Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 28 of 139

Nikan unda na shige daki nabar mami na fada a falo ban fito ba sai bayan sallah isha,i koshi din abinci na fito.
A falo gaba dayan su suke in ka debe mazan da basu rigada sun shigo gidan bako a lokacin don ko hjy a falon tayi sallah bata shigo dakin tayi ba nasan saboda tafiyan ne yasa ta zauna a nan bata dawo dakin tayi sallah ba.
Banda hara ba abindaya shiga tsakanina dasu Rufaida duk da na gashesu a cikin jam,i saidai su basu amsa min ba.
Sai hjy ce ke fadin yarnan yanzu nake zancen ki a raina ina batun aje a dubo min ke a daki ko lafiya kika shige har wanan lokacin ?
Ina zancen dai ai ya wuce tunda kinji uwar ku ta tsawata kan hakan suma kina ganin su da shegen son jiki suke ta yaya zaki dauki kayan kasan ki har kiba wata wanki can.
Haba haba hjy a daina wanan zancen tunda mami tayi mana fada a kanshi dazu ba wanda zai kara bata irin wanan aikin acikkn mu ai tunda mami ta hana abata Aisha ke fadi.
To uwata hanani in fadi tunda kun shuka rashin gaskiya wa yarinya baku son a fada kuma kai kuma dai kazamai ne wallahi.
Ta fada rai a bace tana mai kawar da kanta ga kallon su sukai tsuru tsuru don mami na falon itama ta kafesu da idanu.
Rufaida na shirin mikewa tabar falon don takai kololuwar cika tana batsewa wai akan yar aiki mami tana wullakantasu don kawai taga gidanta ne yanzu dan uwan mahaifin su ya rasu yasa ake masu hakan.
Batakai ga tashi ba taji sallaman jalal yana washe baki ya shigo da ledoji niki niki a hannayen shi yakai gaban mami ya aje lodojin yana zama a kujera tare da fadin.
Wassh Allah yau na gaji da yawa mami tace da kai me ke nan fa mami tunda aka fito daga sallah yaya jack , , , ,
Bai karasa fadi ba saboda hararan da mami ta watsa mai yasan me take hararan shi dashi yace a wani yanayi i am sorry mami na mantane kin hana mu kirasa hakan ni kuma bakina ya saba da hakan tun a can.
Rufamin baki ku kun fada inagana waje jalal ka fita min a ido duk kuka bari wanan sunan ya shigo kasan nan raku saiya baci sosai.
Yana dariya yace yanzu dai mami ba wanan ba kinga ledan nan wai duk na tsohuwar nan ne yaya ya ban kudi a hado mata wai kada taci abinci da dare sai wanan din shi ya dauka nan irin can ne da tsofi sukecin wanan dadin yana magana yana zamowa daga saman kujeran yana kokarin budan ledan.
Wanan ya hana rufaida dake cika tana batsewa tashi don tun shigowan shi falon ya dume da kamahin suya irin na yan gayu ba suya na gida ba wanda yasha kayan hadin sanadarin zamani.
Hannun shi mami ta buge ya jaye yana fadin wassh Allah mami zan bude ku gani ne ai ko ya fada yana dariya.
Mikawa hjy abinta babu maici a cikin ku wurin sai idan ta gama ta baku ragowa idan zaku ci.
Haba mami ta bamu ragowan ta kuma bayan ta gama zuba mai miyau da goro zamuci salma ta fada tana kallon mami din.
Hjy da sai yanzu ta fahinci me ake nufi lokacin da mami ke kallon jalal tana fadin ya mikamata take fadin au me muka samu ne wai.
Bakiji bane hjy wai Jafar ne yasa a sayo maki wanan shine syke son su saka maki rani a ciki don suna yan kwadai.
Ja,irin miskili ya gama babautan nasa yana neman shiri danine kuma yanzu dazun fa ya gama fadin me na biyo ku yi nan nazo in sakawa mutane nauyina sai gashi shiya fara daukan nauyin kuma ?
Haka kika fada ko bari ya dawo saina fada mai wai badan Allah ya saya maki ba neman shiri dake yake ya sayo maki.
Kaji ja,ira zaki hadani fada da wanan mai kama da yan ruwa yazo ya hanani shanruwa a gidan nan ke nan.
Ya jalal yaga sun tsaya surutu mami bata sab sanda ya jawo ledan ba yana fadin bari nidai na bude don inyai sanyi bana iya cinsa kuma.
Yana bude ledan farko wani kanshi ne duk ya game wurin leda daya ya tura a gaban yan mata yana fadin ku ku dau wanan wanan kuma hjy wanan nasu ne idan sun shigo.
Ya mike ya isa gaban tsohuwar tare da ledojin a hannun shi yana fadin hjy mu muci wanan ko tace kaidawa ke nan miko min nan dagani sai yar nan da take dawainiya dani zancisa.
Kaji hjy kuma ya wuce ki bata fifike ne a ciki kilama bata taba cin suya irin wanan ba ai Nazira ta fada a daidai lokacin da suke shigowa gidan shida Jamal.
Yau kan ya wanke kanshi a wurin tsohuwar da murna da lale marhabin ta tare shi tana fadin kaga mijin arziki wanda yasan zafin iyalin shi.
Mami na masu dariya yazo gaban mami ya dan dukar da kanshi wanda kamar hakan al,adan yayan mami ne don har ya mamud haka yake mata da girman sa in zai fita ko ya shigo zai duka mami ta ahafa kansu tana saka masu albarka tare da fatan alheri a garesu.
Don tun ina mamakin hakan har nagaji don na saba da ganin hakan wurin yayan gidan maza ko Aisha da take mace kamar zata koma cikin uwar wani lokaci idan abin ya motsa mata ko yanzu tana zaune tunda tai magana da farko bata kara magana ba a wurin kowan su nakan waya suna abu daya charting ko dawa soke yi oho ?
My friend an dawo ke nan mami ta fada tana shafa kanshi tare da fadin ubangiji yayi maku albarka ya kare mun ku a duk inda kuka saka kafanku.
Tashi yayi ya nufi wurin hjy ya zauna a kasan carpet tare da riko hannun da ta dauki cinyar kaza tana ci yakai a bakin shi ya gutsura kadan kafin ya kai mata itama a bakinta .
Ni dai ina gefe zaune a kasa daga gefen hjyn ina kallon ikon Allah tare da mamin wai yan gidan mami suke kwadayin nama haka ?
Wanda nama sai an mayar da saura kitchen don sunci ya ishesu wanan wani irin nama ne hakan don idan kaga mami ta sayo nama a waje to kilishi ne zata shigo dashi mai yawa kowa yaci har a ture saura su mama kande su dauka..
Dan albarka hjy ta fada tana hadiyan naman dayasa mata a bakinta ta gutsura kowa falon na busy suna cin naman suke gaidashi dashi.
Dabi,an shine kyaluwa dan haka yi yayi kamar baiji su ba hjy ta juyo tana fadin taso mana yar nan ki diba kinyi zaune kina kallon kowa nacin abin arziki.
Saiya dan juyo ya kalleni guri da nake zaune din ya kawar da kanshi kamar ba kowa a wurin .
Na mike nazo gaban hjy din yana zaune har lokacin yayi rigingine a wurin kafanta idon shi a carpet nakai hannu zan diba Nazira tace
Ke dakata don Allah menene haka zaki saka mata wanan hannun naki mai dauda a cikin abu haka kai tsaye ba tare da kin wanke hannu ba.
Cak na tsaya daga daukan naman da nasoyi din ina kokarin mikewa a inda nake gurfane don barin wurin.
Ke diba ki wuce ya fada batare daya dago kai ya kalli kowa a wurun ba ya fadi hakan sai jamal yake fadin haba Nazira ku daina irin hakan don Allah dai.
Bazasu bari ba don da zasu bari ko ance suyi wani abu kan yarinyar nan ai basuyi ba kuma yadda nayi masu yau.
Me ake mata idan ba iya yinta ba taga yan aiki a wurin nan ne ko taga su kande na zama a cikin mune haka su ?
Nazira zan saba maki a gidan nan fiye da tsamanin ki to bari kiji zeey da kike gani daya kuke da ita a gidan nan yadda na daukeku dasu Aisha haka itama nake daukanta don ba wai aikin kudi aka kawota yiba yadda kuke tsammani.
Rokota nayi gurin iyayyen ta suka taimaka min suka ban ita a cikin mutunci sau nawa wai kuke son in fada maku hakane wai ?
Look akan yarinyar nan zan sabawa yarinya a cikin gidan nan ko wacece me yarinyar nan ta tsare makune wai haka kuke sakata a gaba ko yaushe ya fada a hasale cikin daga muryan shi dasai ranshi ya baci akejin shi irin hakan.
May be don sunga ta fisu kyaune da tsari suke kyashin ta jalal sarkin barkwanci ya fada kai tsaye yana masu dariyan kyaita.
Kai amma jalal din din don Allah kada tasa taji dadi har taji dadin raina mutane a gidan nan ta dauka wani kyaune da ita.
Garin dauko naman saboda rawan da jikina keyi na dauko gefen fifiken kazan dayasha carbej da albasa dasu maggi curry da sauran hadi namike tsohuwar na fadin baki dauki abin kwarai ba nace wanan yayi min yanzu naci abinci na bar falon ga baki daya har lokacin jamal da jalal suna cacakan ya matan a kaina.
Jalal ke fadin wanan kina ganita idan tayi clean gidan nan ma baya daukanta ke zeey fa idan ta waye ba karamar classic lady bace wurin nan.
Dakin na shiga na aje naman don naji ya fita min a rai don disganin da nazira tayi wurin daukan naman a gaban kowa.
Nima fa mutum ce kamar kowa da suke min haka don kawai ina yar kauye kuma diyar tallaka tallakama mai faci.
Ina ban daki nake wanan fadan a raina na fito ban tsaya jiran komai ba na hau kujera na kwanta har barci ya daukeni ban sani ba don ban san lokacin da hjy ta shigo dakin ba bayan sun gama hiran su a falon don ko hidimar da nakewa mami ranan ban samu yimata shi ba.
Koda mami ta rako hjy dakin ta samu ina barci bata tayar dani ba ta kyaleni hakana sai cikin dare dana falkone naga wutan dakin a kashe.
Washe gari da safema motsin hjy ce ya falkar dani na tashi nima nayi sallah na idar na zauna a wurin hjy ta shafa tana fadin in koma in kwanta tunda ido akwai barci daga haka taci gaba dajan tasbahan ta.
A daidai lokacin da nake shiga na gyarawa mami dakina falka kamar an tasheni har lokacin tsohuwar tana zaune a inda take.
Mikewa nayi ba tare danayi magana ba na nufi dakin mami din ko a nan ma itama zaune take tana azzakar din safiya.
Ban fito daga dakin ba saidana karasa komai na dawo na samu hjy ta dan kwanta a lokacin banyi dogon motsi ba wanka nayi tare da kara wanke ban dakin har na shirya a hankali duk tsohuwar tana barcin safe wanda nasan na gajiyane.
Sai bayan goma da rabi ta falka lokacin mami tayi mayawa a dakin yakai sau uku tana duba mahaifiyar nata.
Ruwan wanka na hada mata tayi wanka na taimaka mata data fito har ta shirya saiga abin karyawa an kawo mata har daki yaran gidan suna shigowa daya bayan daya suna gaida ita da kwana.
Har suka dauke kafansu sai Aishace bata shigoba nasan bata tashi bane don ita sai wuraren sha biyun rana dama take tashi barcin safe ko ma zuwa dayan rana.
Nan muka zauna muna hira da hjy don ban yarda na fita ba ko karyawa a cikin na tsohuwar na karya dashi take tambayana ni yar wani garine ?
Nace ancau hjy tace ashema yar jaharnan ce ke na dauka ko yar shiyan jalingone ke ko bauchin don na ganki da zubin fulani.
Nace innatace dai bafullata Abban kuma bazzagene shi yar nan da asalin ki haka har yaran nan suke maki wanan tsiyar haka ?

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.