokacin nace mami ke nan nasan da wanan nasan kuma hakan kafin ki furta a yanzu din don tun a gidan ki na hango hakan a idon ki.
Sai dai saukin abin ni Allah bai dora min son daki ba tun farko a zuciyana don har yanzu kallon kyama nake masa ga irin abubuwan sabon daya aikata a baya.
Ba wata mace ko uwa da zata so a danganta da mai itin wanan bakin fasadin a duniyan nan yanzu.
Kuma kada ki manta cewa ko lalacewan tashi ta farko banice sanadin shi ba a haka na sameshi da abinshi kuna tare dashi hakan na zauna a kyamace dashi ?
Don me kuma a yanzu zan jefashi cikin wani rayuwa bayan nina san irin wahalan da nasha a baya don naga ya dawo mutum kamar kowa abin alfahari a yanzu ga wasu.
Sai dai kuma mami a yanzun wanan maganan naki ya haska min idona sosai kan daki din yanzu na gano manufarki ga hakan a kan danki don haka.
Ni a yanzu har na fiki son jafar don ga alama nina fiki sanin zafin shi a yanzu don jafar mijina ne ke kuma danki.
Kinga ma,ana nan ina nufin koda yaushe ina tare da jafar ke kuma uwace sai lokacin daya tuna dake yaje gareni kinga na fiki damuwa da damuwan danki.
Ido tas ba kunya nake fada mata wanan maganan da umma ta tsara min in fada mata idan bukatan hakan ya taso don mami tasan yanzu ba da bane a wurina.
Ko zan samu saukin irin hattarana da suke nuna min ita da diyan ta mata da bansan abinda nayi masu ba har yanzu.
Zainab ni zaki kalli idona ki fada min magana irin wanan haka a gabana ashe dama karyan yi min biyayya kike a gaban mutane kike nuna hakan ?
Lah mami bana karya ko a kan gaskiyana sai dai maganan ya dangaci hakane a yanzu a da ina tunanen barin danki din don kwanciyan hakanlin ki gareni.
Amma yanzu na gane kurena a kan hakan ko aure nawa nafita nayi dole a saka sunan jafar a na farko a cikin mazajen dana aura a duniyan nan.
Don haka barin shi ma bai taso a gareni ba kamar yadda kike son in barshi din ki auro masa wata wace kike ganin itace ta dace dashi a yanzu din bani da banda asali ba kamar yadda kika fada yanzj.
Don haka zama da jafar yanzu na fara tunda mijina naso na bai damu da koni wacece ba ya gani yasoni a hakan da wani manufa da a yanzu ya zama muna alheri ga baki daya mu.
Idan asiri nayiwa jafar har yake sona sai nake ganin ai banice farau wurin yin hakan ba aga yar kauye a aureta ta zama wani abu a duniyan nan.
Ta joyo a hasale zata kai min duka aka budo kofan shine a tsaye a yadda ya gamu ya tsaye rike da kofan a hannun shi yana raba idanu a tsakanin mu
Kafin na wayance da fadin mami kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zan sake ba kuma nayi maki alkawarin komai zai kara daidaita a tsakanin mu insha Allahu.
Na fada a dan maraice kamar ina ladabi kan wani zance data fada ya bata min rai a lokacin ya karaso cikin dakin yana fadin .
Mami is ok ai ku tafi gida kawai zamu zauna mu sasanta kan mu zainab me hakkuri ce da yafiya wanan zance ya wuce a yanzu ai.
Nace don Allah ya jafar ka tayani bawa mami hakkuri bisa abinda nayi a dazun ya bata mata rai ba zan sake kuskure irin wanan ba insha Allahu.
Don't mind with that mami ba zatai fushi dake ba zainab tunda kina son mu da zuciya daya kina kuma zaune damu a cikin amana.
Da ba don ke bace a gidan da yanzu yar leken asirin gidan nan ta gama kai rahotona zuwaga magabatan ta ko, akan abinda tazo nema game dani a gidan nan.
Sai Allah ya taimakeni zainab din ba mai yawan surutu bane haka don haka bana tsamanin ta samu abinda take son samu a wurina a yanzu.
Sabon zance ke nan kuma a yanzu mami takeji daga bakin shi akan fadila, a cikin rawan jiki mami din ke tambayan shi wai wata yar aiki dai yace wanan dai da take zaune damu a gidan nan.
Yar sandan ciki ce ita an turota ne gidan nan ta zauna damu duk tsawon shekarun tana bincike ne a kan mu haka.
Labarin da sirin mutum wani lokaci akan sameshi ga matar ga matar mutumce mami sai ya kasance zainab din bata fadawa kowa sirin takeyi ba har nawa din bata hiran hakan da bakuwar fuska.
Innalillahi ya akayi kuke zaune da yar leken asiri a cikin gidan nan me take nema a wurin ka har tazo ta zauna maka a gida hakan nan tana maka zagon kasa.
Aiki tazoyi a kaina bata san mun gane hakan ba zaune kawai muke da ita me zata fada mami tunda bataga abinda tazo bincike ba a kaina din.
An turotane tayi bincike a kaina, don su gano irin abinda nakeyi nake samun kudin da suke gani nake dashi don su a zaton su ina wani smogling din wani abu da gwaunati bata son a shigo dashine a kasan nan.
Ko ina kaiwa wani kasan abinda suke tuhuma ke nan suka turo min ita a maysayin yar aiki a gidan nan take zaune tare damu.
Mami me zata fada tunda bata gani ba ni wanan abin baya damuna ko kadan kawai dai ta gama zaman ta ta kara gaba.
Mami ta amsa da fadin dama na sani wanan matar munufukace tun farko sam batayi min ba rayuwan ta yana nuna ta faye wayewa da yawa.
Tun da naga kansu hade da matar ka nake tsoron wanan matar wallahi ashe hasashena ya zama gaskiya a kanta.
Kai mami don kawai tana gidan nan ne kike ganin su da zainab din amma ai zainab ba halinta magana haka ba.
Zainab din ma idan mun koma karatu zata fara kuma zata fara aiki da mun koma din zakiyi alfari da wanan sarakuwan naki nan gaba kadan insha Allahu.
Karatu ni ba karatune a gabana ba in daiga kun fara haihuwa a tsakanin ku in samu jikoki irin su ihisan daga tsatson ka.
Kai ya fara sosawa yana dan murmushi tare da fadin with time mami zasuzo har sai kin gaji da dauka.
Ya juya zancen mami din ya juyo dashi dashi da tace wanan matar taka ai ba haihuwan take so ba ita sai dai idan da wata matar zaka haihu jin hakan yasa ya juyo da sauri yana kallon ta a cikin mamaki.
Mami wanan maganan fa inma zolayan zainab kikeyi ki daina don Allah kada kisa hankalinta ya tashi a yanzu
A kan wanan zancen hankalina zai tashi sam wallahi na fada ina dan murmushi naci gaba da fadin ai bazan so in kasance cikin irin mata dake tauyewa mazajen su hakkin ba.
Su hanasu aure alhalin suna son karawa auren a zuciyan su ni alfahari zanyi da hakan ba nuna bakin ciki ba .
Kaida Allah ya bawa ikon yin hudu a lokaci daya don me zanyi bakin ciki don za a kara maka aure a yanzu .
Abin alfahari ne a gareni yanzu idan zaka kara din aini ban son zama kamar laya a wuya.
Na mike na bar inda nake tun idar da sallah mu din zuwa bakin gado ina daukan wayana dake aje a kunne ina recording din zancen mu da mami a ciki.
Mami muje ko ya fada haka ya dawo da ita cikin tunanen jin zafin maganan dana saka mata din don itama ai hana mijin ta kara aure tayi a lokacin.
Rai bace mami tafito a dakin duk da kokarin da takeyi na wayace hakan a fuskan ta sai haka bai yuyu ba a lokacin.
Gaki mana ranki a bace kika fito hjy dake kallonta ta fada tace ba komai hjy gajiyene kawai .
Har kofa muka kaisu na dawo tare da hjy mun dan zauna kafin in mike zuwa dakina na shiga na sake alwala nayi sallah.
A wirin na zauna na dauko wayana na kira layin umman su Nafisa na kwshe duk yadda mukayi na fada mata.
Umma tace dama na fada maki ban yarda da nadamar wanan matar ba a lokaci daya haka tace wai ta sauko.
Tayi hakan ne kawai don ta batarwa mutane da hankali ke kuma ta jefaki a cikin damuwa yanzu sai ki zage sosai ki bi mijin ki ki kara kwantar da hankalin ki a kan auren ki.
Bayan mun gama waya da umma Nafisa ta karba ta bar wurin tana fadin yau kin min daidai kan matar nan wallahi wai me take nufi dake ne zainab ?
Nace koma me take nufi ai yanzu ya saura gareta tace tunda ta nuna hakan wallahi yanzu ki shirya ma zamakin sosai kada ki tafi baki shiryawa zaman ki ba don zata iya yi maki komai a duniyan nan tunda bata kaunar ki dai a ranta yanzu.
Dama tasone ta more maki kawai suci moriyan ki karshe ta hadaki da yan aikin gidan ta aure taci gaba da more maki ko yaushe.
Sai Allah ya fitar dake ya dora ki saman ta da bata taba zaton hakan ba a rayuwan ta ai dole ta yi bakin ciki dake yanzu .
Don alama ya nuna duk cikin diyan ta mijin ki tafi so a rayuwan ta fiye da yan uwan shi .
Allah zainab ki tari mijin ki a yanzu kuma kija hankalin shi sosai tunda kinsan ba sabawa yayi dayin hakan ba kila sai kin koya mai a yanzu.
Nace cikin harara kamar tana ganina a lokacin nake fadin akace maki ni din na iya ko ?
Ko baki iya ba dai kedin mace ce ai don haka sai ki koya kawai daga yanzu zan turo maki wani wa,azi na abubuwa ki saurara sai ki fara daga yau zanyi magana naji ta kashe wayan tana dariya.
Ba a dade ba naji massage suna shigo min na duba itace ke fadin ki bude ki saurara na turo maki sakon Allah bada sa,a sauraren in samu lada ga hakan nima.
Tsuki nayi na jefar da wayan na shiga wanka bayan na fito ne wayan yana ringin na dauka sa,adatu ce a layin take fadin inna ce tace yau baki kira ba tun safe ko lafiya in kira mata ke taba inna muka gaisa tare da tambayan lafiyan su.
Muka dan taba hira kafin taba kannena wayan muka gaisa dasu kowa na fada min abinda yake so in sayo mai idan zanzo sallaman su .
Na kashe wayan ne har zan aje saina tuna da zancen sakon Nafisa hakan yasa na kunna data na na shiga sakon na fara saurare ina shafa mai ajikina lokacin dare ya somayi har goma da rabi yayi gashi ban ko ci abinci ba a lokacin.
Ashe shima rashin fitana ya hanashi cin abincin sai gashi dakin ya shigo a daidai lokacin ina kashe wayan dana saurari wa,azin a ciki.
Zama yayi a bakin gado ina saka rigan dana dako saida na gama yake fadin me kika fadawa mami dazun daga maganan wasa kika sake mata magana haka ?
Amma kinsan mami ita kadaice gun mahaifin mu ai zata dauka da ita kike wanan maganan ai jin hakan sai nayi murmushi ina fadin.
Ba zan taba fadawa mami maganan da zai bata mata raiba don mahaifiya take a gareni saida wani dalilin yasa kaji na fadi hakan a yanzu ma.
Oudio wayana ne ya soma magana ya dago kanshi da sauri tare da juyowa a inda nake tsaye yana sauraren zancen mu da mami na dazun din.
What ya fada har ya mike ya koma ya zauna tare da dafe kanshi na dan wani lokaci ina tsaye na hade hannaye a wuri daya ina kallon shi.
Tare da fadin tsamanin hakan yasa na danna wayana ya dauki komai don sheda a gareni duk da hakan ba wai haka na nufin raini ko wani abu zai shiga tsakani mu bane da mami.
Har kayi tunanen na fada mata maganan da zai bata mata rai dani bayan an shirya mu a yanzu di nida ita.
Kawai na fadi hakan ne don abinda nima take tunanen yi a gareni don haka a yanzu ka barni don Allah in koma gidan mu don ka shirya da mahaifiyar ka a zauna lafiya.
Koyin hakan zai kawo maku kwanciyan hankali a tsakanin ku daga fadin hakan naja bakina nayi shiru tare da zuba mashi ido.
Sai kawai naga ya mike zubur ya fita daga dakin ya barni nan a tsaye ina binshi da kallo kafin in fada saman gado don takaici.
Nakai minti talatin a hakan ina sakawa ina warware a zuciyana kafin in mike zubur na shirya duk wani shiri da zanyi najawo kofan dakina na saka masa key na fita zuwa part din shi kai tsaye.
Yana kwance saman gadon kamar yadda ya saba idan yana cikin yanayin damuwa har na rufo kofan na karaso bakin gadon bai motsa ba.
A hankali na kai zaune ba tare da nayi mai magana ba ina karatun addu,oin kwaciya na gama na kai kwance a gefe shi da dan nisa a tsakanin mu .
Ranan tuesday in Allaj ya kaimu zamu koma don haka ku fara shirin tafiyan mu ya fada ba tare daya motsa din ba.
Na fada ma ba zan zauna ba yaya gidan mu zan koma don mami ta tsaneni har cikin ranta ba zan taba yin haske a zuciyar ta ba.
Idan zaman kanki kikeyi ki koma gida din a yanzu ya fada tare da gyara kwanciyan shi duk a zatona dana shigo zancen mami din zai min kan musayan maganan da muka fadawa junan mu.
A hankali yakai hannun shi ya kashe hasken dake dakin kawai ji nayi ya mirgino ta gefe na ya rungumeni a cikin jikin shi gaba dayan shi ya sakar min nauyin shi yana wani irin ajiyan zuciya.ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA WANAN SAFIYAN ALLAH YA SADAMU DA RAHAMOMIN SA ALLAHUMA AMIN.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.