Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 126 of 139

ZAINAB IDRIS MAKAWAAWAFATAN ALHERI GARE KU DUKKA MASOYANA NAGAISHE TARE DA FATAN NASARA GA DUKKAN AL,AMURAN KU NA YAU DA KULLUN, , ,

KISAYA YAR UWA KI KARANTA A CIKIN LAMUNA KADA KIJI KYASHIN BIYAN DARI UKU DON KARUWAN DA ZAKI SAMU A CIKI YAFI KARFIN HAKAN ALLAH YASA MU GANE HAKAN AMIN, , , ,

A rude suke sama kaina saida likita ya zo ya rokesu dasu fice a dakin su dubani suka fara fita daya bayan daya tare da tarin tambayoyi a zukatan su.
A bangaren ya jafar sai fuci yake yana fitar da iska a baki da hanci don takaici irin yadda yake ji a zuciyan shi lokacin don yasan abinda ke damuna a lokacin.
A bangaren mami kuma ita a nata zaton tunane takeyi kodai jafar din ya samu lafiyan da har na samu ciki a yanzu ne .
Hakama yan uwanshi da suka san da zancen suke zargi suma sai dai ya jamal ne da hankalin shi bai kwanta ba sam don zargin bai dauke shi da muhinmanci ba sam.
A karshe fita yaya jafar din yayi zuwa bayan don yai waya a kuma daidai lokacin Aisha taji tausayin sadiyana dake ta rusan kuka ta jata zuwa bayan.
Da farko bata dauka shi bane yana fadin na fada maku tun farko kada ku taba min yarinyar nan kuma kun sani.
Ta dan dago daga inda take zaune ta hango shi din daine ke magana a waya a hasale saidai bata san da wanda yake wayan ba a lokacin .
Yaci gaba da fadin duk wanda ya tabi lafiyan ta na rantse maku gaba daya dangin shi sai naga bayan su haka yai ta fadin maganganu kafin ya juya ya bar wurin bayab ya kashe wayan nasa.
Jinkin kanwar tasa Aisha har wani irin bari yake a lokacin ta mike tsam tare da jan hannun sadiya suka bar wurin ta hanyar canza hanya.
Kasa zama tayi asibitin take cewa mami ita zata koma gida a lokacin mami tayi mamakin hakan kuma ga yar nata a rude yanayin ta ya canza lokaci guda sai ta dauki hakan ga tsorone kawai yasata hakan yadda ta ga nayi a gaban su.
Har ta fara tafiya ta juyo tana fadin mami kema zanso kizo muje gida akwai abinda nake so zan fada maki .
Aisha kanki daya kuwa ya zan bar asibitu muna cikin wanan halin haka ai saiki sa a zageni idan na wuce.
Haka Aishan ta tafi tabar sadiya tare da fadila a asibitin hankalin kowa a tashe lokacin likita yayi iya binciken shi baigano ciwon komai da yaja min konewan jini ba haka lokaci guda .
Dole wai sai an kara min jini akace a lokacin yace aje a dibi nasa mami tace kai har yaushe ka tashi a ciwo a dai duba na sayarwa a gani.
Kai sam mami ba za,, a kara mata jinin sayarwa ba gaskiya ya fada daga inda yake tsaye cikin tashin hankali kafafuwan shi a harde ya dora hannayen shi saman weast din shi duka biyu.
Jamal yace a je a dibi nawa ai zan iyabawa kowa jini na mami ta kalleshi ta rasa abinda zata fada dole ta kyalesu kawai suka tafi.
A can ma jafar din yaki yarda sai nasa aka diba aka kara min mami tayi fadan hakan sosai don ta nuna mashi bacin rai akan haka har tana fadin idan shi baisan ciwon kanshi bane yake neman kashe kanshi saboda mace su sun dani
Likitan da ya shigone yasa su fita ya fara kara min jinin a jikina sai lokacin na dan farfado har ina gane inda nake ina bin mutane da kallo.
Har dare sosai su mami basu je gida ba sai sha biyu saura na dare suka sauketa a gida don tunda Aisha ta tafi da motan driver bai dawo ba.
Ga mamakin mami ta zata Aisha ta dade da barci a lokacin sai ta iske su a falo zaune suna kallo da yan uwanta.
Tana ganin mami ta mike suka shiga daki tare a gurguje mami tana sauri tana cire kaya a jikin ta zata shiga bayi.
Aishs tace mami ya jikin zainab din da sauki ko tace tana shigewa ban dakin da sauki zainab zaki tambaya banda hjy.
Mami na fada maki da magana wlh kin ki ki saurareni tun dazun wallahi mami akwai matsala akan ciwon zainab din nan.
Ja mami tayi ta tsaya tana fadin wai ban gane ba me kike nufine da magana sai ta kalli kofan dake bude ta mike ta rufo kofan kamar wani zai ji abinda take fadi a lokacin.
Ta zauna ta kurawa mami dake tsaye kofan bayi ido fadi mana ina sauraren ki mami tace ga mamakin mami sai taji yar nata na fadin mami kizo kusa don Allah kiji kada wani yaji mu a waje.
Ikon Allah Aisha meke damuwan ki hakane yau bayan kin rufe kofa wa kike tunanen zaiji kine wai yanzu.
Me kike son fada min har jikin ki ke kyar ma hakane wai tace mami is something serious daya shafe ki wallahi.
Jin haka mami din ta karaso gaban ta yana faduwa don gani yadda yar nata ta tsoroce a lokacin.
Zama tayi a gefen yar nata tana fadin ki fada min gani nazo kusa dake Aisha sai Aishan ta dago kai ta kalli mami din gaban mami ya kara faduwa ganin idanun yar nata tab da hawaye lokaci guda gaba daya hankalin ta ya tashi
Mami ko kinsan ya j yana cikin kungiyan asiri kuwa what mami ta fada da karfi kafin ta fara girgiza kai tana fadin No No No Aisha kin san abinda bakin ki ke fada game da dan uwanki kuwa ?
Kai Aisha ta fara dagawa kafin tace a cikin kuka mami na sani ba zanwa ya J sheri ba ko da kuwa ba dan uwana bane shi.
Wallahi mami ciwon nan na zainab da sanin ya j wallahi ke Aisha mami ta fada da dan karfi ki san abinda kike fada kada in saba maki yanzu a wurun nan.
Wallahi mami naji abinda yake fada a waya da kunnuwana da banji wanan bakin abinba bazan taba fadin hakan ba mami.
Nan ta fara bata labarin yadda abin ya faru har zuwan shi yana waya da abinda taji ya fada a wurin lokacin game da zainab din.
Innalillahi mami kawai ke fadi kafin kuma tazo ta fashe da kuka tana fadin jafar sai kuma ta girgiza kai a cikin takaici.
Can ta juyo kamar tababa tana fadin bayan kanwar zainab din ke dawa ke wurin mu kadai ne ta bata amsa.
Ita kanwar zainab din fa taji abinda yake fada tace ban tsamani taji don kukan da takeyi a lokacin saboda shi najata zuwa bayan wurin filawowi.
Innalillahi Aisha jafar ya kasheni idan wanan maganan gaskiya don ko mu ba zai bari ba wata rana.
Wallahi mami najine ya fada exactly abinda naji na fada maki mami ban kara masa ba ni yanzu tsoron da nake ji shine kada su kashe ta a sanadiyar shi fa.
Ki bar wanan zancen Aisha zanga mamud mu tatauna a kai zuwa safe don yanzu nasan ya shiga gida ko tunda ya saukeni.
Mami a nan zan kwana tsoro nakeji wallahi ba zan iya kwana dakina ba yau ta fada a cikin dan shagwaba.
Mami bata tsaya ba ta wuce zuwa ban dakin da tayi niya kai tsaye zuciyar ta cike da tunanen dan nata.
Har ta fito bata bar jin abinda take ji ba a lokacin don haka ta samu wuri takai kwance Aisha na gefe kwance taji mami din ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Haka yasa ta mike zaune tana fadin mami ki bar kuka please kada ki jawa kanki matsala don Allah addua ya kama ayi masa yanzu please.
Aisha jafar yana son ya kasheni me yar mutane tayi masa yake son bada jinin ta a sh haka ?
Mami ni godiyana ga Allah daba zarah bace yake aure haka ya faru da kinsan iyayyen ta ba zasu taba yarda da hakan ba sam.
Tunanen da nakeyi ke nan yanzu Aisha da ace itace a gidan nasa yau ina zan sa kaina a kasan nan inji dadi.
Yanzu ne na kara tabbatar da kalami da ya keyi idan nayi mai maganan aure sai yace zainab ce daidai dashi ya aura.
Ashe abinda yaron nan yake nufi ke nan ban fahinta ba har hjy tsohuwa ta rigani fahintar manufar sa din .
Haka suka kwana sai kusan asuba mami din ta tashi ta fara nafila ana fitowa sallah ta kira wayan mamud tana neman shi idan ya tashi.
Hankalin ya mamud ya tashi yana zaton ko hjy ko nice wani abu ya faru damu.
Ya amsa da fadin mami gani zuwa yanzu Nuriya dake gefen shi ta dago da sauri tana fadin lafiya dai ko yace ban sani ba sai na tafi.
Kodai zainab din ce ta cika ta tambaye shi tana kure shi da ido don jin amsan da zai bata a lokacin yace itace damuwan ki a duniya dama ?
Kai ba a maganan arziki dakai dama ta fada tana kawar da kai gefe cikin jan tsuki da jin haushi shi a lokacin.
Rigan shi dake gefe ya dauka ya zura ya fice dakin da sauri zuwa part din mami din hankalin shi a tashe.
Yana shiga part din mami din ya nufa babu kowa a wajen sai yan aiki dake ta aikin su a gidan suna gaudashi yana amsawa a gurguje ya kai kofan ya kwankwasa.
Aisha ta amsa mai da fadin shigo yaya ya sakai da sallama ya shiga yana shiga ya hango mami zaune a kasa ta jingina jikin ta ga bangon dakin kamar tana tunane.
Mami lafiya ya tambaya yana kallonta jin ba amsa a wurin ta ya juya wurin Aisha yana fadin Aisha meke farune haka ?
Ka zauna yaya ta fada itama a sanyaye tana kallon mami din ya samu wuri ya kai zaune a hankali gefen gadon yana maimaita tambayan shi har lokacin ba amsa.
Shiru ne ya dan biyo a dakin kafin mami din tace mamud kasan wana ciwon da yarinyar nan zainab keyi a yanzu Jafar ne silar shi kuwa.
Jafar kuma mami ya tambaya a cikin mamaki yana kallon mahaifiyar tasu don son karin bayani a wurin taba
Eh jafar ki fada mai abinda kikaji yana fada tacewa Aisha dakw gefen shi zaune a takure cikin damuwa karara a fuskan ta.
Jine da kanwarta ke kuka bayan ta some din nan sai na jata zuwa baya ko zatayi shiru nan ta kora mai komaai wanda kafin ta gama ya kira sunan Allah yafi a kirga.
Saida Aishan tagama magana har lokacin kai yake gitgiza yana jin ta aje ya amsa da fadin mami na fada maki ina zargin haka gare shi kice in bar zancen nan kada in kara fadab haka a bakina.
Subbahanallahi wlh biri yayi kama da mutum mami duba da wasu halayen jafar na rashin son raban mutane da baiyi kuma a haka harkokin shi suke ci gaba kullun.
Ya kara fadin hasbunallahi wani imal, wakeel wallahi in har wanan maganan gaskiyane jafar ya cuci yarinyar nan don a tsaye take wallahi mami kan al,amarin shi .
Don shi da bakin shi wallahi yake fada min irin kokarin da yarinyar nan tayi a kanshi har ya daina shan giya da neman maza yan uwanshi a yanzu.
Ita zainab din mami ta tambaya cikin dago kai tana kallon shi yace wallahi mami ya fada min komai amma bai fada min yana cikin wani kungiya ba haka.
Ai ba zai fadama ba tunda yasan bai shuka gaskiya ba mana yarinyar da tayima wanan har zaka iya bada jinin ta ga tsafi.
A dai bincika mami don bamu san inda zancen nan yanufa ba kai tsaye kar muzo mu yanke kasa hukuncin da bashi ba a nan.
Idan ba gaskiya bane me zaisa ya fadi haka yana warning din su kada su kashe ta dashi suke da matsala ba ita ba.
Mami jamal yasan da wanan zacen ya mamud ya fada yana kallon fuskan mami din tace kai kadai na fadawa yanzu.
Don tun jiya ta fada min da dare na kasa barci a gidan nan sam ban runtsa ba tun jiya di data fada min zancen.
Bari mu tambayi jamal ko yana da wani masaniya ga hakan da sauri mami tace kada ka fada mai komai yanzu sai in hakan ya kama a fada mai din.
Kasan jamal da bakin zuciya wallahi zai iya kawo hatsaniy tsakanin ka dashi yanzu menene kada a fada min jamal din ya fada yana shigowa dakin.
Don tun shigowan ya mamud ya ganshi ya koma daki ya saka riga tare dayin brush yabiyo bayan dan uwan nashi hankali tashe.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.