Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 81 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWAAkwana a tashi ba wuya a wurin Allah sai gashi har hjy ta gama shan maganin da aka bata suka koma da ya jamal don shi yayi tafiya wata kasa a lokacin yasa yabar komai a hannun jamal din.
Suka bata sallama da sharadin zata dinga zuwa checkup duk bayan wata uku lokacin da naji hakan nayi murna kwarai don a zato zata zauna damu nan ke nan ga baki daya har lokacin da asibiti zasu sallameta baki daya.
Saidai me ranan daya dawo daga tafiya baiko shiga dakin shi ba ya zarce wirin hjy sun gaisa tare da dan taba hira dashi har ta sako mashi zancen da asibiti sukayi.
Shima cewa yayi da ita ashe zama chaina ya kamaki ke nan yanzu zaki shakara tare damu a nan ke nan ?
Da wani irin sauri ta dago kai tana fadin ai in kaga na kara sati daya a kasan nan to bansan hanyar gida ba kenan idan kuma har ban sani ba sai in buga gida suzo su dauke ni.
Hjy kamar wace dai ake kora ya fada a dan galabaice yana dan mika don zama cikin jirgi da yayi yasa shi gajiya don har dubai suka je bayan sun gama meeting.
Hjy ta kalleshi tana fadin jeka ka huta mana tunda ka debo gajiya haka da yawa ni bance kuma da kai ana korana ba a nan.
Iyakar gata dai kan aikun nuna min shi a duniyan nan nikai na godewa Allah na godewa haihuwa don yai min albarka.
Ya mike yana fadin ni dai kan baki haifeni ba uwata dai ta iya haihuwa tunda itace ta haife ni ai hjy tace ja,iri waya haifi uwar taka da kake yabo da ban haiho ta ba har zata haifeka.
Yau dai na gane fitina wanan tsohuwar kike ji dashi zuwa Nigeria kuma baki zuwa sai ranan da likita yace ya sallameki kwata kwata mama ce kadai zata koma ke ko kina nan tare damu.
Dakai da likitan kunci gidan ku na gane abin naku hadin baki ne ni ko da kafa sai in karasa gida ba matsala bane a gareni.
Zakiko hadu da kura dasu zaki hanya in takaman ki zuciyana ya fita yana dariyan yadda ta takankare tana masifa dashi don yace ba zata tafi ba.
Ance sabo turken wawa bansan dan zaman mu tare ba har akwai sabon da ya shiga tsakanin mu hakan sai bayan tafiyan nan nasa .
Duk ko da yatafi bamu cikin dadin rai dashi don har lokacin akwai fushin daukan mai kaya da nayi ina dubawa ya dauki fushi dani sosai a gidan.
Har tafiyan nan ya kamashi yana cikin fushin haka dani ko zancen tafiyan a bakin hjy na farajin zaiyi tafiya wai.
Na nuna mata nasan da zancen sai dai na manta da sunan kasan don yana da wuya mama Ramatu ke fadin ni dai yar nan kada wata rana ki ba dana kunya da wanan kauyancin naki.
Hjy tace haka yarki tayi kafin ta waye itama aishi jafari ya mai da tarihin ubansa ne a rayuwa don haka ku bar ganin laifin shi haka.
Da zai tafi kuma sai safiyan ya shigo min daki bayan ya shirya har an fita mai da kayan shi ina zaune saman dan stol din mirrow dakina ina shafa mai da nayi wanka.
Ya shigo dakin ba tare da tsayawa ba yake fadin zaiyi tafiya zai kwana biyu a can idan muna da wani matsala in kira Samuel in fada mashi ko menene .
Daga haka ya jiya zai fita a dakin na samu na bude bakina da kyar ina fadin Allah ya kai lafiya Allah yasa abinda akaje nema a samu .
Na gode ya fada ya fita da sauri nabi bayan shi da kallo tare da sauke ajiyan zuciya na mayar da kaina ga mirrow ina kallon kaina a cikin madubin dake gabana .
A hankali na raya a raina wai ina nake da matsalane a jikina da ya jafar bai min kallon mace ne har yanzu yadda naga wasu maza sunawa matansu dai ?
Nidai banga inda na kasa ba da bai ma son ko ya kalleni idan har ya tsura dani haka a dakin da sauri kuma na kawar da wanan tunanen a raina ina fadin .
Kenan har na damu da ya tabeni ke nan kamar wata jarababba dani nikan ina zan yarda da wani tabi kazami dashi yana shan giya kuma ya dawo ya tabani.
Yau ma daya dawo ina kwance ina tunanen shi ashema yana cikin gidan ko a lokacin ban sani ba saida zai shiga part dinshi ne kamshin turaren da yake amfani dashi ya bugo hancina don kofa a bude halimatu ta barshi da zata fita .
Saida naji gabana ya fadi sosai shiru na saurara banji motsin shi ba a dakin na sauke ajiyan zuciya a hankali tare da gyara kwanciya naci gaba da karatuna da nakeyi.
Har wani lokaci hankalina bai kwanta da rashin ganin sa ya leko ba kuma ban daina jin kamshin sa a hancina ba saina dauka kewan shi kawai ke damuna nake jin hakan.
Karshe dai waya ta na jawo na fara gamen a ciki tunda layin da nake dashi na Nageria ne bai zuwa ko na kira dashi.
Nayiwa ya jamal magana ya saya min da zai fita ranan mama ta hana ya sayo min wai kila mijina baida bukatan na rike wayane a nan yasa bai sayo min ba don haka kada ya soma ya sayo min su samu matsala dashi.
Don haka ya jamal din yaki sayo min layin da zanyi amfani dashi amma bayan wanan duk abinda mukace muna so idan zai fita yakan sayo muna yazo muna dashi.
Wani lokacin ma idan bamu ce ba zai sayo din tundawa halimatu da take mai oyoyo idan ya dawo tkan zauna ta mai surutu sai ya gaji ya barta.
Shikan gaskiya bamu da matsala dashi ko kadan don a kannensa yake daukan mu wani lokacin ma har ya tsawata wa halimatu idan tana wani abin.
Hankalina ya dauku sosai ga game don haka banji shigowan shi dakin ba sai dai kamshine ya sanar dani hakan yasa na dago kai da sauri na sauke a kanshi.
A lokacin yana tsaye daidai kaina ya sanya fararen kaya a jikin shi farin wando da wani riga mai kama da t shirt din maza saidai yadin shi mai laushi sosai saidai hannun rigan bai sauka har kasa ba.
Saida na dan firgita dan ganin shi girshi hakan a gabana cikin rawan baki nake fadin yaya sannu da zuwa ya hanya ?
Idon shi akan wayan dake hannu da nake game ya amsa min tare da fadin ina sadiya banganta part din su hjy ba dana shigo.
Ban san inda ta shiga ba na basa amsa yasa yai min wani kallo kafin yace kila suna tare da mamane don itama ban ganta a dakin ba.
Kokarin sauka daga kan gadon nayi ina ganin ya juya zai fita don hankalina ya tashi da cewa da yayi halimatu bata gidan.
A daidai lokacin da muka sauko falon ne kuma naga ana shigowa da kayan da ya dawo tafiyan dasu yana tsaye yana magana da Samuel akan kayan.
Dan ganin Samuel di na kallon direction din daya fito yasa shi dan juyowa yana kallon wurin nice nake kokarin gyara daurin gyalen dana rufe kaina dashi lokacin.
Na karaso ina jin yana fadin ku kai wanan part din ta wanan kuma ya nuna part din hjy da nufin su kai can sauran yace su shiga mai dashi wurin shi su adana.
A kawo abinci ko fita zakayi na fada cikin karfin hali da daurewa yace ba yanzu ba sai da dare zanci daga haka ya juya zuwa part din shi ni kuma na shiga wurin hjy don jin abinda ya fito dani.
Na samu hjy tana kallon kayan da suka aje a gabanta tana mamaki nayi sallama take fadin ni wanan menene kuma a ciki suka shigo muna dashi haka ?
Ya jafar yace su shigo dashi nan na bata amsa ina zama zan tambayi su mama sai gasu sun shigo mama na fadin ashe jafar ya dawo yanzun muka ganshi a waje zamu shigo .
Ya dawo yana tambayan ku nake fada mashi kun fita mike kafa da jamal yake fadin ku rage fita a garin nan sosai.
Da gajiyane man kullun mutum yana guri daya a zaune mama Ramatu ta fada tana kaiwa zaune fuskanta a abinda ta gani daure.
Wanan kuma fa hjy ta tambaya tana kallon mahaifiyar tasu hjy tace miskilin danku yace a shigo dashi bai min bayanin ko meye a cikin sa don baima shigo ba tunda ya fita dazun.
Fita halimatu tayi sai gata ta dawo dauke da cup cike da milk a cikin sa sai snack a dayan hannun nata.
Allah yagani ina jin kunyar wanan rawan kan na halimatu a gaban su duk dako nayi mata fadan haka a dakina don ban manta da gorin da mama tayi muna ba a farkon zuwan mu gidan kan abinci.
Yanzu ko tana nuna muna ba komai saidai ni ban yarda da hakan ba tunda har hjy ma data haifeta tace min nayi hankali da mama din ke nan ba sona da gaske takeyi ba.
Shiyasa a kullun nake cikin jawa halimatu kune da ita din kada taje tana sake maganan gidan mu a gunta watarana a samun abin mana gori dashi.
Nikan mikewa nayi da niyar ficewa daga dakin sai naji mama na fadin ai jafar din naga ya fita ina kuma zaki ana zaune ana hira.
Ikon Allah ke haka kikeyi a gidanki idan mijin ki yana gida wanan saka idon har ina kuma Ramatu ?
Haba dai hjy don na fada mata ya fita ai laifine kuma hakan yanzu gani nayi dai ko ta fita baya gidan ai .
Ki barta ta tafi nace maki bana son wanan saka idon tsiya akan yaran nan bansan dalilin ku nayin hakan ba ko kukan mata kuma kuna da diya mata ne a gaban ku.
Yanzu kuma hjy meya kawo wanan maganan daga fadin baya nan ta zauna shine na wanan maganan haka ?
Ramatu ina dai horon ki da wanan dabian ko ita wace kike tayawa din wata rana zatai nadaman hakan mujuri zuwa rafi dai akace inji hausawa.
Tashi kije mama ta fada a dan hasale tana kallona nace dama daki zan koma in dauke kayan dana bari a gurin.
Jeki kawai ban tanbaye ki ba kada kuma kija min wani laifin gun hjy yanzu nikan jikina yayi sanyi haka na fita na bar masu dakin.
Ashe hjy taji wayan mama Ramatune da mami da take fada mata ya jafar baya garin yai tafiya sai mami kecewa da ita.
Ta kara saka ido a kaina ta kula da kyau kada ta bari in samu wani sakewa ko kadan dashi don ta tsani ta bude ido taji muna tare da danta wallahi.
Ta kare da fadin sai yanzu nake yarda Ramatu da ake fadin asiri sukai min ita da iyayyenta tun kan tazo ki duba fa.
Yadda na dauki yarinyar nan kamar ba yar aiki ba a gidana tankar wata jinina na jiki na mayar da yarinyar nan wai lokaci guda jafar yazo ya birkice min a kanta.
Yau itace a kasan chaina zaune abinda ke kara ban haushi da takaici muga namu yayan zaune a gida Ramatu yau wa yaki nasa yasamu miji kamar jafar wai ?
Mama Ramatu tace shine abin da nake fada maki ai anty lokacin nace irin yaran nan ba abin yarda bane wallahi kinki ki gane hakan a lokacin.
Sam ban yarda ai tayi wani abin sakewa ko kadan tana nan yadda kika santa har yanzu saima dawowan hjy gidane ai ta dan sake jikin ta.
Sun dauki lokaci suna magana a kaina itako hjy tayi kamar tana barci ne a lokacin basu sani ba don ta dade da kwantawa a lokacin yasa mama ta dauka barci takeyi har lokacin.
Jin hakan shine dalilin da hjy take samata burki ga duk abinda tayi ta gane da manufa take min shi sai ta taka mata burki a take.
Kayane na ban mamaki na shiga tsara saidai duk kyausu nikan basu min ba don sai na dauka shigan yan iska yake son mu dinga yi kawai a kasan nan yanzu duk da dogayen rigunane basuyi kama da wanda na saba amfani dasu ba masu gyale da nake yafa gyalen a kaina wani lokaci.
Haka na halimatu dana gani a ciki suma dai din masu tsadane sosai daganin su na tattara na saka muna a wardrobe hakama takalma da jakkunan na aje a gurin ajesu.
Sai da dare na shiga part din bada niyar kwana ba kamar yadda na saba shiga yana zaune na sameshi da waya a hannun shi sai cup din daya rike yana shan abu a cikin wanda bansan ko meye ba yake sha a lokacin.
Har na karaso inda yake zaune yana kallona a cikin tsarguwa da daure fuskan shi gareni nima duban kofin nayi na kawar da kaina tare da kaiwa kasa na rusun na ina fadin munga kaya mun gode Allah ya karawa dukiya albarka.
Ya gyada min kai yana zaune yadda yake saidai wanan karon ya mayar da kanshi a makarin kujeran yana mai lumshe idon shi a hankali.
Ina fadin haka na mike ba tare da wani jinkiri ba na juya na fito daga part din zuciyana cike da zargin abinda naga yana sha din a lokacin .
Ya Allah ka kawo wa wanan bawan naka dauki ka rabashi da wanan hali da duk wani abin hani daka hani al,umman Annabi ka dashi ya Allah.
Na fada idona yana mai cikowa da hawaye haka na kwanta na dunkule a wuri daya zuciyana yana min tunane kala kala lokaci guda.
Yanzu koda ace muna kwana a tare ne nayi fushi dashi haka yaya zai barni cikin rashin kulawa ko damuwa da hakan?
Ashe da gaske ne da yake yawan fadin shi mace bata gaban shi asalima saidai yai mata kallon yar uwa ko abokiya kawai a idon shi.
Idan ko har hakane akwai aiki ja a gabana don ba zan zauna a rayuwa haka da miji kamar kurman maza ba.
Shin wai shi wani irin mutum ne haka koko shan giyar dayakeyi ne ya mayar dashi hakan ba,a sani ba ko kuma wanan dalilin ya zabeni a matsayin matar shi don ya cutawa rayuwana haka dai nayi ta faman tunane barkatai har barci yai gaba dani.
Bayan kwana biyu da faruwan hakan nake jin zancen tafiyan su hjy wanda hakan ya tayar min da hankalina sosai.
A cikin hakan ne ranan sai gashi ya shigo muna da takardun karatun mu wanan abin ya ban mamaki matuka.
Duk ina karama haka bai hanani fahintar hikiman shi na kyautata min a gaban su don kawai su dauka kwai fahinta a tsakanina dashi.
Idan ka gani zakacd duk dadin duniya ya kare a guna yadda yakan sayo min abu mai tsada ko ban kulawa a gaban su.
Nikan da abin yakanzo min bambarakwai bana iya boye mamakina a fili ko rashin sabo da haka daga gareshi.
Na samu hjy a daki ita kadai muna hira nake fadin hjy tafiya zakuyi ke nan idan kun tafi nasan rayuwana yana cikin garari a gidan nan.
Hjy ta dago kai tana fadin akan wani dalili har zaki shiga garari yar nan sai lokacin na farga da kato baran da naso yi a gaban ta ashe.
Da sauri nace hjy idan ba wani da zan dan dinga hira dashi haka ai sai damuwa ya kamani ko tunda shi yaya ba zama yakeyi a gida.
Tare da fadin kuma din yace karatu zaku soma ai bada dadewa ba saidai tunanen gaskiyane don nima ban amince na barku haka daga ku sai wa yan nan yan arnakun ba a gidan nan gunda shi din dai bai zama.
Zan kara mai magana kan wace zata zo ta zauna daku nan don kwanaki nayi mai bai ban amsa ba kan hakan.
Barshi dani nasan yadda zan fito masa a yanzu dole ya yarda da hakan ai tunda dai ba zama zaiyi ba daku a gidan.
Ana gobe zasu tafi dagani har halimatu mun kasa tsayar da hawayen mu kuka sosai mukayi ranan saida muka ba kowa tausayi.
Shi da kanshi yaya ya rarashi halimatu don tace ita bin su hjy zatayi ta koma Nigeria da zama daya tambaye ta dalilin ta tace nan din yaya ba a fita kuma bama jin yaren su ai suma basa jin namu kuma.
Da kyat ya samu ya rarashe ta hanyar cewa muma bada dadewa ba zamu je Nageria yanzun ta bari su hjy su fara tafiya don kada tayi fadan zuwa damu.
A airport ma ban iya tsayar da hawayena ba sai faman kuka nakeyi hjy ma hawayene yazo mata tana sharewa da gefen gyalen dake jikin ta.
Ta dan dafani tana fadin zainabu wanan shine aure dakike ji ana fada a rabaka da iyayyen ka da kowa naka zuwa inda baka taba rayuwa a ciki ba sai halin da kaje dashi.
Shiyasa kike jin ana fadin aure yakin mata don idan ba mace ba babu namijin da zai iya barin gidan su har abada sai kadan da suke shigewa duniya.
Gidan ya koma muna ba dadin zama mu biyu kawai ke rayuwa a cikin sa haka zamu suni zungun a gidan idan dare yayi kuma kafin ya dawo ma mun shiga kwana koda kuwa ba barci zamuyi ba a lokacin sai mu zauna muyi ta hira ko labarai a tsakanin mu muna dariya.
Har ranan da zamu fara fita zuwa school din yayi a zatona shine zai kaini school din sai gashi driver yasa ya sauke mun don an gama biyan komai a lokacin.
Sai gamu a bakon wuri muna faman robon ido don ganin bakar fata a wanan wajen sai can ba a rasa ba zaka gansu jefi jefi kuma ba yanayin musulunci a tare dasu.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.