Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 55 of 139

🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

4️⃣6️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

FATAN ALHERI GAREKU YAN UWA TARE DA KARA BAKU HAKKURI DA YANAYIN DA LABARIN YAZO MUNA SABODA KARATUANA A YANZU DON ALLAH A KARA GAKKURI DANI YAN UWA NAGODE, , , , ,

Zan iya cewa tunda gari ya waye ban leko waje ba daga dakin da muke ciki zaune mu uku din kamar muna gidan kaso don tun shigan mu gidan muka shiga sakin ba wanda ya fito daga cikin mu har halima dake daukin zuwa abuja din a lokacin.
Sai gata baki ya fara mutuwa tun ba,aje ko ina ba a lokacin tunda taji matar malam na fadin Allah ya cecemu da wanan gidan har za a yanka mutum a bizzime ba,a san an yanka kaba.
Hankali halima din ya fara tashi tun jin furcin Maizube matar malam din muna zaune ga gari ya waye zugun zugun a dakin da muka kwana din wanda shima munsan da zamu kwana ne ta hannyan kai muna kaya dakin danaga anyi yasa na jasu zuwa dakin muka shiga.
Kofan aka kwankwasa wanda yasa kusan lokaci daya muka dago kai zuwa kofan kafin a sake nocking na biyu wanda yasa nayi karfin halin mikewa zuwa kofan lokavin guda .
Na bude tare da kallon wanda ke bakin kofan a lokacin shine yana tsaye yabawa kofan baya ta hanyar saka hanayen shi a ciki aljihun wandon jikin shi.
Wanda jin karan budan kofan shima a lokacin yasa shi dan juyowa zuwa gun kofan mukai arba dashi da sauri na zube kasa don girmamawa ina gaida shi da kwana.
Bai amsa ba sai cewa da yayi zaki kashe mutane karfe sha daya ake nema baku fito kun karyaba har wanan lokacin haka ?
Dan daburcewa nayi na rasa me zanyi a lokacin don rudewa da nayi yau shine a gaba muke magana haka kai tsaye dashi sabanin da can da hjy kan muna shamaki a tsakanin mu.
Zasu fito yanzu na samu bakina na fada lokaci guda na fada ya juya ya bar kofan kamar maiyin sauri kada wani ya ganshi wuri lokacin.
Dakin na koma tare da fada masu abinda yace sai maizube ke fadin aiko nan ma aka kawo saimu karya ko.
Ciki da daurewa nake fadin kinsan su a table ake karyawa nan saboda haka mu fita zuwa falon inda zamu karya din yanzu, don yana fada wai naki fitowa daku can ku karya.
Maganan da maizube keyi yanayine dake nuna alaman tsoro da karfin hali a lokacin don gaba daya ta gama tsunkewa da al,amarin gidan ga baki daya.
A takure dai kowa yake haka muka iso falon dana lalubu muna inda dinning din yake da abunci a jere sama shi a aje muna.
Dole na nemo karfin hali da jarunta lokaci guda na sakawa kaina don kawai halimatu da matar malam da kiris suke a lokacin su fasa ihu a gidan don tsoro.
Basu ba ni kaina duk da zama a gidan mami ya taimaka min matuka saidai duk da hakan wani abu ban san shiba a gida wanan ne farkon ganina a gida nasa.
Abinci ne mai rai da lafiya aka shirya muna don karyawa wanda nasan halin yadda ake abin karyawa nawai don mu din bane yasa aka shirya hakan .
Kawai dai haka abin yake a garesu ko yaushe dan magana halima tayi min na zuba mata harara daga inda nake take fadin yayan mu duk wanan mu zamuci duka ?
Na watsa mata harara tare da cigaba da kurban tuwan shayin da nake kurba a lokacin a hankali duk zuciyana ina ji wani irin yanayi a lokacin.
Text ya shigo min a wayana na dan saci duba a hankali ko daga waye duk da wayana layin mutum.dayane a cikin sa lokacin.
Ki bisu a hankali kada ki takurawa bakina a gidan nan yin hakan yana cikin bin umurni na a yanzu kiyi duk abinda zakiyi su kwantar da hankali su gidan nan da kowa, ya rubutu min saida hakan ya ban mamaki don ban san a inda yake tsaye yana kallon mu ba alokacin.
Ki dibi duk abinda ranki ke so a gurin nan halimatu duk namu ne do mu aka ajeshi a nan na bata amsa a cikin dan wayen cewa da fuskana kamar babu komai a raina.
Ba laifin sun sake jikin kamar yadda ya kamata sunci abinci daga nan bamu koma daki ba a kokarina na bin umurnin shi a lokacin kamar yadda yace din.
Sai zuwa karfe daya saura ya shigo suka gaisa da maizube matar malam kamar yadda muke jin a gida kowa na kiranta da wanan sunan na maizube matar malam.
Ba wani sakin fuska ko sabo a gaisuwan ya mike tare da fadin halimatu zo naji mana ya fada ba tare da ya tsaya ba na kalleta itama ni din take kallo da mamaki tare da jiran umurnina .
Dan dukar da kaina kasa nayi kafin na dago na kalleta ta mike don ta gane me nake nufi da hakan daga kallon ta danayi din.
Tun ina zuba idon ganinta har na dan far tsoron haka sai gata tare da security din gidan niki, niki da kaya ana shigo mata dasu cikin gidan.
A hankali na sauke ajiyan zuciya tare da bin kayan da ake shigo dasu da kallo inda na dan fahinci wani abu a lokacin.
Maizube tana gefe a zaune itama dai ba sai an tambayi damuwa a yanayin nata ba lokacin har zuwa lokacin da suka gama shigo muna da komai acikin gidan.
Wata mace tayi sallama ta shigo da fara,a a fuskanta ta zauna suna gaisawa da maizube tare da muna bayanin itama a gidan zata zauna tare damu .
Itace wai mai aiki kula da komai yadda ya dace da fatan zamu ji dadin zama da juna yadda ya dace ta kare da fadin .
Itama dai musulmace yar uwan mu don haka mu sake jiki da ita don Allah don komai ya tafi daidai a gidan.
Abubuwan dake faruwa a lokacin koda nake yarinya mai san karancin shekaru da ban wuce sha shidda ba na dan fahinci wasu abubuwan a lokacin saboda natsuwa da fahintar dake gareni .
A waya yai min bayanin komai yadda zan fahinta daga kayan har yadda zamu zauna da matar data gabatar muna da kanta a matsayin mai kula da gida ya min bayani tare da ja min kunne akan komai.
Yana fadawa halimatu a ranan zaiyi tafiya bata fada min ba sai bayan mun sallame sallah a azahar tana muna hira fitan su da inda sukaje ashema ba tare dashi suka fita ba da wanan bakuwar matarce ta sayo muna kayan nan da akazo dashi gidan.
Kallom halimatu nayi tare da fadin yau zai koma ina ya fada maki halima tace yace wuri aikin shi kuma wai muyu karatu sosai kafin ya dawo.
Na dauka shirmen halimatu ne sai gashi da yamma kawai ya shigo yana sallaman maizube da niyar zaiyi tafiya a ranan zai dan jima bayana nan .
Ta shiga jero mai addu,an neman tsari da kariya a gareshi da alaman yaji dadin hakan don irin alherin da ya aje mata yana karbawa da amin ya mike.
Ta kalleni tana fadin wai nikan ba zaki bishi baje harda kinji zaiyi tafiya kina zaune a daki kinki ki motsawa tun dazun.
Ba don naso ba dole na mike nabi bayanshi kamar yadda tace dani din inyi sai gashi har muna kokarin cin karo dashi a kofan da sauri naja dan baya kadan kada mu gwaure .
Ya lura sarai da yanayin kaduwa dana shiga na kaduwa dana ganshi a gabana lokacin.
Tsadadiyar muryan shi ya ratso dodo kunne na yana fadin lafiya ina zaki tafi ko wani abu kike nema ne ?
Dan dukar da kaina nayi kasa tare da fadi a cikin dan damuwa dama dama dai na fito ne don in sallameka kawai ina wasa da yan yatsun hannuna duka biyu nake magana.
Yana tsaye yana kura min ido yana kallona tare da dan sake murmushi a fuskan nnasa tare da dan gyara tsayin sa dakyau har lokacin idon sa a fuskana.
Kamar aafalki naji muryan shi again yana fadin to ai gani saiki sallameni din inji tunda ke baki san abinda ya dace ace kinyi ba.
Kada ki manta komai da zamuyi a tsare yake a kan mu ba tare da kowa ya fahinta a gidan nan ba ina nufin kuwa har wanan yar aikin da zata zauna daku ba zata fahinci zaman mu dake ba kawai dai a matsayin mata da miji masu kula da junan su kowa zai dauke mu.
Na dago kai da sauri na kalleshi do jin abinda ya fada din sai yayi daidai da idon shi a kaina ya daga min gira da kafada tare da fadin idan kinyi hakan kin taimaki kanki.
Yana fadin hakan ya juya ya wuce ya barni tsaye da mamaki a wurin don na kasa fahintar inda zancen shi ya dosa a lokacin.
Gashi ba wai wata kawa ko abokiyar hira ke gareni ba a lokacin da zan kaiwa shawara na har mu gane me hakan ke nufi da zancen shi a kaina.
Ance idan bawa yana son walwale al,amari shiafi yawa haka yafi zuwa mai a daidai tsakiyan sallah don sai shedan yaso ya shagal dakai daga barin sallah ya hasko ma abinda ya shige ma duhu a lokacin.
Nima kusan hakan ne ya faru dani a daidai sallah la,asar danazo yi don yanayin damuwan dana shiga yasa na tayar da sallah a vikk kuncin zuciya.
Tiryan tiryan abinda yake nufi kr zuwa min a rai na har da wanda ban san zankai ga tunane ba saida na fahinci komai a lokacin.
Sheda kenen yaso ya ribanceni ta hanyat bata min sallah a lokacin na farga da hakan da sauri na mayar da hankalina a gurin ibadana.
Bayan na idar ina zaune wani shu,umin murmushi mai hade da sautin dariya yazo mi lokaci guda .
Hannu na daga tare da yiwa Allah godiya akan haska mi hanyar dayi a lokaci daya.
Sai muryan maizube ke fadin lafiya dai yar nan daga idar da sallah kin soma dariya haka kamar an maki bushara da aljanna.
Karfe shidda saura kiran shi yazo min na sameshi na falon shi duk sa bansan wurin ba haka nayi kokarin mikewa zuwa amsa kiran nasa.
Yana zaune a cikin shiri shi sai kamshi ke tashi ko ina a falon na shigo da sallama a bakina ba dauka ya karba hakan ba don ba lale bane ya amaa din.
Banyi gigin hawa kujera dake falon ba a lokacin don haka naja nakai kasa zaune dan nesa daga inda yake hankalin shi yana gun abinda yake a system din shi yayin da falon yai shiru na dan lokaci kamar babu kowa a wurin.
Kafin yadago kai yana fadi a uzurce OK kinzo ko tare da dan lumshe ido ya sauke su akaina a hankali kamar yana nazarina a lokacin.
Yau zan tafi kamar yadda kikaji na fada dazun wa mama don haka komai na kula sa gidan a yanzu zai dawo karkashi ikon ki a garin nan.
Duk wani kokari idan kinga dama ta yadda ba wanda zai fahinci meke tsakanina dake a wanan zama namu yanzu.
Yanzu wasan mu zai fara don a bayana abubuwa zasu faru da dama na sani saidai idan kin iya tsirar da kanki abin zaizo mako da sauki ko yaushe.
Da sauri na sake dago kai na dan kalleshi inda yake zaune din yace yes daga ni sai ke muka san irin zaman da zamuyi a tsakanin mu a yanzu.
Barazan mami ko wani dan uwana kada ki yarda ya kaiki ga furta masu komai dake tsakani mu ki tsaya kaida fata a matsayin matana kike a gidan nan barazan wani ko wata ba zai fitar daken ko ya tsoratar dake ba garesu.
Kaina gyada a hankali don ganin yana maganan ya tsureni da idanuwa shi idona suka dab ciciko da hawayen nadama .
Don tabbas na jefa kaina a tsaka mai wuya duka bangare biyun da nasa dana mahaifiyar su din dama wanda ka taso daga baya.
A hankali ya lumshe idsnuwan shi tabbas tausayin yarinyar ya kamashi don yasa ya jefa yar mutane a wani hali .
Wanda rashin wayau da ilimi ya kaita ga yarda da bukatan shi a kanta ba tare da nazari komai a game dashi ba kuma.
Yace kada kiji komai ba zasu iya illanta min ke ba dan kina a cikj matakan tsarona ta ko ina muddi dai kin iya kanki da bakin ki ko yaushe.
Ba tare dana iya furta mai komai ba na sunkuyar da kaina kasa hawaye na ci gaba da zuba min a hankali.
Shigowan yaron shi da shima na gansa a cikin shirin shi da alaman tare zasu tafi ke na tafiyan.
Ganin yadda nake zaune ina hawaye ya da kalle ni ba tsamani ko zato naji yana fadin lafiya take wanan kukan haka ko an mata wani abin ne kuma ?
Bai bashi amsa ba sai mikewa da yayi tsaye yana gyara kayan jki shi tare da fadin zamuyi sallama da ita ka bamu wuri ya fada mai ba tare da kallon inda yake ba yana daukan kaya.
Haka ya fita daga daki ranshi bace yana dan satan kallona a inda nake kamar mai tuhumana a lokacin.
Murya shi naji a daidai inda nake tsugune ina hawaye yana fadin zainab al,amarin mai girmane ba zaki gane ba a yanzu sai nan gaba zaku gane manufana.
Sai dai ya yanzu ke din kanwa ce a gareni zanso ki rikeni tankar kece Aisha na da muka fito ciki daya da ita wurin kulla da amanata da komai nawa.
Idan ki mun hakan na maki alkawari har abinda baki zata ba a rayuwan ki bikatana kawai ki nuna ma duniyake din matatave ta suna kuma yar uwata a badali.
Kin min alkari hakan ya fada tare da dan tsugunowa saiti inda nake makure ina kuka kafin in magana aka turo kofan tare da fadin kasan fa jirgin mu takwas zai daga kana nan tun dazun.
Kabar falo nan na fadama ya dan fada a hasale tare da nuna mai kofan a ciki zafin rai da sauri ya juya ya fice shima bai tsaya din ba ya mike tare da fadin ga key din daki nan zamu dinga waya duk abinda kike so zaki iya fada min idan na kiraki mu zamu tafi.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.