Complete Hausa Novels

Abu Cikin Duhu Complete Hausa Novel

Reading file: Abu_Cikin_Duhu_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 63 of 139

🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅

5️⃣3️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

ALLAH SARKI YABON GWANI YA ZAMA DOLE JINJINA GAREKU ADMINS DIN WANAN GROUPS DIN WATAU ZAURE BIEBI ISAH DA HUGUMA GROUP DA ZAINAB MAKAWA GROUP1
WA YANNAN GROUP DIN SUNCANCANCI YABO A KO INA WALLAHI DAMA SAURAN GROUP IRIN NASU DA BANSAN DASU BA A SHAFIN SADA ZUMUNTA NA WHAFFS,
DALILI KUWA SHINE DUK KYAU DA DADIN NOVEL IDAN NA KUDINE BASU YARDA A JAFASHI A WANAN GIDAN NASU.
WANAN YA NUNA SU DIN UWAYENE NA GARI MASU IYA BADA TARBIYA GA IYALAN SU DAMA AL,UMMA GA BAKI DAYA A DUNIYA SABODA KARE HAKKIN DAN ADAM YA ZAMA DOLE IN YABAWA WANAN ADMINS DIN GASKIYA IDA BAN FADA BA BAN MASU ADALCI BA A RAYUWA.
ALLAH YA KARA TSARE MUNA IMANIN MU DA ZUKATAN MU ALLAHUMA AMIN DON HAKA ZAN TURA WASU NOVEL DINA KYAUTA GA WANAN GROUP UKU AKYAUTA SABODA ALLAH DA ANNABINSA .

Tsaye yake a tsakiyan dakin yakai gwauro yakai mari ya kasa zama a dakin ya tuhuta babu abinda yake tunane sai abinda ya faru a tsakanin mu dashi din da yammacin ranan.
Ya akayi har wanan yarinyar ta samu courge din da zata iya duban tsaban idanun shi ta fada mai magana haka kai tsaye ba tare data jin tsoro ko kunyar idan shi ba.
Anya kuwa zai iya wanan yarinyar nan gaba a yadda yake tunane idan ta kara wani shekaru a hannun shi kuwa ?
Kai da sake ya fada a fili yana dafa gado ya kai zaune tare da hada hannayen shi wuri daya yana fadin yaushe ma ta zama hakan ne a gidan nan.
Wanan tana da banbaci da zainab din da ya sani a baya wanan kamar idanuwanta ya bude yake gani idan ba karya yakewa kansa ba.
Tun shigowan shi garin nan ya fahinci canjin rayuwa a tare da ita gaba daya ta canza mashi ta koma wata babban mace da bai taba zaton kawan ta hakan ba a yanzu.
Ya zama dole ya lalubo hanyar da zai kwantar mata da hankalita har ta iya manta da wani zargin da take dashi a yanzu akan tajudeen din dayayi mai katsalandar a rayuwan shi ya tashi rushe masa komai daya shirya a baya.
Kwance yakai saman gadon rigingine yana mai lumshe idanuwan shi a hankali kamar mai wani nazari a lokscin.
Kafin ya mike zubur yana kiran layin wani abokin shi ba,ajima ba ya dauki kiran suka fara gausawa dashi.
Bayan gausuwa daya biyo baya yake tambayan abokin nasa kai mota nake so na mata lates one wanda sai ya girgiza mutum idan an bashi shi.
Dariya abokin nasa ya kwashe dashi yana fadin mutumina kayi sabon kamu ke nan kuma ?
Dama nasan wanan zaben yar kauyen da kayi zai dawo ya bata ma rai daga baya dan irin diyan tallakawan nan ba ka taba samun su a yadda kake son su.
Balle kai mutum irin ka wayayye na gani na fada idan babu wata a kasa har zaka fada tarkon irin wa yan nan diyan kauyawan masu kame maza har gwiwa.
Dan murmushi ya sake dan ya gaji da sauraren maganganun shirmen da abokin nasa Amadi yake fada mai a lokacin kan zainab din da shi kadai yasan abinda ya tsara a tsakanin su.
Cikin karfin hali yake fadin ba abinda kake tunane bane Amadi wanan dai yar kauyen da kake fadi din itace zan sayawa motar da babu wace mace dake da ita a garin nan ko akwashi kuwa baifi mace daya ko biyu ba a cikin kasan nan.
Kai mutumina da gaske kakeyi wanan magana kace yar kauye tayi tasiri a rayuwan ka haka ban sani ba nafa sanka a baya da kyakyamin mata balle wanan data zama yar , , , , ,
Dakata Amadi banson jin haka ga iyalai na don Allah ya fada muryan shi na nuna warning ga abokin nasa lokaci guda.
Amadi din cikin sauri yake fadin Iam sorry mutumina nasanka da riko da wasa nake maka nima nasan ai kai baka harka da mata dama.
Idan an samu sai ka kirani ya fada yana kokarin kashe wayan da yake ji kamar ya yarda ita lokaci guda don haushin da abokin nasa ya basa a lokacin.
Ya rasa meyasa mutane suke shiga zancen abinda bai shafesu ba kodan irin haka yanzu ya zama dole yayi wasa da idan mutane akan wanan yatjnyar su sancewa ita din mata take agare shi kamar matan kowa.
Ya dade a kwance kafin ya mike tsaye ya shiga bandaki ya watso ruwa ya dawo ya tayar da sallah ya dade zaune a gurin shi ba addua yakeyi ba kuma shi bai daga ba sai faman tunanen daya addabi zuciyar shi a lokacin.
Yana jin ana kwankwasa kofan shi yaki tashi ya bude sai kallon lokacin da yayi ta hanyar daga kai ya kalli agogon bangon dake dakin nasa makale don gwajin lokaci.

Har kusan sati daya nikan bamu hadu ba dashi a gidan duk dako nasan yana gidan haduwane kawai bana yarda muyi dashi.
Dan nima da baya na danyi nadaman tsayawa in masa rashin kunya a gaban shi duk da hakan ba halina bane aro nayi na yafa a lokacin.
Saboda bacin rai da takaicin maganan da tajudeen ya fada min a ranan na kwata na juya na rasa gano dalilinsa na fada min wanan bakar maganan haka kodan yaga maigidan bai dauke ni a matsayin mace bane a gurin shi yasa hakan ban sani ba.
Bawai yadda yayan ya daukeni yake damuna naba a,a hakan ni bai taba damuna ba a rayuwa saidai yadda shi taju din yai min magana a cikin tsanane damuwana a lokacin.
Da yammane ina zaune a keance a dakina ban dade da fitowa daga gurin maizube ba da yanzu kusan duk zaman daki muke a gidan ga baki dayan mu.
Naji an turo kofan dakin nawa bayan an kwankwasa saudaya sai turo kofan da akayi din lokaci daya da kwankwasan kofan.
Ba tare dana juyoba ina kwance a yadda nake jin kamshin turaren yasa kirjina bugawa lokaci daya nayi yun kurin juyowa da sauri don ganin wanda nake zaton ya shigo dakin nawa.
Yaja ya tsaya a bakin gadon da nake kwance din yana kare min kallo na dan lokaci guda yana karewa dakin dake gyare fes da kallo.
Ido nima na dan dago na kalleshi na lokaci guda kafin in mayar dasu kasa ina kokarin mikewa zaune.
Ki kwanta abinki ba wani abu nazo yiba dama na shigone in ganki tunda kina wasan boyo dani a gidan nan yanzu.
Yana fadin hakan fuskan shi yana a kaina dauke da bada umurni a gareni lokaci guda.
Ban kwanta ba kamar yadda ya bukata din sai gyara zama danayi ina mai sadda kaina kasa lokaci guda dan kallon da yake min din.
Da kyar na iya buda bakina ina fadin kayi hakkuri koda zan fito ka fita lokacin yasa baka gani na.
Yace ke nan ba,a koya maki gaida mutane ba kike nufi ko me daba zaki iya shiga ki gaidani ba ?
Na dago ido da sauri don in saci kallon shi don jin abinda ya fada lokacin still dai ni din yake kallo har wanan lokacin.
Ya tsura min idanuwan shi manya shi da suka canza cikin kankanin lokaci da fara maganan shi a kaina .
Karasa saukowa saman gadon nayi ina gyara bujen jikina dayan yi squeeze nadan hade hanaye a wuri daya ina fadin .
A cikk kyarma ina gudun naje dakin nakene kuma ai min wani fassara na daban shiyasa na daina shiga amma kayi hakkuri dan Allah.
Har zuwa lokacin baiyi magana ba sai na kara dukar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna a hankali.
Hannu ya tura a cikkn aljihu yana fadin nasan matar malam ta gaji da zama a garin nan don haka gobe za a mayar da ita gida ita kuma halimatu tunda tana karatu sai a barta a nan tare dake .
Kai na dago da sauri ina kallin shi wanan karon nan kawar da idona ba daga kallon shi cikin murya mai dauke da son yin kuka nace.
Don Allah ka barta ta kara min wasu kwanaki kafin ta koma don idan ta tafi zan shiga damuwane sosai ga hjy har yau ban daina kewar ta ba a gidan nan.
Babu mutanene a gidan ko kinmata itama tana da aure ne kamar ki da zan aje matar mutane anan na wata da watannk ai sai a yaba min rashin hankali.
Hakan da naji ya kara sa hankalina tashi sosai ya juya kamar zai tafi yana fadin gobe ma zanso na roke shi arziki yai min ai.
Kinga yanzu ai gidan kine zaki iya zama ke kadai yadda kika girman a lokaci guda da sauri nabi kaina da kallon dan jin abinda ya fada min din.
Yes ya fada tare da sauke min wani irin kallo daga sama na har zuwa kasa yana fadin wa zai ganki a yanzu ya dauka kece zainab din mami a baya mai gudun mutane.
Baki na turo gaba ina fadin niban wani girma ba dan Allah ka barmin ita nidai mu zauna a nan tare na fada kamar zanyi kuka a lokacin.
A dan rikice yake fadin me akai maki kuma yanzu don shagwaba kawai daga magana kina shirin yiwa mutane kuka yanzu kuma.
Idona dago kamar zanyi kuka nace bakai bane kake shirin mayar da sai nayi shiru kuma dan na rasa abinda zan fada mai a lokacin.
Yace a cikin zaro idanun shi waje da akai maki me a hankali na furta zaka maida maizube gida mana.
What me kike fada dama nufin ki a nan zata tabba tare dake ko me kedai yarinyar nan da alama shagwababiyar mace ce ke .
Zama nayi a cikin fushi saman gadon na basa baya yasa kai ya fice daga dakin saina tsunci kaina da sake hawaye lokaci guda.
Shike nan yanzu maizube zata wuce ta barmu ke nan ba zan sake ganin wani dan gida ba sai yadda hali yayu ke nan dani duk da naji bada halimatu za,a tafi ba hakan bai hana hankalina tashiba a lokacin.
Karshe na mike zuwa dakin nata sai dai na kasa fada mata abinda nayi niyar fada har na shigo dakin a lokacin dan bansan yadda zance da ita kada ta tafi ta barmu ba tunda itama tana son zuwa gidan a lokacin duk da daulan da muke cikin sa kuwa.
Washe gari ba karamin mamaki nayi ba abinda ya hadawa maizube na tafiya kowa sai sam barka da ita da anty fadila da take hada mata kayan tafiyan a wuri daya don kuka ya hanani tabuka komai a lokacin.
Nasiha da bn baki nasame su gwargwado wurin boyar Allah nan sai kara jadda min kalman inyi hakkuri da rayuwa wata rana idan Allah ya yarda zan dara kan aurena.
A mota sukai tafiyan don har gida za a kaita ga tsaraba mai tarin yawa an hadata dashi ban tsaya naga tafiyan ta ba don kukan da yazo min a lokacin dole na koma gida na fada saman gado.
Duk dauriyan halimatu itama da taga zasu wuce saidai tayi hawaye a lokacin ranan haka muka wuni sukuku damu sai gidan ya koma muna shiru kamar babu kowa a cikinsa lokacin.
Ban fito ba wunin ranan ina daki rufe sai faman tunanen da nakeyi na gida wayana yai kara na dauka innan muce a layi ta kirani tana min godiyan abinda ya jafar ya aika masu dashi.
Saidana hade wasu hawayen bakin ciki tare da saita muryana nake fadin inna ai hakan yiwa kaine duk da bansan abinda ya aika masu dashi ba a lokacin.
Bayan mun gama waya da inna na sake wani irin kuka mai karfi ni kadai a daki babu wanda zai ban hakkuri dole na kyale naba kaina hakkuri.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.