Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 41 of 139

🦅ABU CIKIN DUHU SIRI NE🦅

3️⃣4️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

Bayan kwana biyu da dawowan shi garin na girshesu dakin mu na fito daga kitchen na nufo dakin da sauri na in fadawa hjy aiken da tayi min wurin kande a kitchen.
Da sauri na koma baya na kasa shiga dakin a cikin tsoro da fargaba don Nuriya dana samu a dakin tana kuka wiwi a tsakiyan su.
Kitchen na koma cikin fargaba tare da tunanen ko akan akainane ko kan waye sukayi wanan haduwan haka.
Na dade a kitchen din kafin in koma dakin bayan fitan su daga dakin wurin hjy duk dako sun dan dade a dakin suna tataunawa a lokacin.
Hjy tana zaune ita kade a dakin bayan dul sun watse daga dakin tana zaune da kullin abu a farar leda tana kallo.
Na shigo take fadin kina kitchen wurin kande ne nace eh na shigo dakin nasame ku a ciki na koma .
Muna nan da mara kunyar sarakuwar gidan nan yau tajimu a gidan nan don jarumina yai mata tas a dakin nan a gaban kowa ya tashi taka ta saida uwarku taja mashi burki.
Wanan dan maganan da tayi ne ya sani tunane tare da jin tsanar da nake mai a wautana gani shine ya jawo min duk wani tsagwama da akemin yanzun a gidan mami.
Sai naji ya dan ragu a raina don yadda hjy tayi min bayani sai naji tausayin shi ya dan tsirga min a zuciya tunda duk a kaina shima yake samun wanan matsalan da kowa haka a gidan yanzu.
Ban kai ga gama tunane ba sai ga yaran Nuriya din sun shigo da littafi a hannun su sun zo nayi masu assignment din su.
Kwasan su nayi muka koma waje kada mu damu hjy a dakin can lambun gidan muka je muka zauna na fara koya masu sosai nakan ji dadin zama da yaran don sukan sakani a cikin nishadi sosai idan muna tare da su.
Hakan ne ya kasance a wanan lokacin da muke tare da yaran a lambo na shagala sosai ga dariyan yarinyar dake shirin kuka don kawai bata gane me nake tambayan ta ba.
Daga can bangare daya ba tare da sanin mu ba ya jafar ne da zaman daki ya isheshi ya fito don ya sha iska a wajen.
Daga inda muke zaune yake kallon mu don mun masifan burgeshi da dauke mai hankalin don ya kula da abinda ke faruwa a wurin.
Ga yaran duk gaba daya suna zaune ne a saman jikina a hakan nake koyar dasu sai in basu takardan su kwashe akarshe.
Yakai minti biyar a gurin tsaye hankalin shi a garemu yana tunane shi kadai a wurin yana kallon mu ko kyafta idanuwan shi baiyi.
Ganin yarinyar ta tubure da kuka a lokaci guda yasa shi saki zafaffan ajiyan zuciya ya fara takowa zuwa inda muke.
Baiso ya karaso inda muken ba amma sai ya tsunci kanshi da takowa zuwa garemu din gadan gadan zuciyar shi na cike da jin tausayin yar dan uwan shi dayaga tana kuka akan karatu.
Kamar daga sama na tsinkayi muryan ya jafar yana fadin meya sa kuka sakata kuka haka zainab ?
A dan firgice na waigo baya ta inda nake jin muryan shi din yana tsaye ya zura hanayen shi a cikin aljihun wandon shi gami da zubo min idanuwan shi akaina yana son jin amsan da zan bashi.
Ganin yadda na dan dirance da ganin shi a wurin a bazata yasa shi fadin kuyi hakkuri don min naga kamar har yanzu bata gane me kike nufi bane.
Malaman kuma kina ganina kin firgice da ganina yanzu yana fadin hakan ya duka ya dauki yarinyar ya dora a cinyar shi tare da kaiwa zaune a dayan kujeran dake gefen mu, muna fuskantar juna dashi.
Da sauri na janye kaina gefe daya tare da kurawa kasan wurin ido ina jin yadda yake lalashi yarinyar dake jikin nasa.
Ina zaune a cikin tsarguwa sai kace wata gunki a wurin ko kwakwaran motsi ban yarda na karayi ba wurin tunda ya zauna din.
Da kyar ya iya budan bakin shi tare da dago kai yana kallona yace kiyi hakkuri ki kara fahintar da ita yadda zata gane me kike nufi da wanan lissafi din.
Bai tsaya yaji abinda zan fada ba ya jawo kujeran tare da dan matsowa kadan a inda nake zaune.
Na cira kai da sauri na dubeshi babu wasa a fuskan shi don shima ni yake kallo a lokacin.
Tsoro da mamakin shi yadda ya zauna a gurin kuma yake son in koyar da yarinyar tasu ya kamani sai naji ya sake fadin yi mata bayani yadda zata fahinta a yanzu man.
A firgice nace nayi mata tace bata gane bane yaya kiyi mata yanzu zata gane din insha Allahu.
Ba yadda zanyi dashi haka na fara nunawa yarinyar yadda zata gane takuma fahinci abinda nake nufi a cijin lissafin tiryan tiryan nake mata bayanin komai ba tare da na dago kai na dubi inda yake zaune rike da yarinyar ba .
Duk da ban dago kai na kalleshi ba jikina ya bani yana kallona a lokacin har lokacin da yarinyar ta nuna ta fahinta ya saketa tare da umartan ta data rubuta din a nata littafin na karatu.
Hankalin yaran gaba daya ya dauku ga abinda suke rubutawa a lokacin don hankalin su baya kanmu ga baki daya muryan shi ya diro min a kunnuwa na yana fadin.
Zainab tun ranan dana fara jin labarinki nakuma gankii a gidan nan Allah ya jarabce da tausayin ki dakuma kaunar na tallafawa rayuwan ki a cikin harshen turanci yai maganan da kamar bashi yayi shi ba.
Da sauri na dubeshi don maganan nashi tazo min a bazata don ban zata zaimin wani magana makamancin wanan hakan a wanan lokacin ba.
A dab firgice saida na kalli kofan fitowa daga cikin gidan nace a harshen hausa yaya ka rufa min asiri ka barni don Allah hakan da kake nuna min yana jamin matsala a furin mami da sauran mutanen gidan nan.
Ya dan gyara zaman shi sosai ta hanyar yin balanced a saman kujeran da yake zaune akai kafin yace.
Idan na dauke kiki daga gidan nan zaki daina jin tsoron kowa a gidan nan kinga sai ki zauna ke kadai sai wanda kike tare dashi ya fada kai tsaye.
Hannuna na hade guri daya tare da kaiwa kasa a lokaci daya gwiwa bibiyu idanuwana suka kawo ruwa lokaci guda yanayina ya canza a lokaci guda.
Na bude baki a cikin kyarma ina fadin yaya don Allah ka rufa min asiri ka taimaki rayuwana ka tallafamin ina son karatuna ka barni in samu nasaran karasa karatun secondary dina kada mami tayi fushi dani ta koreni a gidan nan.
Sai naga ya mike tsaye zubur jikin shi ya dau kyarma yace look nasan ko waye shiyasa na shirya hakan a kanki.
Ban fito da zancen nan ba saidana gama shirya komai a kanki koda ace ke din baki shirya hakan ba a zuciyar ki ni a shirye nake na shaye duk wani barazanan da wani zai kawo min a wanan zancen.
Na kara fadi cikin razana don Allah yaya ka taimakeni ka rufa min asiri ka rufawa iyayyena da suka turoni don rufin asirin su.
Yai wani murmushi mai dauke da takaici kafin ya sake daure fuskan shi murtuk kamar bai taba murmushi ba a rayuwan shi.
Ya gyara tsayuwan shi tare da tura hannayen shi cikin aljihunshi yai min wani kallo da ba zan iya fassara ko na kiyayya ko na tsana.
Yadubeni da kyau ya kada kai a cikin alaman tambayoyi a fuskan shi tare da kara kallona kafin fadin .
Nima a lokacin tsoro ko shakkun shi ya fita min a rai don abinda naji ya fada na rabani da gidan ya kaini wani wuri da ban sani ba.
Don haka na tsura mai manyan idanuwana da suke min a firgice ina sauraren abinda zai fada min a yadda yayi min nuni a lokacin.
Shima da kyar ya iya tattara courage din shi ya kalleni ya bude bakin nasa yace dani yace haka na tsarawa rayuwan mu hakan kuma zai kasance damu.
Yaya wallahi ban yarda ba ni ban amince ba bana so kuma bantaba yin wani soba ka kyaleni ka barni a yadda ka ganni in samu in kammala karatuna.
Ya kada idanuwan shi tare da rausayasu yana fadin wanan kuma ruwan kine ko ki yarda ko kada ki yarda ba ra,ayin ki nake son ji ba a yanzu so take care as from now.
A hanzarce ya juya ya fara tafiya ya nufi hanyar shiga cikin gidan ta inda muka fito ya shige ya barni rusunne a wurin ina rusa kuka.
Takon Nuriya data fito ina wurin a durkushe take fadin tsiyar banza za a kawo min yara nan azo ana koya masu abinda bai dace ba a rayuwa don tsaban iya iskancin tsiya don ba kwabo ko tsawatawa gare ku.
Wani sabon kuka na kara barkewa dashi lokaci daya ina fadi a cikin kuka ni kan ba yar iska bace bani kuma naje na kira yaran ki zuwa inda nake ba.
Don haka ki daina aibantani da bata min rayuwa don kawai Allah ya kawoni a karkashin ku in zauna zaki ta min kallon wullakantantar matum ko yaushe.
Ta juyo ta kalleni tare da jefamin wani irin wullakantacen kallo mai tattare da tsana da takaicina taja hannun yaranta suka shige ciki.
Nan suka barni a yashe kasa karshe na dora hannuna a saman kai naja kafana daya gama yimin sanyi a lokacin zuwa cikin gidan ina rusa kuka.
Sam ban san yana dakin ba yasa na fada da kuka wiwi sai ganin sa nayi zaune a dakin ya mike kafa suna magana da hjy a dakin.
Lafiya hjy ta fada hankali a tashe tana kallona kokarin juyawa in fita daga dakin nayi don ganin shi a zaune dakin.
Yace ina zaki ba karata kika kawo mata ba a yanzu gani zaune ai saiki fada mata tayi min hukunci a yanzu.
Hjy taja wani dogon tsaki daga inda take zaune kuryan dakin tace yanzu a kan dan wanan maganan yarinyar nan kike wanan kukan haka ?
Kyaleta tayi hjy do ni a shirye nake na jure da duk wani barazana da wullakancin da zaki iya min a yanzu.
Hjy ki rokeshi ya barni hakan hakan ya isa hjy yanzu anty nuriya ta gama kirana da yar iska a kanshi nazo zan iskanta mata diya a gabansu muke iskanci don mu lalata masu yaransu.
A zabure ya fadi what da karfi saida na dan razana na dan ja da baya a daidai lokacin da ya mike tsaye a firgice zai bar dakin.
Yaka zonan kada ka fita dan nan dawo ka zauna wanan yarinyar babu abinda ke damun ta yadda na kula sai kyashi da hassada da bakin ciki a rayuwanta.
Kyashin me hjy ina ruwanta da yarinyar nan tunda ba mijin ta zai zauna da ita ba.
Kai dai ka barta a hakan kamar yadda na fada watarana zakace nace hakan koda bana raye kuwa.
Nasan kai a shirye kake da ka dauki duk wani cin fuska da zaka gani a gidan nan don haka ya saura gareki yanzu ki daure ki amshi zancen yaron nan da hannu bibiyu.
Hjy ba zan iya ba bazan iya jure wanan abinba a barni a yadda Allah ya ajeni tun kan sunana ya kara tashi ga barauniya zuwa yar iska.
Yadda nake magana a wurin ba hjy ba har shi kanshi a lokacin mamakina suke yadda nake fitar da lafazi a bakina babu shayin kowa a wurin.
Duk da suna min kallon mai dauke da ma,anoni a zukatan su hakan baisa na fasa fadan abinda ke a bakina a lokacin ba garesu.
Hjy sai kallon mamaki take watso min tare da tuhumar kodai wanan zancen ya taba min kwakwalwane har na hadu da wani lalura da damuwa ya jawo min.
Idan ba na samu tabuwa ba ko kurciya ta yaya Allah zai ban wanan daman inyi wanan sakarcin da nakeyi haka.
Ya mike duk da hjy ta hane shi da fita daga dakin ya kalleni tare da sakarmin wani malalacin murmushi mai wuyan fassarawa a fuskan shi kafin ya juya ya kalli hjy yana fadin.
Ya kirayi sunan hjy yana fadin ki kyaleta akwai kurciya a tare da ita duk wanan haukan a yanzu baya damuna ko kadan don wata rana bazata so ta tuna hakan ba.
Yana gama fadin hakan yayi hanzarin juyawa ya bar dakin ko juyowa bai karayi ba a lokacin.
Hjy ta bishi da kallo har ya bace mata da gani kafin ta juyo ta mayar da kallon ta gareni a cikin takaici tana fadin kaicon ki yarinya kurciya zai kaiki ga aikata abinda zai dawo ya dame ki a rayuwa da baya.
Tana fadan hakan itama ta juya ta bani baya ba tare data kara kulluni ba taci gaba da harkokin ta a dakin ita kadai ta barni a zaune a guri daya ina zaune a takure a gurin a cikin damuwa.
Ni da kaina sai na tsargu a wurin na shiga tunane da nazari ina neman mafita a kaina da rayuna.
Cikin kankanin lokaci saina tsunci kaina a cikin matsanancin tashin hankali mara misaltuwa ba tare da wani bata lokaci ba na gama yankewa kaina shawaran abinda zan aiwatar a zuciyana.
Don kwakwalwata ya fara hasko min abinda hjy dashi yaya jafar din suke nufi a gareni don rayuwana.
A sannu na fara hasko manufarsu a kaina kan son in amince da zancen da yadda rayuwana dana yan uwana zasu daukaka kamar yadda kullun suke shan fada min.
Tabas nasan ko basu fada aurena dashi kamar yadda yake fada alheri zai zamo min dagani har iyayyena nan gaba din.
To amma duk da hakan zuciyana ta kasa yarda da cewa wai shi yaya jafar so Allah da Annabi ne yake min har kasan zuciyar shi hakan.
Dole sai idan dai yana da wata manufane a zuciyae a kaina idan ba hakan ba ni nasan babu abinda zai kawo ya jafar din wurina da wanan zancen.
Duba da irin rayuwan su da kuma irin yan matan dake hariyar shi a rayuwan shi sam ni din babu ta inda na dace dashi duba da cewa.
Ko hausa sun fadi wutsiyar rakumi tayi nisa da doron kasa don ni din ba sa,an auren shi bace don nasan ya fini ga komai daga kudi ilimi kyau da wayewa.
Tun lokacin da na kula hjy ta fita zance na a gidan sai kuma hakan ya saukar min da damuwa a zuciyana .
Don nasan ni kaina nayiwa tsohuwar cin fuskan da baidace ba duk da kokarin da take min amma a gabanta na bude baki nake fada mata bana kaunar jikanta jinin ta.
Sai bayan sallah magariba ban yarda har lokacin na fito daga dakin ba daga sallah sai kwanci da nakeyi ina faman tunane barkatai a raina .
Ina zaune a cikkn muzanta bani baya da hjy tayi tun safe har dare ba tare data kara kulani ba har abin yana son ya zama min ciwo a zuciyana.
Saida na bari ta idar da sallah ta zauna cin abinci na taso daga inda nake nazo mannin ta na dan tsuguna tare da kiran sunan ta da hjy.
Ta dago kai fuska ba yabo ba fallasa ta dubeni kafin ta mayar da hankalinta ga abinda takeyi tace ina sauraren ki.
Sai kuma yadda tayi min din ya kara sani muzanta a gurin a dan maraice nake fadin kiyi hakkuri ki yafe min idan na bata maki ba zan kara maki hakan ba idan Allah ya yarda zaki sameni da maki biyayya a koyau.
Ban yarda ba hjy ta fada har lokacin bata dago kai ta kalleni ba taci gaba da cin abincin ta hankali kwance kamar bana a wurin.
Kiyi hakkuri hjy na sake fada hawaye na zubo min a cikin muryan kuka da nadama lokaci guda don na gama fahinta da tsohuwar ta hau sama dani a zuciyar ta.
Kinga jeki ya wuce a gareni duk da ta sallameni na dade a gurfane gefen kafin in daga na koma na rakube gefe daya a cikin damuwa.
Washe gari ma har na fita zuwa makaranta muna a halin da muke ciki da hjy babu wani sakin jiki a tsakanin mu dakin.
Kwana biyu da faruwan hakan ina dari dari da kowa a gidan ko me hjy ta gani ranan ina zaune nayi shiru saman kujera .
Naji hjy na fadin me ke faruwa ne dake haka kwanan nan yar nan kina kokarin susuta kanki a banza lokaci guda ina hankalce dake ko abinci baki son ci a gidan nan.
Na girgiza kaina cikin mamaki nake fadin banu komai hjy.
Hjy tace ban yarda ba ta yaya zakice dani babu komai bayan ina kallin ki a cikin damuwa haka ?
Ai duk mahalunkin mamalaki daya dubi yanayin ki da fuskan ki a yan kwanakin nan yasan akwai damuwa a tare dake sai dai idan boyewa kike son min.
Hjy ba komai saidai banjin dadin yadda kema kike fushi kamar yadda mami keyi dani akan laifin daba ni na kawo hakan ba akaina.
Baki daukan shawara ne yarnan a rayuwana nafi son mutum ya tsaya a inda na ajeshi kina ganin da tsufana za a hada kai dani a cuce ki idan ban tallafa maki ba.
Da sauri na girgiza kaina ina fadin hjy ba hakan a cikin zuciyana ko kadan nasan kina hakane garemu dan raimakawa rayuwan mu ga baki daya na fada a sanyayye cikin muryan dake shirin kuka.
Kinga wanan kukan ya isa haka yanzu taki kwantar da hankalin ki mu masu taimakon kine ba masu cutar dake ba.
Na tsaya inga wanan abin ya tabbata a tsakanin ku don ni nan na tsukayi wani abinda sai kece zaki iya hakkurin jure irin sa.
Wanda uwarshi ta kasa hango komai ga nufin yaron nan ya fada ba sau daya ba a gabanta da cewa din karinya da wani manufa ya zabi hakan a gareshi.
Da sauri na dago kai na kalli hjy daga inda nake tace kwarai jikata yaudai zan fada maki gaskiya a gidan nan.
Duk wani abinda iyami zatai maki ki daure ki fitar da mu akan wanan sarkakken abin da yake a cikin duhu wanda wani sirine dake rufe a duhu wanda Allah kadai yasan dalilin hakan a gareku.
Sai dai zan shawarceki duk ritsi duk wahala kada ki yarda ki fitar da wana zancen don idan zaka sadaukar da rayuwan ka ga wani ba sai maishi yasan da haka ba.
Don wanan abinda kike shirin yi zakiyi ne akan Iyakin da yanzu take wanan haukan a kanku don, , , ,
Sallaman wata mace ce da ta shigo dakin da abinci ta ta dire a gaban hjy ya hanata yin magana naji hjy na fadin wani abincin aka sakw girkawa ko me ?
Wanan ba abinci ba ta fada a cikin wani hausa dayasa saida na dago kai na sakw duban matan don na fahinci ita din yar garin abujane irin gwarawan nasu.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.