Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 14 of 139
KAUYEN ANCAU
Iska na wahal da mai kayan kara a gidan nan yarinyace dai ta tafi ba dawowa zatayi ba balle mutum ya shige daki yaki fitowa.
Lantanace ke magana ita kadai a tsakar gida inna na daki tun bayan tafiyan mu har yara suka dawo boko suka tafi islamiya taki fitowa waje.
Gashi sai tambayana suke inna ina yayar mu bamu ganta ba tun dazun tace dasu ta fita kawai daga haka kowa ya shiga harkan gaban shi.
Sun tafi islamiya sun dawo sun samu inna a yarda suka barta haka yasa saratu mai dan wayau a cikin su sake tambayan inna.
Inna wai lafiya kike yau kuwa ina yayan mu tajene tun dazun bata dawo ba kuma ban santa da zuwa unguwa haka ba ai.
Hawayene ya fara zubawa inna da sauri saratu ta juya wurin jakkan kayana tana dubawa tare da fadin inna sun dauke yayan mu sun turata aikatau ke nan ?
Wani irin kuka inna ta kara fashewa dashi lokaci guda saratu ma kukan ne yazo mata sai hakan ya jawo hankalin sauran yan uwan mu dake wasa kofan inna.
Saratu ke fadin wayo yayan mu ki dawo kada kije aikatau don Allah an ce ana lalacewa wurin aikatau din nan.
Haba dakin inna ya koma dandalin kuka da tashin hankali don kuka sosai yaran keyiwa inna.
Da gudu lantana taje ta kira Asabe tana mayar mata da karya wai ga inna can ta tasa yara a gaba sai kuka sukeyi don tafiyana.
Asabe ta fito babu ko dan kwali a kanta sai a hannu ta rike tana fadin bamu cikin abin kuka da yamman nan .
Kuyi muna shiru masu mugun manufa da sheri don tafiyar yar uwarku zaki zauna ki dasa muna kuka ke da yara haka kamar anyi mutuwa a gidan.
Asabe wallahi sai kin dawo muna da yayan mu ko zaman gidan nan ya gagareki keda munafukanki da cewa lantana.
Mara kunyar banza da wofi koke can kika nufa idan naji dadin yar uwanki ana turo min kudi irin haka marasa hankali kawai.
Da kuna zaune a gida kara zube ina zamu samu irin kudin da muka samu yau a gidan ba gashi har kun dawo kun samu anyi abinci ba yau.
Kowan nan sai ya dandani wanan hanyar aini yanzu gaba haihuwan ku ya kaini tunda na samu mafita daku.
Ana cikin hakane Abba ya shigo yana fadin yaya yayane tun a kofa nake jin muryan ki umma.
Asabe tace barni da mutanen kawai din nan wai tafiyar yarinyar nan yahanasu ta saka yaran nan a gaba suka mayar muna da gida gidan makoki.
Yahanasu kina da hankali kuwa ke yanzu idan kina da tunane ai wani nauyi aka rage maki Abba ya fada.
Fada mata dai ko zata gane hakan ina nan gashi dan kudin da hajiya ta fara bayarwa kowa ya fara amfana dashi gidan nan ba gashi kunci shinkafa da wake ba yau a gidan.
Umma kyale ta barin ganta ni yahanasu har mamaki take bani yanzu kan yarunyar nan babu nuna kawaici a kanta ko kadan.
Idan ma bata nuna ba ita ta sani nidai na nuna mata nike da iko da abina daga diyan ko har kai a gidan nan ko wa yan nan na samu mai daukan su bayar dasu zanyi zuwa birni.
Ba saki bada muba tunda ke kika haife mu cewan Saratu sai inna takai mata duga daidai Abba na shigowa dakin inna din.
Bar dukan ta rabuwa da dan uwa nada zafi tundai irin wanan na yarsu nima dai ba haka naso tafiyan nataba kai tsaye so nayi muje tare inga wurin.
Koma dai menene yanzu aikun nuna min kukeda yarku saidai ina son ku sani naji umma na fadin har wa yan nan za a tura min can birni aikatau.
To wallahi hakan ba zai yuyuba wanan ya isa haka idan da hali dawo da yata zanyi gabana yafi mun kwanciyar hankali idan kasa mukeci mu kwaba muci tare.
Toto to ya isa haka yana sa hannu ga aljihun shi ya ciro yan dubu guda biyu yana fadin ga wanan kya samu ko sabulun wanki ku saya.
Da da nake saya kai kake ban kudi katafi da kudin Allah ya isan ka can kuci ku kadai ku gani.
Kwadan ku ya fada kun raba ni da yata kun rabata da gatan ta da Allah yai mata don kawai tana diya mace.
Shiru Abba yayi don inna bata taba tsayawa ta fada mai magana ba haka kai tsaye irun ranan.
Kwafa yayi ya fita bayan ya mikawa saratu kudin yana fafin karbi ki aje mata idan ta sauko zata karba a wurinki.
Yana fadin haka ya fita daga dakin don kada yayi laifi a gurin lantana dake tsaye ta rike kugunta tun shigan Abba dakin inna.
Yana fitowa fuskanta ya fara kallo ta watsa mai wani harara ta juya zuwa dakin ta shima abba yasan sauran zancen ranan a guri lantana don haka wani dabara ya fado mai.
Yana shiga dakin ta juyo zata fara fada yace me zakiwa fitina kin san dai ba zama nayi a can ba rufe mata baki nayi da dubu biyu ke kuma ga naki dubu biyar ki rike.
Sai lokacin lantana ta dan saki murmushi tana fadin wallahi yau Allah yaso ka da kakoma can ka kwana surin tsohuwar matar ka
Nina fara hakan gani da dalleliya kamar ki inje dakin da warin fitsari da kwamatse ya ciki.
NEW G R A KADUNA
A hankali mama kande take koyar dani komai duk wani abinda ya shafi mami da zirga zirgan ta na cikin gida nice mai mata hidinar shi..
Da na zauna zaki ta kirani da zeey zan amsa da na,am mami in zo da sauri don biya mata bukatun ta wanda ba wani aiki bane.
Sai dauko min kaza jiki mayar da wanan a cikin wardrobe ko dauko min ruwa shine aikin nawa kawai dawai mami bata iyawa sai an dauko mai mata wanan hidimar da ban daukeshi a aikin komai ni.
Sai gashi cikin sati daya kacal na gane komai na mami nasan lokacin tashin ta daga barci .
Zan shiga dakin in gyara gado in wanko mata ban daki zan koma in hada mata ruwan wanka tana zaune tana lazumi don mami akwaita da yawan ibada sosai.
Zan dawo dakina in jirata tana tashi zata kirani in dawo in share dakin duk da ba wani datti ke ga dakin ba amma kullun sai nayi gyaran shi sau biyu a wuni.
Kafin ta fito wanka nagama hada komai sai in koma dakina can kuma idan ta fito zata kirani da zeey zan zo in je dining in hada mata tea wanda wani ruwa ne baki kawai sai dan sugar kadan bata shan madara da suga ita.
Idan na gama zan koma dakina inyi wanka in shirya in dan huta kafin ai mi wani kiran kuma inzo.
Kai masu kudi suna shagalin su banda abin aikin kudi wai wanan dinne aikin da aka raboni da gida do shi aikin da mutum zaiwa kansa ba sai ya nemi mataimaki ba.
Amma hjy gashi tana ganin ina aiki sosai sai fadi take yarinyar akwai kwazo da sanin ya kamata.
Do ita gani take yanzu komai na zuwa mata da sauki a nata bangare har zata samu tayi barci ta huta na dan lokaci.
A bangaren yaran gidan hjy kuwa ba ruwab su da shiga tsabgata nima hakan ne dasu.
Saidai su wani lokacin zasu sakani wani aiki a gidan wanda ya shafi rayuwan su suma ga tsana karara da ko wace ke nuna min.
Dan gara salma da har yanzu ba zance tsanane ko tausayina ba a ranta don na kasa fahintar inda ta dosa dani a ranta.
Wani lokaci inji sanyi a wurin ta wani lokaci kuma idan ta daka min tsawa sai na gigice don tsoro.
Ita irin mutanen nan ne shiru shiru da mugun ta don surutu bai dameta ba ko kadan za a zauna wuri ba zakaji bakin ta ba sai wani lokaci ta furta idan ta furta daya kuma shike nan.
Duk wanan abinda suke min bai damuna naka ma raya a raina idan naga sun dau wanka zasu tafi school nakan ce inama a ce nice a matsayin su haka.
Nasan da ko Asabe ba zatayi gigin takani ba balle lantana dana tsana fiye da kowa a gidan mu yanzu.
Ni dai na rasa dalilin da yasa yaran gidan hjy suka tsaneni a baki dayan su in ka debe hjy da mama kande da suke nuna min kulawa a gareni.
Tun dai ace yan matan don a fili suke nuna min kin jini da kyama duk da yanzu nasan nima ina tsabta fiye dacan da nake Ancau din mu.
Na kanyi tunane indon dun kauyancine da kazanta yazu duk na daina wanan a ganina do na canza nayi fes na kara zama shar kamar bani ba.
Ga mai da turare na yan gagu da hjy taban tace in dinga shafawa idan nayi wanka gun kashe gari dana zo.
Komai ina yi shi a taka tsamtsam a gidan ban yarda in ketare iya inda aka ajeni ga aikina dan dama wani lokaci idan zama ya isheni nakan shiga kitchen in taya su mama kande aiki do su basu da hutu kamarni.
Ko yaushe a cikk girki suke dan hutun su kadan ne tundai idan yaran gidan suna gida wancan yace kaza yake so wana yace baya cin kaza yau.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.