Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 91 of 139
ZAINAB IDRIS MAKAWAYA HAIYYU YA KAIYUMU BIN RAHAMATIKA YA ASTAGIS UBANGIJI KAI HASKE GA KABARIN DUK KAN MUSULMIN DA SUKA RIGAMU GIDAN GASKIYA ALBARKA KALMAN LA,ILLAH HA,ILALLA MOHAMMADAN RASULILLAH DA SUKA TABA FADA A RAYUWAN SU ALLAHUMA AMIN , , , , ,
Gidan yayi shiru lokaci guda baka jin motsin kowa a gidan sai na,orurin dake aiki kawai na gidan a lokacin.
Mami dake kwance ta mike a hankali zaune taji zaman bai mata dadi don zuciyar ta daya cushe wuri daya a lokacin.
Haka yasa ta saukowa daga saman gadon a hankali ta gyara hulan dake saye a kanta ta nufi kofan fita daga dakin.
Ba kowa falon don haka ta nufi wurin shan iska inda zaka iya tsayawa kaga duk wani abinda wajen gidan ke ciki daga inda kake tsaye.
Jamal ta hango tsaye shi kadai a cikin duhun yana tsaye ya harde hannayen shi guri daya yayin da kafafuwan shi ma suke a harde mashi.
Hankalin shi gaba daya ya mayar dashi gaban gidan jikin shi na jingine da dan bangon wurin yana tunane ga iskan sayi yana huro mashi a jiki.
Jin motsin mutum da yayi lokacin yasa shi dan juyowa inda yake jin tafiyan mutum din mami ya gani don ya sheda ta duk da akwai duhu a lokacin.
Hakan bai hanashi sheda mahaifiyar tasu ba da take tafe itama mami din ta sheda ko waye a wurin tsaye duk da duhun dake akwai din.
Mami baki barci ba ya fada cikin mamaki da tare da juyowa inda take yana fuskantar ta.
Jamal ban dauka zan kara barci da idanuna ba kuma a wanan halin da dan uwan ka ya jefa kanshi a ciki na rayuwa irin wanan.
Mami yanzu kin gani ke nan kema abinda na gani gareshi nake wanan fushin dashi .
Jamal na gani Allah ya nuna min da idona yau naga mugun gani da idanuwa ga dan dana haifa da cikina .
Sai wani irin kuka yazo mata lokaci guda jamal din yace mami ba kuka zakiyi ba don yanzu yaya addua da taimako yake so a garemu don yayi nisa a cikin wanan harkan ko yanzu.
Jamal dole inyi kuka yau jafar ne a cikin wanan halin haka jamal ina zan saka rayuwana dan dana haifa aka bar min amana shine ya zama haka a rayuwa.
Wanan kaddaran bawane, mami duk mai rai baya wuce kaddaran shi a rayu don haka zama ya kamata ayi asan hanyar da za a fitowa wanan maganan tunkan zancen nan yayi bosting kowa yasan hakan.
Sani kuma na yaushe jamal tunda matar tasa ta sani kila kuma yan uwanta nan da suke zaune suma duk sin sanda hakan ko ?
Kai haba mami zainab tana da matukar wayo bazata bar kowa yasan wanan zancen ba rufa min baki wani wayau can.
Zata dai iya yin hakan don ta kare kanta itama tunda take zaune dashi ai kila itama din yar hannun ce ke nan ai yanzu.
Ina mami baki san waye yarinyar nan zainab ba ashe har yanzu don koni danagani da idona kuma a kusan tare zance munga wanan abin amma bata yarda nasan da hakan ba .
Saida na fito mata da zancen da kaina ta yarda tayi min bayanin komai don haka nake ganin ko yanzu ba zata taba barin kowa yaji hakan ba a bangaren ta.
Jamal ke nan duk da kai yaron har yanzu baka tunane ko ita yanzu ya bata ta yasa bata yarda ta tona mashi asiri.
Shiru Jamal din yayi yana tunane kala kala a zuciyar shi kafin yaji muryan mami yaci gaba da fadin nima haka wanan tunanen yazo min .
Don yadda naga tana kokarin rufa mai asiri dole akwai wani abinda itama take boyewa nata don ko hjy dake dakin muna magana da mamud cewa tayi kada a bati taji komai don tsufa.
Sai wanan karewan da takeyi din ya tsaya min a zuciyana na fara zargin itama ta dade da lalacewa ta wanan fannin yanzu.
No mami kada kiyi zargin hakan a dai bincika a ji ai zata fadi gaskiya koma meye ba zata boye maku gaskiyan ba nake tsamani.
Kana wasa da wanan yarinyar jamal ya katse da fadin haba mami yanzu kuma meya saura na zargin zainab gareki.
Ga gaskiya tayi halinta baro baro za a tsaya zagin yar mutane damafa ya J yayi amfani da yarinyar nan zainab ne ya aureta bada yardan ta ba yabi ta wajen iyayyenta ya aureta.
Don kawai ya kawar da idon mutane a kasan ace yana da aure ai ba haka kawai yake zaune ba.
Don kada mutane damu a gano abunda yake aikatawa din wanan hikima yayi yaki yarda da auren hadin da kika so yi masa a baya.
Don yasan idan daga bangareki ne yarinyar ba zata taba yarda ta boye shi ba yadda zainab din ta boye shi na shekaru.
Idan ma cutane mami yanzun dai kingani yar mutane da aka baki amana aka cuta don mutuncin ki iyayyen ta suka gani tun farko suka yarda suka aura mai ita ba tare da wani kwankwanto ba can.
Kai jamal ni kake kokarin nuwa yaran nan kome ina dukkan ku ta dalilina kuka san yarinyar nan dai ?.
Koma meye zan zauna da ita ai in fahinci komai wallahi idan yarinyar nan tana da hannu cikin wanan matsalan gaba daya sai na sabawa rayuwan su.
Don me zai shiga daki haka da wanan katon suna wanan wasan banzan idan ba wani abu suke aikatawa ba hakan ?
Ok mami hakan yana da kyau ai ki bincika kiji komai don zaki gane mai gaskiya a cikin su yanzu ai idan kin bincika din.
Sai dai kuma mami ki sani danki fa abinda kika gani shine gaskiya abinda danki ke aikatawa a kasan nan don shi sam bai damu da diya mace ba a rayuwan shi.
Ga abu kin gani da idon ki mami zaki tsaya kina wani kwanaye kwanaye akan yar mutane ?
Yanzu dai ai abin cikin duhu ya fita fili Allah ya nuna maki wanan sirin da danki ke boyewa sheka da shekaru yanayi.
Ji kawai yayi mami ta fadi kasa a wurin somamiya da sauri ya nufi kanta yana kiran sunan ta cikin tashin hankali.
Gashi su biyu ne kawai a falon dabara ya fado mai na ya yayyafa mata ruwa ya nufi kitchen da sauri ya dauko goran ruwa mai sanyi ya dawo dashi inda take.
Ya yayyafa mata sai gata ta farfado lokaci guda sannu yake faman yi mata sai ta koma luuuu ta kara somewa kuma.
A daidai lokacin fadila ta fito don motsin da take ji tun dazun a gidan idon ta yai arba da mami kwance kasa somamiya .
Ga Jamal a kanta sai faman gurgizata yakeyi ihu ta yanka don tsoro lokaci guda muke bude kofofin gidan muna fitowa daga dakun nan mu.
Kai ranan munga tashin hankali asibiti suka nufa da ita kai tsaye dashi da yaya mamud sai jamal da jalal da suka bisu.
An barmu gida hankali tashe don bamu san halin da mami ke ciki ba a can don duk sun bar wayoyin su a gida tunda ba fitowan girma da arziki sukayi ba daga dakunan su.
Tambayan nasha shi wurin Aisha amsa daya nake bata shine nima ban san dalilin hakan ba nadai ga mami a wanan halin tun bayan shigan ta dakin yaya .
San nan na samu sa,ida a wirin su da tambayan da suke min hjy kan iya damuwa ta damu sosai da yar ta mami a halin data shiga.
Basu dawo gidan ba sai washe gari suke fadin anba mami gadome asibitin da aka kaita tana can kwamce tare da jalal da jamal.
Duk da hankali ya dan kwanta tunda sunce ba wani case bane sosai wai gajiya ne yai mata yawa na hanya.
Nikan a raina nasan ko meye umul,aba,isin hakan da takeyi naja bakina nayi shiru don kada wani ya farga ya gane nasan wani abu.
Gani da test a ranan Maya tana ta kirana dole haka na sance jiki na fice zuwa rubuta test din fadila kawai na fadawa inda zan tafi a lokacin.
Allah ya taimakeni ba a fara ba saura minti biyu za a fara na shigo ban dade ba aka fara test din muna fitowa nayi sallama da maya na tafi.
Na dawo na samu sun tafi asibitin duban mami sai fadilace kadai a gida sadiya bata riga data dawo gida ba daga makaranta don ni nayi saurin dawowa ranan.
Da kaina na shiga kitchen muka hada masu abinci tare da mai aikin daya data saura a gidan don sauran sun dauki hutun sun tafi gida.
Fadilace ke fadin rashin kyautawana da ban je asibiti duba mami ba nace da zuwana da rashin zuwa daya yake a wurina.
Don yanzu jira nake kawai ta ba danta umurnin ya sallameni mu koma gida don shi kawai nake jira yanzu.
Da sauri ta kalloni da mamaki tana fadin kada ki fadi haka zainab don nasan boss bazai taba sakin ki ba ai.
Saboda wasu dalilai nasa kina da rana da amfani a wurin shi sosai wanda ba kowane yasan da hakan ba.
Saki ya zama dole yanzu gareshi don lokaci yayi da zaiyi hakan na gaji da ganin laifina da mahaifiyar shi ke min ko yaushe.
Gara na bar mata danta a zauna lafiya ta aura mashi yar masu arzikin da take so ya zauna da ita.
Ina shima yasani ai zainab babu macen da zatayi wanan hakkurin da kikeyi a gidan nan yanzu.
Don haka ki daina ma wanan zancen zainab don haka ki shirya muje anjima mu dibo ta ko ran mijin naki bazaiyi dadi ba idan bakije ba ai.
Amma anty don ta katseni da fadin please zainab kada kice ba zaki ba din ko rashin zuwan ki a yanzu ai tasan da wani abu a kasa don abin zai iya damun kowa nan gaba.
Nace shike nan anty zan tafi da yamma idan Allah ya kaimu sai ki shirya idan sadiya ta dawo mu tafi dukkan mu.
Sun dawo gidan saidai ba wani damuwa a tare dasu don jikin mami din da sauki sosai sun dai kwantar da itace don ta samu hutu da natsu a can.
A falo suka zube wasu kuma suka shiga yin sallah masu rikon addini ke nan daga cikin su irin hjy tsohuwa da anty Na,ima sai Aisha data shiga itama don laluran ta ba laifi ta tsaya tayi sallah a dakin.
Don na shiga na sameta tana sallah amma su Nuriya dasu Rufaida suna falo ana hiran garin wanda a cikin hiran nasu suke sako habaici a ciki.
Dawowan Sadiya ba ta dade da shigowa ba a lokacin kowa na falo zaune har mazan suna cin abinci duk suka bita da kowa da abinda ke zuciyar shi .
Lokaci ne na mike zuwa daki na samu Aisha kwance tana waya nan daki na shiga ban tsaya ta kanta ba na fara watsa ruwa a jikina.
Nafito nake shiryawa don fitan da zamuyi zuwa duba hjy muryan Aisha ya daki dodon kunnena da farko tsuki mai karfi naji taja.
Hakan baisa na waigo inda take ba don zatona da wanda take wayan take tsukin sai naji muryan ta na fadin tsiyan banza ashe da gaske ake fadin dan talakka bai iya samun wuri ba dama.
To bari kiji wallahi zainab idan wani abu ya samu mahaifiyar mu wallahi ni da kaina zan dauki mataki akanki koda kuwa ya j zai halakani nima.
Na juyo ina fadin au dani kike zance ashe amma dai kafin ki halakani din zai fi kyau shi J din ki fara halakashi don shi musabbabin komai da mahaifiyar ku ke ciki.
Ni meye nawa a ciki don bani nakar zomo ba rataya akabani don haka kowa ya sakar mun mara nayi fitsari .
In laifine jeki gun dan uwanki ki tsure shi donni ba haifana kikayi ba da zaki sakani gaba zaki fada min rubish.
Tunda na juyo na fara magana Aisha ta tsura min ido tana kallona da mamaki karara a fuskanta har nakai karshen magana na juya ina daukan kaya da zan saka.
Can naji tace min lalai Aisha wuyan ki nan ya isa yanka zainab ni kike fadawa magana haka kai tsaye ?
Kamar ba zan bata amsa ba saida na dauko kayan na aje na dago ina fadin nafada maki indon wanan auren kaddaran na dan uwan kine harke kuke son takura min a rayuwa don Allah yanzu ba sai anjima ba kisa ya sakeni na koma gun iyayyena yafi min zama da wanan kaddaran.
Fadila ce ta turo kofan da sallama tana fadin madam we are ready ke muke jira ki taimaka ki fito min da takalma da jakka kayan nan.
Tace yes ma ta nufi inda nake aje su tana daukowa tsuki Aisha taja tana sauka a gadon ta nufi hanyar fita daga dakin.
Yadda ta fita yasa fadila gane akwai wani abu atsakanin mu lokacin ta kalloni bayan fitan Aisha din tana fadin meya faru kuma ?
Ba komai na bata amsa tare da rolling din dan kwali a kaina ina fadin muje ko tace ok muka fito na rufo kofa da key.
Muna saukowa duk idanuwan su a kaina don shigan da nayi ya girgizasu a wurin da alama kuma akwai maganan da sukayi akaina lokacin.
Zamu fita nace dasu don su basu gajiya da kallona ni har mamaki abin ke bani yasa ban nuna masu na tsargu da irin kallon da sukan min ba a yanzu.
Bin bayan mu Rufaida tayi da leke har lokacin dana bude mota muka shiga na fice gidan ta juyo tana fadin what ?
Wai kunsan kuwa yarinyar nan wani kafirin mota take ja haka da kanta a garin nan ya mamud ne daga inda yake zaune ya dago yana fadin ina ruwan ki ko jirgi a yanzu sai zainab taja wanan ba abin mamaki bane ai.
A mota nake ba fadila rabarin yadda mukayi da Aisha da amsan dana bata ni kuma .
Fadila tace kin min daidai wallahi don raga masu baida wani amfani ko kadan gara su san yanzu ke din ba sa,an su bace ai.
Mun isa asibitin ban wani sha wuyaba muka gane inda mami take muka shiga kamar yadda ka,idan shigan su yake a kasan.
Don sukan ba,a barsu sun shiga ba don sunyi yawa kuma ba time din duba mara lafiya bane lokacin.
Muna shiga muka samu jamal da jafar a zaune shiru a dakin mukai sallama bai dago kai ya kallemu ba yana dakilan wayan shi.
Jamal ne yayi muna sannu da zuwa muka kara gaidasu tare da yiwa mami sannu da jiki ta dan dago tana amsawa.
Abinci da muka zo dashine muka aje a gabanta nace mami ga abinci munzo maki dashi.
Godiya tayi muna sai lokacin jafar yayi magana yake fadin fadila ki taimaka mata ta tashi zuwa bandaki ta dan gyara.
No ta bari zan iya mami ta fada a karo nabiyu da tayi magana ke nan tun zuwan mu dakin da take kwance din.
Da kyat ta yun kura ta mike ta shiga bayin haka yasa dakin shiru babu mai magana a cikin mu har ta fito ta hau gadon da niyar kwantawa.
Abincin nake kokarin zubawa muryan mami ya dakatar dani tana fadin dakata zainab kada ki zuba don bazanci abincin gidan ku ba.
Wani irin kallon mamaki kowa na dakin yai mata lokaci guda sai fadilace mai karfin halin fadin mami kiyi hakkuri ki danci wani abu don Allah.
Jamal ta kalla inda yake tana fadin akwai kudin kasan nan a hannun ka ka sayo min abinda zanci a waje.
A sanyayye dan nata ya amsa mata yana fadin akwai mami amma da kici wanan din don gurin sayar da abincin yana da nisa sosai.
Jeka ka sayo min zan jiraka hakanan har ka dawo ta fada tana kawar da fuskanta daga kallon mu cikin dakewa.
Jamal na fita jafar din ya mike tare da fadin mami zan koma wurin aiki sai anjima zan dawo insha Allahu.
Ko motsi batayi ba balle yasa ran amsawa ga sallaman da yayi mata haka yasa kai ya fice daga dakin duk wanda ke wajen saida yaji wani abu a ransa lokacin.
Munyi shiru dukkan mu mami ke fadin kada ki damu zainab badon ke nayi haka ba wanan karon donshi mara hankali da tunane na aikata hakan don haka kada ki dauki wanan don ke nayi hakan dama.
Babu komai mami Allah ya shirya tsakanin ku na fada ina mikewa tsaye da sauri suka mike suma nace su jirani a waje ina zuwa.
Suna fita fadila ta rufo kofan hakan ya bani daman karasawa bakin gadon da mami din take kwance.
Ka nakai gurfane ina fadin mami kiyi hakkuri ki gafarce ni ban auri jafar don wani manufa da kuke fadi ba.
Asalima shi jafar di ne ya turasasa iyayyena ya aureni da wani manufa da yake dashi a zuciyar shi don cinma burin shi.
Kimarki da martaban ki hade irin kaunar da kika nuna min yasa iyayyena basu tsaya dogon bincike ba suka bayar dani ga danki.
Kuka ne yazo min na dakata na dan lokaci saida nayi mai isata naci gaba da fadin Alhamdullahi mami tunda yau kin gane waye jafar da abinda yake aikatawa na fasadi a doron kasa.
Don haka nake rokon ki a matsayin ki na uwa a gare mu mami ki tursasa jafar ya sakeni in koma wurin iyayyena tunda Allah bai nufa burin shi ya cika ba a kaina.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.