Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 18 of 139

Tunda muka tunda muka tun karo gifan naga wasu canji a cikin dan kwana hudun da nayi bana garin.
Ni dai sai bin ko ina nake da kallon da mamaki a raina don ganin bakin fuskokin dake gidan namu tun daga get har zuwa cikin gidan.
Na fito daga cikin motar tare da dora hijjabi da kyau a kaina na nufi hanya shiga gida don na tsaya daukan kayana malam usman yace za a shigo min dasu ciki.
Da sallama a bakina na shigo falon sai dai abinda nayi arba dashi ne yasa gabana faduwa don ganin mutane a falon gidan kusan kowa na gidan yana falo ga bakin fuska.
Wa nake gani kamar diyan mami haka muryan mami ya dawo dani daga tunanen dana fara a lokacin.
Da dan gudu na karasa na fada jikin mami data ware min hannayen ta alaman inzo gare ta a lokacin.
Kai kai kai mamana me innar taki ta baki haka cikin kwana biyu kika kara kiba haka kinyi wani fresh dake mami ke fadi.
Tsuki yaya jamal yaja yana fadin ko dai ta kara kauyanci ji wanan bindata saka don Allah da cewa hijjab din jikina wai.
No dan Allah malam usman bace muna da wanan kayan kazantan wurin nan ka shiga dashi wurin kande suna kice cewar Rufaida dake nufin a kauce masu da kayana a wurin.
Malam usman dake shirin aje kayan ya dauka da sauri ya nufi hanyar kitchen dasu na dago ina fadin ban jakkana in kai daki bayan mun gama gaisawa da mami ban kalli kowa a falon ba.
Jeki kai ki fito ki ci abinci wai ai kunsha tafiya don wurin bai kasa ba akwai dan nisa da kaduna.
Shiyasa nace malam usman yayi sakko yaje ya dauko ki don ku dawo da wuri bana son tafiyan dare.
Na dauki kayana zan shige naji muryar yaya jalal na fadin baki iya gaisuwa bane ke idan kin samu mutane ?
Ke tafi ki aje kayan daki ki dawo mami tace haka yasa ban tsaya sauraren shi ba don bin umurnin mami din.
Na kai kayan na dan dade ban fito ba azatona bakin zasu tafi kafin lokacin sai dai har na fito suna nan a inda suke sai lokacin na gaidasu sai dai sun ragewa a fLin don ko su yaya Jamal basa falon yanzu.
Abinci na diba kamar yadda mami ta umurce ni na koma dakina ban kara fitowa ba sai dare bayan nayi sallah isha, .
Don na kwanta ina tunanen gida ina tuna innar mu da na dan saba zama da ita a yan kwanakin danayi a can gida sai nake ji kewan su na damuna yanzu.
Hjy na samu a falo kishigide saman kujera sai wani matashi dake zaune kasan kafet dake tsakiyan falo.
Ya mike kafafuwan shi sambala sabala tare da dora daya saman daya kanshi yana daidai cinyar hajiya.
Suna hira a cikin natsuwa su biyune kadai a falon, kowa yagan su zasu bashi sha, awa alokacin.
Ni dai kallo daya na iya masu na kawar da idona garesu don kyawon mutumin da kwarjini ga zati da Allah yai mashi kamar shiyayi kanshi.
Da ina ganin kyawon su yaya jamal kamar su sukai kansu gasu da iya kwalliya da tsabta shiyasa zaginsu gareni bai damuna da sukece min yar kauye amma sai ganin wanan ya dushe duk kyaun da suke dashi a idona yanzu.
Zeey ga yayan ku yayan su jamal jiya yazo sai kanwarshi da tazo ranan da kika tafi.
Sannu da zuwa yaya ya hanya nace mai ina dan rusunnawa don bashi girma da Allah ya bashi a kaina.
Fuska a sake ya amsa min gaisuwa bazakace bakin shi na motsi ba yadda yake magana da hausarshi da baya fita da kyau.
Daga haka na mike don barin wurin ina tafiya a harde don rudewa da nayi don ban taba ganin mutum yai min kwarjini irin haka ba a idona.
Muryan mami naji tana fadin zeey dauko ma yayan ki abinci nan yaci yau a kasa yake so ci yace don kiuya.
Taci gaba da fadin ki dauko har dani don nima din kiuyan nake ji sosai in samu inci in shige daki duk na gaji yau munyi yawo sosai yau.
Kulolin abincin dana gani a jere sabbi fil dasu wanda ban taba ganin irin su ba a idona don kyau.
Saida na dauko na karshe zan kawo naji karan bude kofa a part din mu wata matashiyan budurwace ta fito daga dakin dake kusa da nawa tana fadin.
Mami na dauka baku dawo ba har yanzu naga yanzu is aftre eight ashe kun dawo sannun ku da zuwa ta fada fuska a sake.
Mun dawo mami ta bata amsa lokacin da budurwan ke zama kusa da na zaune a kasa tana fadin bros yau kaga kd ke nan ashe ?
Yamutsa fuska yayi yana fadin mami ta kaini gurin yan uwanta dana daddy har na gaji a cikin turanci suke maganan wanda ba ko wani abin nake ganewa ba saboda kwarewan su da yaren.
Ina wuni nace mata da hausa ina durkushe kasa a lokacin lfy ta fada tana kallona kafin ta juya wurin mami tana fadin who is she mami ?
Zainab ke nan da nake fada maki tayi tafiya yarinyar da nake zama da ita yanzu wace gwaggon safiya ta kawo min yar uwar safiya din ce.
Oh itace she look quit ai ba kamar yadda su Rufaida ke fada ba a kanta mami tace rabu da yan rainin wayau kawai ban san me yarinyar nan ta tare masu ba gidan nan.
Mami me za a zuba maki na tambaya sai ta dago tana fadin fara zuba mai shi da baison cin abinci sai shiririta ya saba da abincin su na shirme can.
Lokacin ne na saci kallon shi na fara bude kulolin abincin ina son tambayan shi abinda zan zuba mai kuma ina jin tsoron ko bai iya hausa ba.

ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

1️⃣2️⃣

ALHERIN ALLAH YA CIN MAKU MASOYA A DUK INDA KUKE A FADIN DUNIYAR NAN ALLAHUMA AMIN ALLAH.

LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA DAUKAN NAUYIN HAKKIN WANI A KANKI BA.

Nidai na kula tun dawowana kowa ke walwala ga yawan bakin dake ta zuwa gidan babu wanda zan dan tambaya ko meke faru a gidan haka.
Naga kowa na gidan yazo ga kuma baki daketa zuwa daga ban garori daban daban sai gidan ya cika da baki sosai.
Wurin kande naje ina tambayan ta abinda ke faruwa take fada min ai zancen hjy ne ya tabbata za, a tafi Abuja a rantsar dasu.
Itace a jahar kaduna wace ta samu mukamin sai wasu daga sauran jahohin kasan nan kafin in furta wani abu larai take fadin.
Wai mukamin me hjy ta samu hakane wanan cikar da akeyi gidan nan haka mama kande tace waya sani yar nan su dai suka san abinsu can.
Shigowan anty safiya kitchen din tare da yar uwarta yasa muka katse hiran da mukeyi muka shiga gaidasu da zuwa.
A, a ke yaushe kika dawo me tafiya babu sallama koda yake baki da laifin hjy ta fada min komai daga baya.
Tana magana take karasawa cikin kitchen din tare da fadin kande zamu kawo maki wasu yan aikin da zasu kwana biyu suna aiki tare daku a gidan nan don aiki zai maku yawa ku biyun nan yanzu.
Duk da dai maza da matane zasu zo din ba lalai bane ma ku taba masu aikin su sai dai idan suna nema wani abu zaku iya basu.
Iyakar ku ke da larai shine zaku taimaka muna wurin bawa ko wani bako abinci idan an gama daga na karyawa har zuwa dare.
Ta juya tana fadin ke naji hjy tana neman ki tun dazun ashe kina nan gurin su kande.
Da sauri na mike zuwa wurin kiran da ake min na barsu kitchen din dasu kande tana masu bayani .
Cikan da gidan yayi a lokacin yasa na fara dan rabe rabe har na isa wurin hjy din dake dakin ta tare da wasu jiga jigan mata farare tas kamar ta sai dai sunfi hjy jiki da tsayi sosai.
Haka na rabasu har nakai wurin hjy nake fadin mami gani ance kina kirana ina kitchen wurin su mama kande ne.
Tace yawa zee wanan kawar tawace ke son kitso sai kuma Autana da naji tana tambayana ke dazun din.
Kallon matar data nuna min zanwa kitso nayi ina fadin yanzun zamuyi mama naji dayan race kai hjy wanan yar taki tayi min kyau wallahi.
Kafin daya tace hjy maria ke nan kedai diya mata suna burgeki tace wallahi naso dai in haifi mace kamar yadda hjy iyami ta rufe da ya mace bayan maza amma ban samu ba.
A raina nace duniya ke nan wasu na gudun mata wasu kuma suna son su kowa da irin bukatan shi duniyan nan.
Nidai ganin dukkan su manyan matane yasa na juya da sauri na bar dakin tun kan ta bani amsa lokacin da zan mata kitso.
Ina fita daga dakin mami dakin Anty Nuriya na shiga daga kofa na tsaya ina sallama kafin ta ban amsa in shigo.
Dakin yana da dan duhu ba haske sosai a lokacin tana kwance saman gadon ta makale da waya a kunnen ta.
Anty ina kwana na fada tare da dan rusunnawa kadan ta amsa min da fadin ina zuwa please taci gaba da wayan da takeyi abinta.
A hankali na juya zan bar dakin don ganin ta shagala ga waya naji tana fadin ki dan jirani please kayan da zan tafi dasu Abuja nake son ki shirya min.
A raina nace masu duniya ke nan kayan ma sai wani ya shirya mashi idan Allah ya ba wasu sai su manta kowa ma rai gare shi ai.
Dole naja na tsaya din ta gama wayan ta juyo tana kallona tare da fadin yawa tun dazun nake neman ki ai mami tace kina cikin gida.
Ina gun mama kande na bata amsa tace dama kayan da zan tafi dasu ne nake son ki shirya min su don ba wani dadewa zamuyi a can ba bai wuce ki saka min kala biyar ko hudu ba.
Nuna min jakka da zan saka mata kayan nayi na nufi wurin tare da tambayanta a ina kayan suke ?
Bude wanan drower suna ciki na zaba yadda tace hakan nayi na bude kayana daga sama har kasan wardrobe din.
Kinga na tsakiya din nan sune ban taba amfani dasu ba a ciki so ki dinga daga min dinkin su ina gani ko zanga wanda yayi min.
Bani da zabi sai yadda tace din na shiga daga mata kayan kamar yadda ta umurceni idan na daga wanda yai mata zatace muga wanan ta dan mike ta gwada a jikin ta idan kuma na dauko wani tace No bar wanan miko wancan da nake gani.
A haka har muka zabi kalla hudu zuwa biyar na gyarasu na saka mata a dan karamin troler na tafiya mai masifan kyau.
Na gyara sauran na juya don barin dakin take fadin kinga kwaso dagayen rigunan can mu gani.
Sai naji raina ya baci don dai ba wani gitma na tayi ba kila amma ta kafeni da aiki haka ba wani aiki ba.
Na nufi wirun kayan tare da kwaso mata ina dagawa take fadin aje wanan nan ko jefa wancan can har muka gama ta sake nuna min wanda zan mayar na nafe na marya inda suke.
Na juyo in kwashi sauran don in mayar take fadin wa yanan ki kwasa ina ganin ai zasuyi maki wanda naje dasu school ne wanan time wani ma sau daya nayi amfani dashi.
Ikon Allah ashe shi yasa ubangiji yace idan zakayi kayi don Allah idan zaka bari kabari don sa.
Nagodewa Allah da ban nuna komai ba duk da raina ya baci amma na tsaya nayi mata abinda take so a dakin.
Don kayana na yayan wani da wance masu tsada da kyau sun fi kalla goma wai duk ni kadai keda su tace min.
Na juya kaina a sunkuye ina fadin nagodd tace kai haba dai da baki nan ma ai duk a nan zan barsu saida hjy ta bayar dasu ga wanda take so.
Jin dadin kyautan yasa na ranan harda dakin ta na gyara mata da zuciya daya sai dai ta dawo ta samu dakin a gyara na gyara mata ko ina.
Nayiwa kawar mami kitso haka yaja hankalin sauran matan suke ta kwadayin in masu suma sai naji mami tace su bari a dawo Abuja don tare dani zata tafi.
Wani dadi naji sosai a raina jin mami tace dani za a tafi abuja din garin da nake jin labarin shi yau gani zan tafi cikin sa duk da nasan ba fita zanyi ko ina ba amma dai zan karasa ince ai na taba zuwa.
Tun da naji na fara shiri nima duk da naji Nuriya ta fadi ba dadewa za ayi a can ba nima kaya kala biyar na zaba daga cikin wa yanda ta bani ranan.
Naso sai na nunawa mami kafin inyi amfani dasu hakan bai samu ba don busy da mami take a ranan .
Bata da lokacin kowa har kanta ma da tashigo zata fice daga gidan ko ace ana mata sallama.
Sai ya kasance ina daki ko ina wurin su mama kande sai idan zanwa mami din wani abinda ya shafi rayuwan ta za a kirani.
Dan taron da akayi a dan kwana biyun dana dawo kauyen mu a gidan mami yasa na koyi wasu abubuwa da dama a furin jama,an da suka cika gidan.
Su kansu yan mata gidan mami suna ta kansu ne yanzu kowa na shirin tafiya saidai na kula cewa kamar ba wani shiri tsakanin su da yar mami din Nuriya don ban faye ganin su a tare ba.
Ko banza duk tafisu aji da kyau sosai ga wayewa da tsari don ko maganan ta abin koyone.
Washe garine za ai tafiyan inda wasu zasubi jirgi wasu kuma a mota zasu tafi inda ina cikin wa yanda zasubi mota da farko.
Amma mami tana duba list din lokacin ina dakin take fadin ban yarda abar zeey nan ba idan mun isa can waye zai kula damu kafin su iso sai dai a cire sunan wani a sakata cikin tawagan da zamu tafi.
Wayyo Allah na ashe in Allah yasoka tsuntuwa yake maga ko a dakin ka yau nice wai zan shiga jirgi tunda mami ta furta ai kamar na shiga ne in Allah ya nufa.
Karfe shidda yai muna a filin jirgi ranan nasha zagi gun yan matan mami don tafiyan nan da mami tayi dani a jirgi tare da kawayen ta da yaranta dama wasu daga cikin dangin su.
Koda muka isa can motoci muka samu sunzo daukan mu nidai basai na fada ba don bakauya na koma a cikin duk da dai kowa yana harkan gaban shine.
Amma hakan bai hana tsaraguwa ba a cikin su da rakubewa a guri daya tunda ba wanda ya sanni ko nasan shi sai mami da yaran ta sukuma bata kaina sukeyi ba.
Duk da akwai yan aiki irina kalian da wasu sukazo dasu daga wasu wurare sai dai hakan baisa na mamesu ba ina falo ko da yaushe don kada mami ta nemeni ban kusa kamar yadda naji ta fada kafin muzo.
Haka komai ke tafiya a tsare kamar yadda suka tsara abinsu gwanin ban sha,awa sai kallon mamaki nakeyi maza da mata ana ta cudanya a guri daya ba wanda ya damu da hakan .
Da kauyen mune ai da hakan ya zama abin magana a gurin mutana amma nan ba wanda ya damu da hakan .
Wai washe garine za ayi rantsuwar su mami din tunda muka iso wasu maza sukazo gidan suka fita tare da mami da yaranta manyan mazan biyu.
Haka yasa kadaicin rashin gabnin su mami a gidan ya dameni na dawo katon falon na zauna tare da wasu mata suna ta hiran su nidai sai sani lokaci nake dan jin hiran da sukeyi din.
Ina kallon duk mai shiga da fita don na jawo kofan da muka sauka a cikin hikima na zare key din kofan ina ji daga inda naje zaune ana tambaya na kyalesu.
Don ba wanda zai daukacewa nice na kulle kofan sai dai da mutum yazo ya murda yaji a rufe kofan yake ya juya inda ya fito.
Har masu tafiya a mota suka iso gidan ya kara rikicewa da hayaniyar jamma, a haka yasa na fito daga cikin falon na dawo waje na zauna.
Balle tun isowar ya matan suke aika min harara da warning ya karasa na gudo daka ciki na dawo wajen gidan.
Nan ma motocine ke faman shige da fice tun ina aunawa a raina ince wanan yafi kyau a, a ta dazun tafi har na gaji na zubawa sarautan Allah ido.
Can naga dawowan su mami hakan yasani mikewa tsaye daga inda nake zaune ina kallo na nufo wurin motar nasu.
Sannu da zuwa mami na fada daga bayan ta hankalin ta naga daddy su siyama jikokin ta suna magana.
Hakan bai hana mami dan juyowa tana amsa min gaisuwan ba ta juya taci gaba da maganan da sukeyi na juya zan bar wurin .
Sai kuma ta juyo tana fadin zeey karbi jakkan nan nawa ki rike min nazo da sauri na karba na ja dan nisa dasu na tsaya.
Sun dan gama magana ta fara tafiya yana biye da ita yana fadin amma mami sai naga kamar dai bayanin farkon nan shine shawaran bi koda yake barin gashi Jafar din duk da ban san inda ya shiga ba.
Kuje kuyi shawara dai zan dan shiga inyi sallah kafin wani abu ya dauke min hankali kuma ta fada ta fara tafiya makarrabanta suka biyo bayan ta ruuuu dasu.
Nima binsu nayi da kallo ina mamaki duk wanan taron haka don mami akayi shi haka ?
Naji tace on Allah ku bari inyi sallah yanzu zan fito ta nufi kofan dakin da nake zaton shine nata wanda na riga dana rufe tunda na fahinci hakan.
Mami ai kofan a rufe yake wata ke fadi daga gefenta lokacin da hjy ta murda kofan dakin da zuman shiga dakin..
Tun dazun ai dakin yana rufe an rasa inda key din yake da dan mamaki ta tsaya tana juyowa kafin na karso ina fadin ga key din mami a hannu nice na rufo kofan dazun.
Ok zeey key din yana hannun ki ashe thank god wallahi yarinyar kirki shaf na manta da zan fita in rufo dakin.
Da sauri na ciro a cikin aljihun dogon rigan dake jikina tunda ta dan jaye wurin na gane nufin ta na isa da sauri ina bude kofan.
Juyawa mami tayi tana fadin don Allah a dan jirani in fito tasa kai tsshiga tana fadin zeey shigo ki hada min wanan maganin nabi bayan ta muna shiga tace don Allah rufo kofan nan in huta hakana.
Ki duba akwai magani a cikin jakka ban samu shaba da safe na fita take fadi tana shiga bandakin.
Maganin na dauko daga cikin jakkata don nasan shi na saba hada mata na balla daidai yadda take sha na dauko goran ruwa mara sanyi dake dakin na a je akusa.
Daidai tana fitowa ne ake buga kofan taja tsuki tare da fadin mutanen nan idan nabita nasu bana samun sallah ko azahar ban samu yiba yau balle la,asar ga lokaci na shigewa.
Dukan kofan da aka karayi da karfi take fadin wai waye zeey bude kofan idan maishi ya shigo yaga ina sallah dole yajira idan zai iya.
Kofan na nufa na bude daga ciki aka turo ana fadin haba mami kin fita tun safe kin dawo kuma kin shige kin rufe kofa.
Aisha yar mami ke magana tana shigowa dakin a cikin shagwaba idon ta ya sauka kan mami dake kabara sallah kafin ta juyo tana kallona tana fadin.
Tare kuka fita ke nan da mami din kai na girgiza bakina kuma na fadin ina nan gida ina falo zaune na bata amsa.
Wuri ta samu ta zauna tana maida hankalin ta furin wayan ta yayin da na shiga gyara dakin don wanan daman na samu a yanzu tun zuwan mu garin..
Har mami ta idar da sallolin dake kanta ta juyo tana fadi Esha ya akayi ne wai ma kunci abinci kuwa ?
Zeey kinci abinci ita dai wanan din nasan halin ta balle yau taga wanan taron haka a gidan nan ?
Kaina girgiza daga inda nake tsaye ba tare da nayi magana ba kina jiran me wanan yarinyar da gidanci kike wallahi ga abinci nan ki tambayi safiya mana tunda ta iso idan baki san wanda zaki tambaya anan.
Waya ta dauko ta kira wani layi aka dauko ku kawo min abinci na mutum uku a hada komai a ciki ta fada.
Tana kashe wayan tare da jan tsoki kafin Aisha ta ce mami gobe fa ni dinner kawai zan yi attending.
Kina haukane gaba dayan ku da tan uwaki zamu tafi don duniya ta san ku ta fada sai yarinyar tace but mami kinsa, , ,
Hannu ta daga tare da fadin ban son korafi idan na fada kinsan iyakar maganata ke nan aka turo kofa wace ta kirane dauke da abincin wata hamshakiyar hajiya zakace ba zatai bara gidan kowa ba don bunkasanta sai gata itacs mai kasowa mami abincin .
Bayan ta aje suka dan tsaya magana da mami nidai duk sai naji na takura a cikin su don Aisha ita tana dawainiya ne da wayanta bata ma saurareb su.
Can mami ta juyo tana fadin zeey zuba muna abincin muci ko ?
Matar ta juyo tana kallon daidai lokacin dana tashi tana fadin wanan yar ina kika samotane don ban santa ba gaskiya.
Yata ce ta bata amsa kai tsaye tana jawo plate din abincin dana aje mata a gabanta inda ta idar da sallah.
Kije ki lissafa min matan nan da suka zo da yamman nan za a kaisu masaukin su idan sunci abinci tafadawa matar.
Yan kaduna ko na wani gari eh toh zaki iya lissafo min group group daga nan ki kiramin safiya tazo.
An gama hjy ta fada tana fita daga dakin Esha aje wayan nan ki dauki abincin nan kici ta fadawa yarta.
Ke kuma zuba naki idan kina zama da yunwa zaki jawa kanki matsala ba ruwana tana kai abinci a bakin ta.
Zuba wanda nasan zai isheni nayi na dauka zan fita daga dakin take fadin ina kuma zaki dawo ki zauna muci a nan .
Aka turo kofan yaya Mamud ne daddy su siyama ya shigo dakin da sallama ta karba mai tare da fadin har kun dawo ke nan yace .
Eh mami an samu inda ya dace saidai kudin kusan duk dayana ne ma mamud kasan kudi ba matsala bane ai a dai samu inda ya kamata din shine abu yanzu.
An samu mami kuma danki yace a tura mai ko nawa ne kudin zai biya munyi waya dashi ban samu ganin shi ba.
Ai da ya barshi tunda akwai kudi a hannu na don gwaunati ta bamu dan kudi a hannun mu ai.
Sun dade a dakin suna magana shigowan anty safiiya dakin yasa yafita ni dai ins zaune cikin su a tsawale.
Bayan na gama na fito na barsu tare da anty safiya din suna magana kayan abincin na kwasa nakai kitchen inda ake tarawa.
Nafito da zuman komawa falo in zauna muka hade da anty Rufaida wani irin shock naji lokaci guda saida na dan ja baya don tsoro.
Yar iska masuwa mutane asiri kin dauka ba wanda yasan abinda kukewa mami daga ke har wace ta kawo kine gidan.
Mu zuba dake a gidan nan ki gani idan zaki sha ruwa ya fada maki a ginan nan bakince kun iya mallake mutane ba ku.
Duk da ban gama fahintar inda zancen ta ya nufa ba na dan gane wani bangare na zancen nata kadan.
Tana fadin haka ta juya tabar wurin ba anty rufaida ba gaba dayan su yan kaduna dana sani a gidan wani kallo na kyamata suke bina dashi .
Na kulla da hakan ne idan sun hangoni sai inga suna kallona ana gulmata ma,ana dai sun sani a baki sun tsargeni ke nan a yanzu.
Wanda bansan wanan dalilin ba kuma banda wanda zaimin bayanin hakan sai kawai na fara kama kaina da kowa fiye da dacan baya dan dama anty salma idan mun hadu ba wanan kallon raini ko wullakanci sai dai idan na gaishe tace zeey din mami ke nan.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.