Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 115 of 139

ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA ALLAH YA SADA MU DA AHERIN SA AMIN YA ALLAHU, , , ,

YAR UWA KADA KI MANTA NOVEL DIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA, , , ,

Sannu a hankali har inna ta fahinci irin zaman da nakeyi da ya jafar tun bayan auren mu dashi ba abinda ya taba shiga tsakanin mu har zuwa wanan lokacin.
Kalman hakkuri kawai da ban baki yake fita daga bakin ta na kara hakkuri na dan lokaci kamar yadda malam ya fada.
Na kancewa inna naji kawai amma amma a zuciyana ba haka abin yake ba din ni ba zancen gyara nake so a tsakani mu ba illa iyaka dai naga na barshi har abada.
Kwana biyu ya cika a haka na shirya zuwa gidan malam din kamar yadda mukai alkawari dashi zanzo bayan gama binciken shi.
Inda na samu ni yake jira na iso daman zai tafi wani unguwa shi bayan mun gaisa da iyalin malam din mun dan taba raha kamar yadda muka saba da iyalinshi idan mun shigo a matsayin su na matan kakan mu din.
Na nufi wurin malam din ni kadai nabar kanne dana zo dasu tare dasu maizube suna hira a tsakar gida.
Muka gaisa dashi yake tambayana lafiyan inna nace suna can lafiya ya dan dade yaja dan dube dube yana jawo ledoji a cikin kayan shi.
Kafin ya dago kai yana fadin kamar yadda na fada maki zanyi istihara kafin nace wani abu sai idan na bincika naga abinda ke nan.
To a gaskiya nayi din kuma naga akwai matsalan da duk kika fada ba karya a cikin sa ko kadan.
Ya dago kai ya kalleni na dukar da kaina a cikin damu a lokacin da yake fadin sai dai abinda nake so dake yanzu na farko ki kwantar da hankalin ki .
Komai yana bukatan natsu a cikin sa dolene mu bishi a sannu kafin mu kai ga nasara ga abinda muke nema.
Bai fada maki karya ba kamar yadda yace maki ya daina ya daina wanan harkan din saidai kawai matsalan da karfin maganin nan da tsohuwar nan tabaki da yaso yai mai yawa a jikin shi saboda abin ya bugeshi sosai.
Ki godewa Allah yar nan da Allah ya taimakeki ya hau dake kan masu bibiyan ki da sheri akan mijin naki.
Mafarkin ki da kikeyi a baya ya baiyana a gareni yanzu na fahinci dalilin mafarkin naki akan wanda kike yawan gani ya shiga tsakanin ki da mijin ki a cikin mafalkin ki.
Ba wani bane illa wanan harkan da sukeyi ne Allah ke son ya baina muna tun baya ba a gane hakan ba sai yanzu da lokacin da baiyanan yazo muna.
Don haka ya zama dole ki daure ki kara jajircewa akan wanda kikeyi tun farko kada su ga kasawan ki ga hakan.
Babban kokarin da zamuyi shine muga mun shawo kan matsalolin nasa a baki daya har in son samune ya rabu da abokan harkan nasa har abada.
Saidai gaskiya wanan tsohuwar data baki magani tasan kanta a wirin aiki don tasan magani sosai.
Don mawuyacin abune mutum ya iya daina wanan dabi,an haka kai tsaye ba tare da ansha wani wahala sosai ba dashi.
Don abin nasa ya hade masa da yawa akwai sa hannun makiya dana muggan abokai a cikin lamarin shi .
Shi yasa abubuwan suka taru sukai mai yawa a lokaci guda don Allah yayi yaron nada karfin arziki mai yawa a rayuwan shi dan ba haka akaso ya kasance ba.
So akayi ga baki daya ya lalace a rayuwan shi tun farko an haska anga cigaban shi dana sauran yan uwan shi akwai rinjaye mai tazara a tsakanin shin da duk wani na family din su baki daya tun wanan lokacin aka jefa masa wani rayuwa na daban a cikin lamarin shi don ba haka mai sakon yaso ya kasance ba.
Kuma an basa abin yacine tunda kurciyan shi na yarinta akaso ya soma lalacewa don mahaifinsa yana tsaye da lamarin yanyan sane abin bai samu tasiri sosai a jikin saba wanan lokacin sai bayan mutuwan mahaifin nasa ne abubuwan suka fara aiki a jikinsa yanzu.
Gareku iyayyen zamani kalubali ne wanan zancen a gareku mu kula da wa yanda muke mu,amula dasu a rayuwan mu don wasu a fuskane kawai soyayyan su garemu.
Baikai ciki ba yadda kike zaton kekaki bazaki iya cutawa dan wani ba wani nacan ya kyashewa naki yana kai masu hari a fakaice sai mu yawaita addua gun yayayen mu don nema masu kariya daga shedanun mutane kamar yadda malam ya fada mahaifin su jafar yana tsaye ga addua a gun yayan shi.
Shine dalilin dayasa abubuwan jafar din sukai sanyi basu samu aiki a gareshi yadda maishi yaso ya gani ba.
Ga kuma abokai dake canza rayuwan yaro lokaci guda ya zama dole garemu wanan zamanin musan dawa diyan mu suke mu,amula a kullun don kawaicewa fadawa halakan zamanin Allah ya tsare ya kare muna zuri,a amin.
Har malam ya gama bayanin sa jikina ya mutu a lokacin ina tunanen waye zai jefosa haka da mugun abu don ya koma hakan.
Don masu kishiya nake jin iri wanan kalamin na faruwa a tsakanin su idan a hadu da mai raunin imani.
To amma gashi ita mami bata da kishiyan kuma hakan ya sameta ga zurian ta yanzu.
Muryan malam ne ya dawo dani ga tunanen da nakeyi da yake fadin kinga akwai aiki babba a nan don sai mun wareware kulin zamu san aikin mu na kyau akansa.
Na gyada kai kawai alaman eh malam don jikina ni lokacin ya gama mutuwa da zancen daya fada min din.
Zaki iya turarara wanan hayakin ta yadda zai kai ga hancin sa ya shaka na kwana uku malam ya tambayeni.
Na dago da kai da sauri a dan razane don sanin kwanan wasan don wancan karon da kakar maya ta ban magani yadda muka kwashe dashi.
Malam bai tsaya jin ta bakina ba don ya fahinci irin tunanen da nakeyi a lokacin sai cewa yayi dani zaki iya mana sai kace ke din ba mace bane.
Yana fadan hakan yake miko min maganin dake kulle a cikin wani dan kyale ja na karba kafin ya juya yana dauko wani a haka dai duk yai min bayanin ko wani maganin da amfanin sa gareshi.
Nabar gidan malam a hanya wayan ya jafar ya shigo min na dauka da kyar bayan mun gaisa yake fada min yaso shigowa satin nan don mu dawo amma yafiya ya kamashi zai fita ba zai dade ba zai dawo sai yazo ya dauke mu mu dawo.
Jin hakan take wani tunane yazo min a zuciyana don na gama yanke shawara a kansa ko yanzu.
Do duk abinda zanyi karshe nice mai laifi a wurin mami ba zata ga hakan ba sai laufin da zata dora min da banji ban gani ba.
Haka na dawo zuciyana cike da zargi iri iri a lokacin don ni abin har tsoro ya fara ban don mutum ba abin yarda bane ashe haka.
Don ko waye lalai na jikin sune don yadda mami take kafa kafa da yayan ta nake gani ashe hakan bashi ya dace tayi kawai ba a rayuwan ta a kan yayanta.
Don bayan sa ido irin wanan da takeyi ya zama dole kuma uwa ta dage da addu,a da neman tsari gun yayayen ta ashe .
Koda ta hanyar yawan yin sadaka ko alheri da sunan yayanta Allah ya tsare mata su don sherin zamani.
Amma da yake ita mami yanzu irin rayuwan turawa ne gareta duk ta mance da wanan a rayuwanta batayi sadaka ba zuwa garesu don hakan balle wani neman taimako gun malamai a kansu don abin yanzu saida hakan .
Saidai kada mutum ya zure don gudun fadawa ga halakan ubangiji don yadda da irin abubuwan nan gaba daya yana juya kan mutum ya manta da Allah watarana.
Sai mu kula mu dinga sadaka da sunan yayayen mu da yawaita alheri ga marayuwa da masu karamin karfin shine mafita.
Washegari kawai na tashi ina fadawa inna zan tafi fambeguwa tayi mamakin hakan saidai bata hana mu zuwa ba sai ta fadawa Abban mu shima ya yarda.
Da sa,adatu da sadiya mukai tafiyan inda Allah ya taimakeni shine mun tafi washe gari sai ga waya ana neman su sa,a datu makaranta nace su tafi tare da sadiya don naga bata sake jiki ba.
Suna tafiya nima na tsiri tafiya kan zanje na duba wata kawata na dawo kafin su dawo haka na samu hanya na balle ba wanda yasan inda na nufa.
Ni kaina ban san inda zan nufa ba na juyo zuwa kaduna kawai gidan wata kawata da mukai yayin zuwa makaranta a tare lokacin can dabaran zuwa ya fado min don su din gidan sune na kansu bana wani ba.
Ban sha wani wahala ba sosai wurin gane gidan saidai itace da farko bata gane ni ba saida nayi mata kwatance da kyau tace ta ganoni ta rungumeni.
Mun zauna ana yaushe rabo a nan take ban labarin ai mahaifin su ya rasu bayan rabuwan mu bada dadewa ba.
Na tausaya masu sosai don ni kaina naga sauyi sosai a gidan maganane kawai ban yi ba tun shigowana.
Gidan da yake da yawan arziki ga yan aiki da jama, a amma yanzu shiru babu kowa tun wajen gidan shara da tulin ganyen bishiya zasu tareka a waje shiyasa da farko harna zata ko ba kowa a gidan ne yanzu.
Mun kai wani lokaci muna hira kafi mu ci abinci mu kwanta barci na kashe wayana gaba daya tun shigowana garin kaduna na jefa a jakana.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.