Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 24 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1ï¸Â⃣8ï¸Â⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU MASOYANA UBANGIJI YABA WUNI LAFIYA YA SADAMU DA RAHAMIMIN SA AMIN YA ALLAHU.
KI BIYA HAKKIN MU KI KARANTA A CIKIN SALAM DA SAKEWA DARI UKUNE KACAL 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA NA DARI UKU.
Ranan naga yadda ake nunawa jika so da kauna na gaskiya don tsohuwar kamar ta hade yaran su koma cikinta take ji basu kadai ba harni da nake bakuwa a cikin su bata nuna min bambancin hakan ba.
Ga tawa kakar saboda wani dalilu nata na daban ta turoni bitnin yin aikatau badon Allah ya hadani da uwar daki ta Allah ba.
Allah kadai yasan yadda rayuwata zata kasance a birni ba tare data damu da hakan ba ita nata butin dai shine ta samu kudi ta gareni kawai.
Basu bar dakin ba nan kowa ke zuwa taron su suna gaisawa su yaya jamal ne suka mike don zaga gari zama wuri daya ya ishesu.
Yaya mamud ya dade da fita daga dakin ya barsu yana fadin zai leka wani abokin shi ko yana nan suka bar yaya jafar dake faman aiki a cikin sytem din shi yamai da hankalin gaba daya ga abinda yakeyi din.
Ina zaune takure wuri daya na kurawa tv dake aiki ido ana wani shiri a kscm kaduna hakab yasa hankalina ya dauku ga kallon.
Ai bata jikaba tshohuwar ke fadi me take da suna tana murmushi take kallona nayi firgigit in dago kai sai naga ido shi a kaina.
Bakiji me na fadaba yake tambayaba kai na girgiza mai ina tasowa daga inda nake ki dauke kayan nan da suka bari a nan ya kara fada.
Sai lokacin nasan meya fada da farko na tashi da sauri na fara tattara kayan dake saman karamin table din.
Waini kan dan gidan iyami yaushene zaka kawo muna sarakuwa tshohuwar ta fada tana kallon shi.
Cikin basarwa da kalan maganan shi ba tare da ya dago kaiba yake fadin banga matar aure ba har yanzu.
Allah na tuba duk matan daka baro kaduna har Abuja bakaga mata a cikin su ba don tsaban ruwan ido idan an fada uwarka ta tare maka.
Ni yanzu nafi dason yaro yayi auren shi a cikin lokacin don wanan rayuwan baida tabbas dan rayuwan yanzu kadan ne.
Ba sai ki nema min ba tunda ke kinga matan a ko ina birjit yo ko cikin yan uwanka ka nema mana ko wanan yar ta uwarku ai irice ta kwarai gata da hankali har naji dama ace ta shigo cikin zuria na.
Ke kiji da kanki don Allah da wanan shirme da kikeyi an fada maki kowa irin kune halan ya fada yana zareww tshohuwar ido.
Ta sake dariya tana fadin kaji min dan kawai ido ma zaka zare min don kawai na fadi gaskiya ko sai mun kaika mararaba mun ma wankane kafin a soka.
Kinga idan kina matsa min da wanan magana idan na tashi na tafi ke nan ba zan dawowa ba ya fada kanshi duke.
Nasan zaka iya dan nema mai zubin jan fata kai dama Allah yaga abinda ya gani ya kaika can cikin su da zama.
Wanan karo kan tare dake zamu koma ai don naga kema dasu kikafi kama ai barni na mutu musulma tsohuwar ta fada.
Saiga mami ta shigo falin tana fadin hjy dake dawa kike magana sai ta ganshi a zaune take fadin a a aboki kai kana ciki ashe na dauka tare kuka fita ai.
Ina nan mami idan wanan tsohuwar bata daina damuwana ba zan bar garin nan yanzu ba sai anjima ba.
Zaka iya na sani damuwar dai nasan fadan so kankane takema da baka son ai maka ko ?
Kamar kin sani yar albarka daga zancen aure yake wanan halakon haka kamar an mashi maganar mutuwa shi.
Wai shi baiga mata ba duk garin nan nakece mai ga wannan yar taki tun ba a kai ko ina ba don ni na yaba da halaiyar wanan yar taki.
Da sauri mami ta juya inda nake ina daukan gorunan drinks a kasa take fadin haba dai hjy har abin nasa yakai haka kuma ?
Ai ba zan barshi ya tafi ba sai ya tsayar da matar da zai aura in yaso sai ya koma idan bukin ya karaso ya dawo ayi buki nima zaman shi haka a can shi kadai ya dameni yanzu.
Kaji maganar gaskiya don wanan da kike gani idan bakiyi da gaske ba baida niyar aure yanzu gashi ya fara zama magidanci.
Wani kallo yaiwa tshohuwar tare da mikewa lokaci daya sai kuma naji ta koma rarashin shi tana fadin ai kasan bama haka dakai.
Kada kasa mamuda yai muna dariya tun ba,aje ko ina ba yanzun fa na gama mashi tsiya a kanka yai fushi ya fita don nace kai nake so.
Yanzu ma zan fada mai ya dawo nabar masa ke ya dauka bana so ni don kin faye jininini da yawa yanzu.
Dawo dawo ka zauna na bar wanan jininin indai a kankane na isheka ni kadai ai dama ai baikai ciki ba zancen nawa ina ka taba ganin mutum ya dabawa cikin sa wuka ?
Komawa yayi ya zauna sai abin ya bani dariya har bansan lokacin da sautin dariyan ya fito min fili ba.
A, a a takwarana dariya kike min kuma don ina neman shiri da maigida a gaban ki ?
Hararana yayi yasa na bar falon na koma daga wajen dakin na zauna saman dan dakalin dake wajen ina kallon mutanen gidan dake gittaya tako ina.
Sai da ta fito da niyar zuwa sallah mami ta biyo shi suna magana dashi mami ke fadin zeey a nan kuma kika zauna ne ?
Na juyo ina dan gaida ita take fadin shiga mana ciki koda yake ma anyi sallah azahar yanzu sai ki shiga wancan dakin dake gefe akwai bandaki a cikin sa a gyare dakin yake ku zauna keda Aisha.
Jin haka yasa na mike ina kokarin shiga dakin don kallon da yai min mai kama dana warning a lokacin.
Dakin da mami tayi min kwatance na shiga dakine gyarare da katon gado hade da mirrow din shi sai kujera three seater dake dakin gadon yasha gyara dakin yana ta kakahin turaren wuta.
Ban dakin na nufa na samu ruwa a manyan robobi aje dashi nayi amfani na dauro alwala nafito na tayar da sallah saman salyan dake dakin.
Ko dana idar ban zauna ba falon na fito na gyarashi tsab har waje duk suna cikin daki basu sani ba sai da mama habiba tazo fitane ta ganni take fadin yar nan kina nan kina aiki baki huta ba.
Hjyn su mami ke tambaya wace yace kuma sai kuma ta tuna dani take fadin au yar iyami ko ?
Wani aiki take kuma yarnan ki huta hakana mana ina hankalce da ke baki da son kazanta ta juya inda mami take kwance tana fadin.
Kin samu ya sai ki rike tada amana don Allah yarinyar tana da shiga rai lokaci guda gata da ladabi.
Sai naji ina kwadayin hada iri da ita don irice mai amfani ita din ba abin yarwa bane haka.
Hjy nima yarinyar ta kwanta min a rai sosai ina kulla da ita tankar yar cikina don bata da kyashi ga sanin ya kamata kamar wata babba can.
Tarbiyane idan kinga haka ta samu tun daga gida uwarta ta tarbiyartar da abinda yadda akeson ko wani da ya kasance sai ki kara himma wurin riko Allah ya taya ki rikasu.
Don tafi min wa yan nan marasa moriyan sau dubu a wurina sai hjyn tasu tace tafisu kan gaskiya yaron da ba sai kace ya tashi yayi ba yake abu ai yana da dadin zama.
Hjy kin san wancan zuwan da nayi da yaran nan iskancin da sukai min saida muka koma gida nake ji nayi masu tas wallahi.
Kiyi hakkuri dasu tunda su suka kawo kansu gare ki inma sunyi maki don kansu kowa ma zai girbi tsiyar shi ai.
Ke dai ki rike wanan bisa ga amana da yarda idan dai bata kauce bane don mutum mugun icce ne sai yaga ya ginu yace kaine makiyin sa daga baya Allah ya kare mami ta amsa da amin.
Sai dare mazan suka sake shigowa ina daki naji hayaniyan su ban daga daga inda nake zaune ba naji muryan mami ta fito daga uwar daka tana fadin.
Garin yai maku dadi ke nan ko kun shige cikin gari tun dazun ina shi aboki yake ne banganshi tare daku ba.
Wanan friend naki saike mami yana masallaci mun barshi wai yanzu yake son sallam guards din shi su koma kaduna su kwana.
Da daren nan tau haka dai yace don wai baiga inda zakaisu ba nan suwa ke nan tsohuwar ta tambaya.
Security din da mijin ki ke tafiya dashi don tsaro yaya jamal ya bata amsa a takaice take fadin.
Ikon Allah tafiyan ma sai anyi shi da masu tsaro ko may sai yaya mamud yace kin san su can hakan ai wani abu ne tundaga can aka hadu shi dasu aikin su sukeyi su.
Duniya inda ranka kasha kallo yanzu shi wanan dan figegen aron ne harda wasu masu tsaron shi.
Hjy mu a nanne ba a dauki tsaro da mahinmanci ba amma su can idan har kai wani abune dole kana da masu binka a baya ai massanman shi da sukeji da shi a can.
Waini na kasa gane aikin yaton nan sai jalal yace bako zaki gane ba don shi bros telent ne sosai ilimin shi yaja masa hakan.
Yanzu zai iya kera maki wani abu a wurin nan wanda sai kinyi mamaki don har abin yai tafiya da kafansa su ake kira da sciencetics mana masu fasahan kwakwalwa ikon Allah tace.
Tare da fadin gaskiya yaki aure haka har yana batun rufe arbain fa don in ba zan manta ba tun mulkin shagari na farko aka haifeshi ai.
Kai hjy wanan tashin tasgin haka kan friend dina yanzun dai ni abinda nake so kafin ya tura mutanen nan a cikin daren nan ai masu kokarin wurin kwana hjy.
Tshohuwar ta tambaya su nawane akace hudu hudu ta fada da mamaki tana fadin har karte hudu ke yawo dashi wanan abindai da nake gani.
Ikon Allah yafi gaban mamaki yau ace wai dannan ne Allah yaiwa bawa haka Allah ya ciyar daku baki daya suka amsa da amin.
A daidai lokacin da dan bawan ke shigowa yana waya tsohuwar ke fadin gama yanan ya shigo dayani.
Kai yanzu don baka da tausayi zaka tura yaran mutane da daren nan su koma kaduna don rashin imani.
O lord wanan kuma wani zance take hakane da shigowan mutum ya fada yana kaiwa zaune yana aje wayan da yakeyi.
Aboki wai yanzu da daren nan zaka tura security din nan su koma kaduna sai naga dare yayi ai.
No sun fasa ai mami uncle bello ya sama masu wuri zama da zasu zauna suna can sun tafi suga wurin kafin su dawo su dauki abinci.
Ko kaifa nace ko kai fa dan nan amma ka tura bayin Allah a cikin daren nan haka ai abin baiyi ba kamar dai ba mutane a nan.
Enough dan Allah waiwa ya fadawa wanan mai wa,azin ta damu mutane da wa,azin nan nata a gurin nan.
Kai rufamin baki aini yanzu nasan ba cikkaken namiji kake ba don a matsoraci nake kallon ka yanzu tunda sai an rakoka har karkaran mu matsoraci.
Daidai lokacin nake fitowa daga dakin don kira da mami tayi na amsa daga ciki.
Dariya ya bushe dashi bashi kadai ba duk wanda ke falon saida maganan ya bashi dariya yadda suke kwasa dashi din.
Barin gani idan baki tsorona din da gaske ya fada yana mikewa ya harota ta juya tana neman abinda zata kare kanta kafin ya iso gareta .
Tayi sa,a filo na kusa da ita ta dauka wai dashi zata kare kanta din tana kaimai duka yana dariya ya juyo a daidai lokacin na kawo wurin zan wuce sai ji nayi kumus nayi baya tangal tangal zan fadi.
Mami tace zaka karya min da da wanan karfin naka haka kamar na doki shi kuma ya juyo yana fadin oh sorry .
Tsohuwar nan kinga zaki saka in karyawa mami yarta don fitinan ki to yaushe rabo damuyi fitinan haka.
Ai rabu a gana arzikine dan nan wata ran idan kunzo sai kun tunani da wanan wasan da mukeyi yau ina Alh ina mahaifin ku sun kare.
Kowa yai wani iri a dakin don abinda tsohuwar ta fada wallahi hjy gashi yau muna kewan tsohon nan don da zaran zan shigo naga part din shi sai in tuna da lokacin da muke zuwa yana bamu mazzakwala muna sha yaya mamud ke fadi.
Kai mukan bamu sanshi ba gaskiya sai dai a photo jalal ya fada ai old man din nan ya kware mu daya tafi bamu sanshi ba.
Waike zeey kin debi abincin nan kuwa na juyo ina fadin ban diba ba mami yanzu na idar da sallah dama.
Jeki ki dibi abinci da wanan halin naki ga abincin mu can ankai mana daki tun dazu wanan nasu sai na mutane yayan ku yacan sai a samu yaro yakai masu idan sun dawo.
Juyawa nayi zan koma dakin don ban iya sake jiki suna wurin don haka na juya don na koma dakin hjyn su mami.
Banji me yake fada ba yaya jamal yace ke wai kizo ki zuba mai abinci yar mami.
Jin an ambaci sunana yasa na tsaya tare da juyowa na dawo zuwa inda abincin yake aje dan kallon yaya jamal nayi ina fadin wa zan zubawa.
Yaya jackson ya fada hankalin shi naga wayan shi rasa abinda zan zuba mai nayi don kuloli ne gurin zasu kai biyar duk an cikasu da abincin alfarma har da fate da mami tace tana so yaji gyada a cikin sa.
Fara bude masu kulan abincin nayi don ya zabi abinda ranshi ke so sai dai baya kallona hankalin shi naga waya yana rubutu.
Yaya me zan zubama na tambaye shi ina dan gurfane a gaban shi don ba dining table falon tsohuwar kamar can gida kaduna.
Ya dan dago kai yana fadin anything zaki iya zuba min Aisha ta fito daga dakin yaya mamud daya karbi plate din da mami ke shan fate yana dan sha yake fadin Essha kina gidan nan ashe tun zuwan mu ban ganki ba.
Ina kwance ne yaya ta fada tare da ratsowa ta zauna a hannun kujera tsakiyan su shi da yaya Jafar din.
Ke may kike a wurin nan ne haka ta tambayeni ya Jalal yace wai abinci akace ta zuba take tunane na dan kalleta ina fadi a hankali ban san may zan zubabane ai.
Oh shine kike tsaye a gurin ya mamud yace ka duba ai tana da gaskiyar ta kada ta zubama abinda baka so ne.
Wanan dai ina so inga matar shi kafin in mutu yaro da izza da isa kamar wani basarake dashi matar ka tana da hakkurin zama dakai haka.
Hjy naga fa yau sai yar tsama kuke da yaya Jackson tunda muka zo Jalal ya fada don shi yafi yawan dan magana bisaga Jamal dake da zubin yanayi ya jafar din wasu halaiyan su suna da kama sosai.
Aure nake son yayi hakana ya baku wuri kuma ku samu ku zaburo wanan gwauron ya tare maku wuri.
Muka fada maki samarin suka fada tace to ai shike nan tunda baku son a matsa mai yayi aure.
Wanan fa zata iya hada ma abincin nan duka tunda kace anything zata dauka kace tayima mix ne gaba daya Aisha ta fada tana kallona.
Ke zuba min ki daga min nan don Allah ya fada tare dan dagowa yana kallona.
Hasken kwan fitilan falon ya haskani gaba daya launina bada wani kala na daban ga mai kallona a lokacin.
Na duka ina zuba mai kullan gabana wanda sakwara ne a ciki ashe sai na bude kulan miyan shi dake dauke da miyan ganye yaji egushi da manyan nama na zuba daida don nasan shi baya cin abinci da yawa.
Mikewa nayi zan bar wurin ya kara fafin ruwan wanke hannu fa ba tare daya ko kallo inda nake bai yi ba yai magana.
Har suka bar falon ban kara fitowa ba sai bayan danaji fitan su sunawa mami saida safe na dan kara mintina na fito.
Kayan da sukaci abinci nake kwashewa yayin da nazo kan nasa naga spoon a ciki da alama dashi yaci.
A raina nace bakin bature ke nan abincin ma da cibi zaici don sallo ai kakar nan tasuce maganin shi.
Tas nayiwa falon kafin in shiga wurin mami ina tambayanta koda abinda zanyi mata kafin na kwanta.
Zeey a kwashe kayan abincin nan da sukaci nace na kwashe mami ki duba min kayan barci na a cikin kayana ki ban shike nan sai kije ki kwanta.
Har na kwanta a saman dogon kujera anty Aisha ta shigo tana fadin af namanta da charger na dakin tsohuwar nan dan Allah zeey dauko min.
A kofa na tsaya nayi sallama kafin in shiga dakin yanayin dana samesu a ciki nagane wani magana sukeyi mai muhinmanci a tsakanin su su hudu.
Tsohuwar da kuma kannen mami din duk suna zaune sunyi shiru da suka ganeni.
Sai mami ke fadin bakiyi barci ba ashe zesy a, a nace nake fadi charger anty zan dauka ganin suna kallona duk sai na tsargu .
Na dauka na fita da dan saurina daga dakin don ban son in dakatar masu da maganan da sukeyi din .
Washe gari tunda safe dana tashi nayi sallah na fara gyaran falon har zuwa waje ina jin hayaniyar su dakin har na gama wanka na shiga don mami tana cikin dakin da yan uwanta.
Sai kusan karfe goma suka fara shigowa falon ana gaisawa a tsakanin su babu muryan wanda nake jin tsoro don haka na fito na gaidasu da kwana ina jin mama Ramatu na fadin.
Ga abinci nan tun safe aka aje masu shi basu shigo ba ina shi jafar din gana yan aikin shi nan suma .
Bai fito ba jamal ya bata amsa tare da fadin mama kinsan shi baya fitowa da wuri haka ai sai idan ya gama abinda yake yi.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.