Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 56 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4ï¸Â⃣7ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA ALLAHUMA AMIN, , ,
Duk yada naso na boye damuwana a lokacin nayi iya kokari wurin boye hakan saidai hakan bai samu ba don saida maizube ta fahinci hakan a tare dani .
Sai gashi ta koma lalashina wai a zaton ta saboda tafiyan ya jafar dinnne nake haka idanuwa da suka hau saboda kukan nadama danayi a lokacine.
Ba komai yasani wanan kukan ba sai fahintar inda na jefa rayuwata dan kawai tausayi da biyayya ga ya jafar din da yake zaton don deal din shine na yarda dashi da bukatan shi gareni.
Saidai kuma a yanzu kalaman shi sun fara jefani rudani don ban san a matayin da nake a garshi ba da wanan tunanen ya barni a gidan suka daga zuwa inda yake aiki.
Ranan kan mami tayi fushi sosai Allah ya taimaka a gaban hjyn taya kira yana sheda mata zancen tafiyan shi inda ta haushi da sababi saidai ta makara ga hakan don yana shiga jirgine ya kirata.
A zaton mami din tare dani ya wuce don idonta ya rufe a wurin har take ikirarin da sai dole ya dawo dani kasan nan inma don hakan ne ya guje mata din.
Aikin ma gaba daya zai bar can ne ya dawo nan kasan kusa da ita inda take iya ganin komai da yakeyi din a gabanta.
Saidai mami bata san da ta makaro ga hakan ba gareshi don a yanzu kan ba zata iya taro dan nata ba kai tsaye yadda take so din tayi.
Wai ke iyami yaushe kika koma hakane hjy ta fada a hasale daga gefenta ta dora da fadin zaki raba auren da Allah ya nufa sai anyi a tsakanin su ne ko me ?
Ta dago don fadin abinda ke a ranta hjy ta katse ta da fadin yadda kike zaton zaki iya yiwa danki baki ko ki tilasta shi ya saki yarinyar nan.
Ki tuna nima hakan ina da hakkin da zan tursasa ki a kanshi dan ni dince dai na haife ki ai .
Hjy yarinyar nan bawai sonta yake ba ko wani abu shima dole da akwai abinda yake nufi da yin hakan a zuciyar shi tunda bawai sone ya hadasu ba ai.
Iyami bana sonki da shiga tsakanin yaran nan wallahi wararana kunyan hakan zakiji da kin daure kinba yaran nan goyon baya a yadda yakeson abinsa .
Da Komai da zaiyi ai dole ya fada maki ko ya sanar dake amma zuciyar ki yana rudin ki kin hana kanki sakat da nasu haka .
Karfi da yaji kin hana yaron nan ya zauna ya huta a zuciyar shi balle kiji sirin zuciyar shi kinsan irin illan da kike jawa kanki ga yin hakan da kikeyi kuwa.
To idan ma har baki sani ba gara ki san abinda kikeyi ki bar yaran nan hakana idan ko kinki kin tsaya kina jayayya da ubangiji ne .
Sai Allah ya dauke ki a zauna lafiya ayi kuma bada ke din ba kinga sanadin hakan sai sauran diyan naki su zauna a marayu ke nan ba uwa ba uba garesu kuma.
Ina kema idan har talaucin yarinyar nan ne damuwan ki a haka uvan yaran nan ya aureki baki da komai a tare dake ilimin ma a gidan sa duka kika same shi ai.
Jikin mami yai sanyi ga abinda hjy ta fada dan tabbas kawar da ita din ba komai bane a gurin ubangiji ai.
Ganin tayi shiru hjy taci gaba da mata nasiha sossi inda take fadin ki kyakeshi da abinsa inma har akwai abinda yake nufi da hakan ai lokaci zai fadi hakan ga kowa.
Jalal da yanzu ya zama dan gaban goshin ta yana zaune a gefe yace mami gaskiya hjy ta fada ya j ai ba yaro bane yanzu.
Yana da right din da zai zabawa kansa abinda duk ya dace dashi kuma ai kinji hjy ta fada kila daddy mu ya biyo a wurin zabe shima.
Ran kwashi takai mai saida ya dafe wurin don zaifi tare da fadin aini na bar wanan zancen yanzu tunda na gane gaba daya kuna goyon bayan sa a yanzu kan hakan tunda yanuna maku yana da kudi da zai iya yin komai.
Ni kuma wallahi bana rsoro ko shakkar sa idan da ya biyo ta hanyar arziki dani zai iya hakkura dashi a hakan yaje yayi abinda yake so din ai duniyace dai ko , ?
Baki zaki masa ya kara lalacewa ko mai idan ma kin masa din dake dashi duniya zata zaga ai hjy ta kare magana a cikin zafin rai.
Har suka dawo abuja mami bata kara tayar da zancen komai akan da nata ba ko ni do tana zaton tare muka tafi dashi hakan yasa fushinta ya kara karuwa a zuciyar ta saidai batayi zancen da kowa ba kuma.
Sannu a hankali muka fara sakewa da wanan matar da ta gabatar muna da sunan ta da anty Fadila kamar yadda muke kiranta dashi.
Don da safe zata shigo har dakin da muke su gaisa da maizube ta dan ja halimatu da fira tun bamu sakewa har muka fara sakewa da ita a yinin farko da mukayi tare a gidan.
Sai ya kasance duk abinda zatayi zata kirani muyishi a tare da ita a cikkn sakewa da kulawa kamar uwar da ke koyar da yarta wani ilimi na duniya a yanzu.
A cikin hikima da basira take koyar dani zaman duniya da tako aka komai da rashin saka ido ga wani ko wani abinda bai shafeni ba can zamu zauna tana da bamu labari da zai dauke muna hankali ga komai.
Sai gashi mun dan sake da ita har ina iya tambayan ta abinda ya dan shige min duhu wani lokaci tayi min bayani akan komai .
Tun Saturday ta kaimu saloon aka wanke min kai akai kitso shiga school monday driver ya kaimu school don fara shirin jerabawa.
A school di muka hade da yaran ya mamud wanda a wuri su ne mami ta samu labarin ina kasan bai tafi dani ba ashe .
Tayi mamaki matuka don jin hakan koda ta tura ai mata bincike sai ta gane ina zama da fadila ce inda ta zaci ko wani alakane a tsakanin mu bata danta bane ya hada mu.
Inda ta gano ko waye Fadilan da kuma aikinta saidai ta kasa fahintar komai ta kawo ido ta saka a hakan don nasihan da hjyn ta tayi mata a kanmu.
Wanda nasan Allah ne ya dorani a kan mami din ta basar da zancen binciken komai a kaina har na samu daman fara jerabawa hankali kwance.
Yanzu kan ina waya da innar mu tun zuwan mu sabanin da cab da dif idan mun tafi har take fafa muna ginan da akayi a gefen gidan mu itace ashe aka ginawa gidan da zata zauna a ciki.
Inda sa,adatu take labaranta muna abinda ya faru bayan angama aikin ginan dayasa a ginawa innan mu sai lantana ta fara bala,i akan bata yarda da hakan ba dole sai Abban mu ya san yadda za a yi itama ta shiga ko a gina mata nata sashen da zata shiga.
Wani wan mahaifin mu kuma makwabcin mu ya fito yana fadin baki isa ba lantana don arzikin yartane ya kaita ga hakan don babu abinda baki fada akan tafiyan wanan yarinyar birni.
Yanzu da tafiyan ya kai ga alheri gare ta zaki fito kice ke baki yarda da hakan ba dole sai mijin ku ya dauki mataki a kan hakan wani irin mataki kike son ya dauka kan haka din a yanzu ?
Ko so kike yace ba zata shiga ginan da arzikin haihuwan ta ya jawo mata ba ta dalilin diyar ta data haifa .
Yanzu sai kije can ke mai haihuwan diya maza ki jira su girma kema su gina maki naki ai don Allah ba ai mashi ganganci ga hukumcin sa.
Idona ya kawo ruwa lokaci guda da take muna wanan bayanin ban karasa sauraren abinda take fada ba na kashe wayan .
Zama nayi cike da nazarin wanan abinda ya faru da innan mu din wanda a sanadiyan na da abindana jefa kaina a cikin sa wanda bansan ko me hakan ke nufi ba har yakai innan mu din ta fara samun saukin rayuwa a tare da ita.
Don haka ya zama min dole in jure duk wani kalubalin rayuwan gidan dan mami dana mami din a yanzu tunda har na gano hakan zai iya haifarwa mahaifiyata da yan uwana da zaman lafiya a rayuwan ta.
Karatuna nake sosai kuma ina fahintar hakan don bamu tare da wani mstsalan komai a tare damu a gidan zaman kadaicine kuma wanan Fadila din tana iya kokarin ta wurin ganin bamu shiga damuwa da komai a gidan.
A haka har Allah ya taimaka na gama zana waec dina muka zauna jiran zana neco din mu wanda a lokacin ne na samu dan natsuwa sosai tare da maizube da halimatu da yanzu itama take zuwa makaranta tare dani.
Na mayar da hankali sosai wurin koyon girki tare da anty fadila da sauran abubuwan da take koya min na zaman duniya a cikin hikima da basira .
Zakace ya da kanwa muke da ita a yadda nakan bata girma da kuma daraja sai hakan ya kara sawa matar sona a ranta sosai.
Don a yanzu mun sake da juna zata fada min kai tsaye idan nayi wani abinda ba daidai ko bai dace nayi shi ba a take zata tsawata min kan hakan a karshe kuma in bata hakkuri.
Sai ya kasance a dan watannin da mukayi da ita wani irin sabo da shakuwane ya shiga tsakani mu sosai har yakai ranan take tambayana labarina ?
Sai kawai na danyi murmushi ba tare dana furta komai ba a hakan muka bar zancen ba tare dana fada mata komai ba.
Da yake ita din mace wayayyiya a cikin hikima irin nasu nasu na manyan mata take dan tambayana wasu abubuwan a cikin hikima har take samun amsa daga gareni.
Take kuma sakani a hanya yadda zan kula da komai da zaizo min a bazata daga ko wani bangare.
Yau ban tun safe ban leka falon ba ina daki kwance na tashi sa ciwon mara wanda kan dameni duk karshen wata.
Har daki anty Fadila ta kawo min magani nasha wanda hakan ya sakani barci bayan nasha magani sai bayan karde hudu na samu fitowa falo na zauna.
Bandade da zama a falon ba halima ta shigo dauke da ledan corn a hannunta tana ci ta samu wuri a gefena takai zaune.
Na dago kai na kalleta ina mamakin ta a raina ban kaiga karshen mamakin ba ta jefo min tambaya tana fadin wai anty sai yaushe zamu tafi gaida hjyn ki sa kike aiki a gidan ta.
Gabana ya fadi don jin abinda ta fada saida na tattaro dauriya a raina kafin ince da ita kin santane ko wani abin kike son yi a gidan nata ?
Kai ta gyada min alaman a,a tare da shan jinin jikin ta a yadda na bata amsa din cikin bacin rai don bansan zancen gidan mami duk da ina kwana ina wuni da zancen mami din a raina.
A hankali na zame na kai kwance daga inda nake zaune tsaban tunane sai kawai naji hawaye suna zubo min ba tare da nasan zuwan su ba.
Dafanin da akayine yasa na dago kai anty fadilace a tsaye kaina tana kallona yadda hawaye ya bata mun fuska lokaci guda.
Badai ciwon bane har yanzu ta fada a cikin kullawa tana zama a gefena tare da mayar da hankalinta gareni.
Kafin in bata amsa halimatu dake gefena take fadin yayan mu bansan ranki zai baci ba da bance muje gidan hjy din ba .
Wace hajiyan anty fadila ta tambaya da mamaki a fuskanta a hankali na amsa da mami mahaifiyar ya Jafar.
Anty fadila tace kan me kukai zancen ta har ya kawo wanan hawayen haka ?
Bazaki ba tunda tun farko ta nuna bata kaunar ki da danta kina garin nan kuma ta sani bata nuna kulawanta kan danta ya barki amana a gurin su ba maizube ke fadi daga bayan mu.
Don haka ki nisanci su kamar yadda suka nisance ki a yanzu saboda da talaucin ki ko rashin gata ta nuna bata kaunar danki dake dafarko .
Sai yanzu kuma ke zaki kwashi kafan ki zuwa gidan ta ko zaki kai kanki ne su kara wullakantaki a can .
Ki zauna a matsayin da Allah ya ajeki gidan nan ki bi umurnin mijin ki har sai idan shi ya furta zuwan ki gidan dan mahaifiya ba wasa bace ai amma yanzu kan babu inda zaku tafi gaskiya.
Maizube nima bance zan tafi gidan mami ba a yanzu don nasan mami har yanzu tana rike dani a zuciyar ta.
Duk da ba zan iya matawa da alherin ta a garni ba har gobe don ta dalilinta har na kai hakan a yau da sunan auren danta a kaina.
Maizube tace dani ato ki daiyi wa kanki fada don babu inda zaki tafi don ni bazan zama babban kwabo ba a cikin ku duk da muke matalauta muna rike da mutuncin mu a idon kowa.
Murmushi Fadila tayi tare da fadin hjy maizube ba a hakan ai idan ma har zasu tafi din aiba haka kawai zamu barsu su kadai din su tafi ba dole saida shirin hakan ko ?
Maganin dai kar ayi kar a soma dan ba a san da wace zata tare su ba abar zancen nan har wanda take zama don shi ya dawo kasan nan inma zuwan ne sai su tafi tare dashi din zaifi.
Jinsu kawai nake yi don sam ban amince da zuwan ba nikaina a lokacin don nagama tsiracewa da mami din yadda muka bar gidan tare da hjy a yadda tayi min koran kare a gidan ta harta amince da mahaifiyar ta tabar gidan donni.
Wanan zancen da akayi a gaban Fadila yasa ta dauki wani haske a cikin zancen sai da muka zauna daga ni sai ita take kara tambayana abinda ya faru a tsakanina da mami din.
Shiru nayi na dan lokaci kamar mai tunanen wani abu sai can naji tana fadin zanso nasan wani abu daga bakin ki duk dana dade da gano komai amma zanso ji dafa gare ki din yanzu.
Wani tsorone ya lullubeni lokaci guda na janye na dauki hannuna na dora a fuskana kafi in sauke na dukar dakai na kasa.
Karo na biyu ta koma kiran tana fadin kina jina kada ki boye min komai ki daukeni kamar yar uwa a gareki don ni din a yanzu mai taimakon ki ne zainab.
Wani sanyi naji a raina tare da yarda da ita lokaci guda duk da
Banso fada mata komai ba amma ya zama dole ta danji wani abu a gurguje na dan fada mata saidai ba duka ba don ban san yadda zata dauki zancen ba a ranta.
Bakina ta zubawa ido har na kare na kare fadan abinda zan iya fada mata na zamana da mami da haduwan mu da ya jafar din a gidan mami har na kare sai tace.
Zainab yau zan baki shawara kamar yarda ya da diyarta zata bata shawara ya amfaneta.
Tagumi nayi ina sauraren abunda zata fada min din a lokacin ita kuma taci gaba da kawo min misali na zamantakewa da mutane a duniya.
Yadda mama maizube take nufin kiyi danzun nake ganin bashine mafita ba gareki zainab don ko yaya suka samu matsala a kanki da mahaifiyar shi ki tunafa uwa uwace a gare shi.
Duk yadda kika dauka da zafi ko iyayyen ki suka dauka hakan ba zai taba mashi dadi ba a ranshi duk ko yadda yake sonki.
A sake na ce yanzu yaya zanyi anty don mami ba zata taba yarda dani ba a cikin a halin ta ni kuma na sani auren nan namu nadan lokaci ne dashi.
Tsaki taja tana fadin ki bar wanan zancen do Allah kefa mace ce zainab duk wani abu da ake bukata a mace kina dashi zainab lokacine kawai zai nuna hakan akan ku.
Kedai kawai yanzu duk abinda nake koyar dake ki maida hankalinki ki koya do zama daku na dan lokacine da zaran contrac dina ya kare daku tafiya zanyi in barku a gidan nan.
Yanzu lanbanta zamu nema zaki dinga tura mata sakon gaisuwa da girmawa tare da nuna mata ke din yace a gareta har gobe.
Ya zama dole ki koyi halin kissa da kisisina irin na mata masu son kama gidan su a hannun su yanzu .
Ta yadda zaki iya tunkaran kowa da wanan kalubalin dake gaban ki domin yanzu sai da wanan akan samu riban rayuwa mai dorewa wanan sanyin ba zai kaiki ko ina ba a rayuwa.
Rashin wayen ki ko sanin duniya zai iya haifar da komai a kanki har aci galaba akanki a cikin sauki don wanan shirun da kike ganin tayi irin su hjy da abinda take shiryawa a hakan.
Da sauri na dago kai don jin abinda ta fada din nace amma anty ta yaya kamata zan iya ja da mami matar da ta kafu da komai akan danta dama kowa ?
Murmushi tayi tare da fadin kina kwankwanton hakan ne zainab ai tun damazo gidan nan na fahinci akwai wata a kasa tsakani ku.
Naso tafiyan ya tafi a hakan inyi aikina in wuce saidai ke din yarinyace mai saurin shiga ran mutum a lokaci daya saboda halinki na sayi da girmamawa ga kowa don baki dauki duniya da zafi ba a yadda na fahince ki.
Don hakane ma kike ganin har abinda ba a ssni na koyar dake ba nake kokarin koya maki don na taimakawa rayuwan ki.
A sanyayye nace anty nagode da wanan taimakon naki gareni in Allah ya yarda zaki sameni da amfani da duk abinda kika koyar dani insha Allahu.
Tayi murmushi tana fadin ya zama dole in taimaka maki zainab don nasan wata rana hakan zai min dadi nima a rayuwana.
Kin ganni nan nasan halin maza kamar yunwar cikkna ina da yara biyu na barsu badan naso ba saboda halin da namiji a yau.
Don haka ba zanga wata mace yar uwana zata fada a halaka ba in barta ta dandani irin ukubar dana sha a baya.
Sau nawa ya kiraki a waya tun bayan tafiyan shi ta jefo min tambayan da ban zata ba a lokacin da sauri na dago kai ina tunanen hakan ?
Bai kirani ba anty na bata amsa kai tsaye do babu zancen boyo yanzu a tsakanin mu kuma tunda ta fahinci komai.
Zai kiraki naji ta fada idan mun fara dana masa tarkon muna mata ai idab yasan wata baisan wata ba zamuyi mai karya baki da lafiya zai zo idan har kina da muhinmanci a rayuwan shi .
Saidai zaki bani goyon baya zaki koma ki kwanta ciwon na kwana biyu do wanan kanwar taki mai shegen surutun tsiya zai iya tambayan ta idan hakan gaskiyane kin sani.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.